Sashe 17
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***Tunda fahad yakwanta bacci bai ko juya ba sai da asubah, tashi yayi yaje yayi alwala yafito yafita masallaci tareda baba suka shigo gidan lokacin harsu mamuh sun fito suna kokarin hada wuta, dakin yakoma bayan sun gaggaisa dasu,har lokacin bilkisu na kwance ta tukunkune acikin mayafi tanata sharar bacci, tashinta yafara yi tatashi tayi salla amma taki tashi dole sai kyaleta yayi ya janyo wayarshi wadda ke jikin sucket tana charge yasoma matsata. Sai karfe shida saura sannan ta farka, akwatinta ta janyo ta bude taciro soson wanka da sabulu sai brush da toothpaste tajiyo ta kalleshi yayi saurin dauke idonshi yamayar kan wayarshi,
"Malam dan bani wuri zanyi wanka..."
Kamar bazai tashiba zuwa can dai yamike da wayarshi ahannu yayi waje, saida ta tabbatar da ficewar yayi sannan ta kwashi duk abubuwan da zata bukata tashiga bathroom, harta fito tashirya tsaf tasaka wata pink din shadda riga da skirt bai shigoba, turarukanta na alfarma da sanyaya zuciya ta dauka ta shafe jikinta dashi sannan taciro mayafi ta zauna mayan ta maida akwatinta mazauninshi, handbag dinta ta bude ta ciro chingum ta saka abakinta ta dauko wayarta ta kunna. Bata dade da kunnawa ba kiran maama yashigo suka gaisa daga nan su Hindu suma suka kakkarba suka gaggaisa, bayan sun gama wayar dasu meenah saiga kiran khulsum,
"Amarya bakya laifi... Amarya kinsha kamshi"
Murmushi bilkisu tayi,
"Zan ramane wallahi, Allah yakaimu lokacin"
"Au danma na kiraki naji ya kika kwana?"
Kafin tabata amsa fahad yashigo direct bathroom yawuce tabishi da kallo,
"Ni lafiya lau natashi malama"
"Shikenan haka akeso ya angon namu?"
"Lallai kam, yana nan lafiya"
"To agaidashi ace sako injini nace ya kular min da kawata"
"Wannan sakon yafi karfina sai dai idan kun hadu ki fada masa da bakinki"
Khulsum nata tsokanarta tana ramawa daga karshe dai sukayi sallama takashe wayar, haka kawai sai kuma tunanin gida yafado mata nan taji kamar tafashe da kuka, Allah sarki rayuwa yanzu idan banda aure me zai rabata da gidansu, dakinta ne yafado mata arai da gadon da take kwanciya da komai nata dake cikin dakin, kiran da yashigo wayar tatane yakatse mata tunanin da takeyi, goggo maigado ce kanwar mahaifiyar Abba wacce aka yimata takwara da bilkisu, dauka tayi cikeda farin ciki domin goggo bilki halinta daban yake tafi iyallo kula da faran faran,
Har yafito daga wankan waya takeyi, tagaisa da wancan ta gaisa da wancan, kayanshi ya dauka yakoma toilet zuwa can yafito yana rataye kayan da ya cire saman kofar toilet din, cumb yadauka yagyara sumarsa sannan yajuya yana kallonta lokacin da yake kokarin shafa turaren amirul hub, ido suka hada ta wani janye nata cikeda sigar harara yana jinta lokacin da tagama wayar,
Zama yazo yayi gefen katifar domin saka sabuwar bakar safar dake hannunshi,
"Hajjaju kin tashi lafiya?"
"Alhamdulillah..."
"Ya bakunta?"
"Lafiya"
Murmushi yayi ya kalleta,
"Bari naje nakarbo miki breakfast anjima sai na rakaki kishiga cikin gidan ku gaisa dasu"
Jijjiga kai kawai tayi amma bata yi magana ba hakan yabashi damar mikewa yafita, yana shiga cikin gidan masu tsokanarshi suka fara suna fadin,
"Ga ango ga ango..."
Su Mariya kuwa rugowa sukayi suka rirrike hannunshi,
"Ya fahad muje mugaida Anty yanzu?"
