← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 67

Sashe 11

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jin su baba sun mayar da abun raha yasashi zare jikinsa zai fice har yakai bakin kofa yaji baba yace masa,

"Gobe idan Allah yakaimu zanje sai ka sanar musu"

Daga kai kawai yayi yana shafa sumar kanshi batare da yace komai ba, ganin sun cigaba da maganar su yasashi karasa ficewa dasauri.

Bayan fitarshi baba yadubi mamuh cikin nutsuwa,

"Abinda nakeso daku idan har dagaske auren aka bashi to mu mara masa baya yayi tunda har yafurta, yin hakan yafi fiyeda mu bada gudun mawa wurin lalata tarbiyarsa da ruguza rayuwarsa, saboda yaran zamanin nan da kike ganinsu sai dai abarsu kawai shiyasa komai kankantar yaro ko yarinya idan suka nuna aure sukeso kawai yimusu ka huta domin idanfa baka yimusu ba to watan hanyar zasu bi ta daban,... Ai mu da muke fita waje mune muke kallon abubuwan dake faruwa Rahmatu"

Gyada kai mamuh tayi cikeda gamsuwa tace,

"Hakane Baban asabe ubangiji Allah ya shirya mana zuri'a da sauran al'ummar musulmi"

Daga nan sun jima suna tattauna maganar atsakaninsu.

Abangaren fahad kuwa ko zama baiyi adakin ayiyah ba yadauki abincin shi dake rufe yafice, dakinsu yabude yashiga sai lokacin yaji nutsuwa tazo masa domin da alama su baba bazasu hanashi wannan auren ba zama yayi bayan yarage kayan jikinsa ya zamana daga shi sai vest da gajeren wando, abincin yabude yafara ci nan kuma hankalinsa yakoma kan lissafin abubuwan da zaiyi tofa account dinshi yaduba yaga nawa yake dashi daga nan lissafe lissafe yatashi wanda ya daukeshi tsawon lokaci daga karshe abincin ma barinshi yayi. Sai da yasamu nutsuwa bayan yayi wanka sannan yakira bilkisu wacce tuni harta kwanta amma ba bacci takeyi ba,

"Kaje gida lafiya?"

Shagwabe fuska yayi kamar tana kallonshi,

"Ni wallahi bazan amsa ba tunda ai baki kirani kin tambayeni ba...."

"To ai sai kayi min uzuri dai ko"

"Nayi miki ranki yadade, dama mai gidane yace zaizo gidanku gobe wurin Abba"

"To Allah yakaimu, amma da yaushe zaizo?"

"Da safe naji yace,sai ki sanar dasu"

"Babu matsala Allah yakaimu"

"To saida safe? Ko zamuyi hira?" Yafada dan jan magana,

"A'a saida safen dai" tabashi amsa tana yatsina fuska,

"To kihuta lafiya baby...."

"Thanks" tafada cikeda bacin ran kiranta da baby da yayi,

Daga haka takatse wayar juyi tayi ta gyara kwanciyarta aranta tana cewa,

"Wannan shine Abu kamar da wasa yana shirin zama babba,hamood meyasa kayi min haka? Amma babu komai tunda ban san abinda ke faruwa ba sai dai nayiwa kaina alkawarin zama injiraka har lokacin da Allah zai sake hadani dakai..."

Sake muskutawa tayi cikeda damuwa,

"Lallai yaron nan ni yake kira da baby? Tab ai kuwa dolene ma na yanka masa serious warning wallahi...."

Da bacin rai tayi bacci wanda bata san ko na menene ba amma tafi alakantashi da rashin sanin takamaimai halin da hamood ke ciki da kuma kiranta da baby da fahad yayi.

Koda gari yawaye bayan tafito suna karyawa da ammah take sanar da ita batun zuwan babansu fahad wurin Abba, ai ammah farin cikine ya mamayeta harta kasa boyeshi saida ya fito fili bilkisu tagani,

Shiru tayi aranta tana jin tausayin ammah domin azahirin gaskiya bata jin zata iya zaman aure da wannan karamin yaron kawai dai aure ne na wucin gadi za ayishi da zarar abin sonta yadawo zata koma gareshi domin shine yadace da ita ba fahad ba.

A bangaren fahad kuwa tunda ya kwanta bayan yayi sallar asubah bai tashiba har 9 saida ayiyah tazo ta buga masa kofa tace baba na kiranshi sannan yataso da hanzarinsa yana kokarin zura doguwar rigar jallabiyarsa wadda yacire bayan ya idar da salla. Lokacin da yashiga dakin baba yasameshi yana karin kumallo da kakkauran koko da kosai nan ya durkusa yagaidashi baba ya amsa cikin fara'a kana yace,

"Nayiwa babanka Alhaji Nuhu magana mahaifin salim yanzu haka yashirya ni yake jira zamuje gidansu yarinyar, a ina gidan yake?"

Sunkuyar dakai fahad yayi sannan yasanar dashi, dayake sanannen mutum ne mahaifinsu bilkisun shiyasa baba bai wani wahala wurin gano inda gidan yakeba daga karshe yace fahad din yatashi yatafi. Yana kwance adaki yajiyo fitar baba hakan yasashi jin faduwar gaba babu kakkautawa dakyar yasamu yaji yakoma daidai amma baccin da bai komaba kenan hakane ma yasashi fadawa toilet yayi wanka yafito yashirya sannan yasaka kananan kaya yanufi cikin gida, yana shiga su mamuh na waje suna gyaran waken suya wanda zasuyi awara dashi da rana, ji yayi kamar yakoma dan kunya gashi yau sai yaji duk ya tsargu dasu saboda yanda daga ayiyah har mamuhn suka zubo masa ido gefe daya ga mariya tsugunne arakabe,

"Yaya fahad tattabarunka sunyi sabuwar kinkisa Allah leka kagani"

Dama mafaka yake nema dan haka yanufi dakin barun batare da yakarasa wurinsu ba yana cewa Mariya,

"Haba? Ashe zan baki biyu tunda kece kika fara yimin albishir"

Zuwa yayi ya lelleka nan yahangosu sun doshi goma koma fiye da haka, ma'ajiyar abincinsu yanufa yaje ya ciko musu kwano da hatsi yazo ya watsa musu sannan yakoma wurinsu ayiyah yana hararar Mariya,

"Ke meyasa bakije makaranta ba? Kema gardamar karatu zakiyi ko?"

Kafin Mariya tayi magana ayiyah ta amsa,

"Ka ganta nan da zazzabi tatashi da asibiti ma zan rakata babanku yace inbari anjima inkaita wurin murja nurse makotanmu ta dubata tunda can asibitinma idan anje layine kuma ba lallaima aga likitan ba watakil nurse din za agani"

"To Allah ya sawwake, ina kwananku?" Yafada bayan ya durkusa,

"Lafiya lau ango" inji mamuh, ai baice komaiba yamike yana murmushi yafada dakin ayiyah domin karyawa yanaji mamuh nacewa ayiyah,

"Sai mufara asusu tunda danmu ya lakato aure"

Dariya ayiyah tayi sannan tace,

"Atoh bikin auta guda ai dole anuna bajinta"

Agurguje ya karya yafito yabar gidan yanufi shago saboda yanada ragowar dinkunan da bai karasa ba kuma yaga har masu dinkin sun turo masa kudin dazu da asubah. Acike yasamu shagon kowa yafito harda yan karbar dinki da masu zuwa zaman hira shagon, hamza ya iske asaman kekenshi dan haka yanemi wuri yazauna yana jiran yagama yabashi wuri,

"Yau mutuniyarka zuwanta biyu nemanka ta dubaka taga ko ka fito amma shiru"

Duk da Tj bai fadi sunaba amma yasan husna yake nufi,

"Yar naci kenan, ni garama da ka tuna min bari inyanka atamfar can tata kafin inhau keke"

Atamfar yadauka da almakashi da sauran abunda zai bukata yafita domin yankawa.

Kamar yadda baba yafada shida mahaifin salim sukaje gidansu bilkisu a motar yayansu salim din baffa wanda shine yakaisu, lokacin da sukaje bilkisu tafita wurin aiki sun samu kyakkyawar tarba awurin Abba wanda ya karbesu hannu bibbiyu cikeda girmamawa da mutuntawa, kasancewa abune na manya masu ganin mutuncin juna anan aka kulla magana inda Abba yace yabaiwa fahad bilkisu sannan shi baya son wadannan bidi'o'in masu hana aure yayi karko dan haka nanda watanni biyu sai adaura musu aure yafi ayita dogon zancen nan suna sake shakuwa da juna daga karshe kuma ba asan me zai faruba, duk da baba yana ganin kamar hakan bamai yuyuwa bane duba da su ba karfine dasu kamar gidansu bilkisun ba amma haka yakarbi maganar Abba hannu bibbiyu aranshi yana cewa idan da yuyuwar su daga lokacin bikin sa sake dawowa su nemi alfarma, cikeda mutunta juna sukayi masa sallama suka fito inda yayi musu rakiya har gaban motarsu,wannan fa shi ake kira da babu zato babu tsammani daga zuwa tambaya ansaka ranar aure alhalin shi angon bai tanadi komai ba na biki.

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA....!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*13*

***Daga fahad har bilkisu babu wanda yakeda masaniyar abinda yake faruwa, shi fahad baima koma gidaba sai bayan sallar la'asar wannan dinma yunwa ce ta addabeshi shiyasa yana zuwa gidan ta kan abinci ya fara saida yaji ya koshi sannan yawuce dakinsu yayi wanka daga ayiyah har mamuh babu wanda yayi masa maganar kowa acikinsu kama bakinsa yayi yai shiru, bayan yagama shiryawa yafito yana kokarin rufe daki baba yashigo, kayan hannunsa yakarba sannan yashiga cikin gida baba yana biye dashi, bai san wa zai kaiwa kayanba kasancewar bai san wacce keda girki ba domin su al'adar gidan nan baka gane wacece ke girki saboda komai tare sukeyi wannan dalilinne yasashi ajiye kayan a kofar dakin baba yajuya yana kallon maryam da mariya wadanda ke ta faman kallonsa suna yar dariya kasa kasa,

"Ke Mariya kin warke zaki fara munafurci ko? Bari nazo nakama yarinya sai nayi ball da..."

"Ya akayi kuma? Dawa za ayi kwallo?" Baba yafada bayan yashigo,

"Ahh babu komai baba" fahad ya amsa yana shafa kai,

"To zo ina son ganinka..."

Bin bayan Baba yayi cikin turakarsa, sai da yajira Baban yazauna sannan shima yazauna bayan ya dora habarsa kan gwiwarsa,

"Muhammadu tofa karamar magana tazama babba, naje wurin mahaifin yarinyar nan kamar yadda ya bukata kuma mun tattauna dashi, ya yabeka iya yabo haka kuma ya kaunaceka domin duk mutumin da yaso hada zuri'a dakai to mai kaunarka ne, kuma naji dadi domin gidan da kaje gidane na mutunci da karamci saboda bana tunanin duk nahiyar nan bama cikin kano ba babu wanda bai san mahaifin yarinyar nanba..."

Shigowarsu ayiyah da mamuh ne ya katsewa baba maganar da yakeyi sukayi masa sannu da zuwa sannan suka nemi wuri suka zauna suna saurarensa,

"Yanzu dai zancen da nake maka fahad mutumin nan yabaka yarsa yace baya bukatar komai daga gareka domin har yama sanya ranar aurenku watanni uku, duk da nasan kanada sana'ar yi amma sai nake ganin kamar zaka shiga wani hali saboda aure abune mai wahalar gaske musamman ma a wannan lokacin..."

Shiru fahad yayi yana jin abun kamar amafarki wai shine zai auri bilkisu matar da yake mutukar kauna, maganar babace tadawo dashi cikin hayyacinshi,

"Yanzu menene abinyi? Kaga dai nafarko bakada muhalli domin baka gama ginin da kakeyi ba, na biyu rikon gida dole sai anshirya duk da nasan Allah shine da kowa amma mu ta bangarenmu zamu taimaka maka da abinda zamu iya sannan zan tattaro yayunka ma duk in sanar dasu"

"Baba nida tunanin da nayi ko insaida dayan filina dake digar maharba sai inkarasa ginin?"

"A'a kabar filinka bari dai zamuga abinda za ayi, tashi kaje, zamu shawarta da iyayenka"
Chapter 11 · 0% Book details