"A'a Mariya ba yanzu ba, yanzu hutawa take zan kai mata abinci taci idan tagama zata shigo ku ganta"
Dakin ayiyah ya furmutsa yashiga duk da dakin tafare yake da baki amma haka ya tsattsallakesu ya isa gareta, cikeda farin ciki ta amsa gaisuwarsa sannan tace yaje yasamu yaya asabe yakarbi abincin karin kumallon bilkisu, fita yayi bai tsaya jin dan bikin da abokan wasa keyi masa ba wadanda ke cikin dakin, wurinsu anty fauzy yaje suna zazzaune kofar kitchen suna dama kunun farar shinkafa can gefe daya kuma masu suyar fanke nayi ga kosai shima anata sakawa,
"Ah kaga shalelen ayiyah ango..."
Dariya yayi yaduka agabansu yana cewa,
"Kai yaya asabe bari kiran angon nan dan Allah"
"To ya kwanan amarya?"
"Tana nan lafiya, yanzu ma abincin ta nazo karba"
"Dakyau ango mijin amarya..."
Mikewa yayi tsaye yana kallon anty Fauzy wacce rufe bakinta kenan,
"Anty fauziyya kema haka zakice? Shikenan bani abincin natafi"
"Za abaka ai daina gaggauta, da alama gaba daya hankalinka na can..." Anty juwairiyya dake cikin kitchen itada anty kubra tafada tana dariya, shi sam baima gansu ba wallahi sai yanzu ashe suna ciki suna hadawa amarya breakfast,
"Ohh God....,ashe yan sa ido ana ciki..."
"Mudai ga abincin amaryarka sai ka sakar mana Mara muyi fitsari" Anty kubra tafada lokacin da take fiffito masa da abincin, kayan sunyi masa yawa dole sai su mariya yakira suka tayashi dauka domin bazai yuyu yadauka shi kadai ba, har cikin dakin suka kai masa abin mamaki sai yaga bilkisu ta sake dasu sosai harda cemusu su zauna suci abincin tare, harara ya zabga musu babu shiri suka fice simi simi, tabe baki tayi tagyara kishingidar da tayi, shi wallahi wannan mulkin nata dariya yake bashi, abubuwan da aka girka yafara dubawa, chips ne aka yimasa wani hadi na musamman da dan salad sai farfesun kayan cikin saniya sai bread da ruwan zafi,
"Ranki yadade ga abincin... Bismillah"
"Ok..."
A flate daya ya zuba musu komai yasa fork yafara ci, wayarshi ce ta katse masa hanzari, husnah ce bai san lokacin da ya girgiza kai ba yace,
"Allah sarki husnah bakiyi fushi ba?"
"A'a prince banyiba, angama biki lafiya? Allah sanya alkhairi yabada zaman lafiya agaida min da ita"
Jin abinda husna tace sai tausayinta yasake kamashi bai san da biyu ta kirashi ba dan saida kawayenta suka tirsasata sukace tayi masa kirsa irinta mata ta nuna bata dauki auren da yayi da zafiba karta nuna masa komai amma da zarar burinta yacika ta nuna musu tafisu iya wulakanci, wannan dalilinne yasata dannar zuciyarta ta kirashi amma fa can kasan ranta kishine fal dankare da tsanar bilkisu wadda bata ma san da ita ba,
"Amin husnah nagode sosai..."
"Babu komai Prince ai kafi haka agareni"
Ita dai bilkisu kallonshi ta tsaya tanayi yayinda shikuma keta yiwa husna godiya, cin abincin shi yaci gaba dayi zuwa can wayarshi tasake yin kara ya dauka yana dariya bayan yasaka a hands free,
"Kai gwauro ya akayi...?" Yafada yana dariyar shakiyanci, daga can bangaren salim yace,
"Malam wallahi yau kasan wanda zaiyi maka gadin gidanka nidai nagaji tahowa zanyi"
"Karka damu yau masu gidanne zasu kwana aciki, insha Allah yau anan zamu kwana kai kuma kaje ka karata da tsohuwar katifarka..."
"Ohh hakama zakace? To babu komai ai akwai gaba..."
"Wasa nake abokina... Yanzu kadan bada jimawa ba za akawo muku breakfast kaida babban yaya, dan Allah amika min gaisuwa"
Kit yakashe wayar yana yiwa salim dariyar shakiyanci, ita kallonshi ma kawai ta tsaya tana yi tana mamakin yanda yake da bakin tsiya,
"Hajjaju ya akayi ne? Nace kizo kici abinci kin ki ban saniba ko kina jin nauyina ne, amma ai ko za ayi fulako bai cancanta ayiwa mijiba domin shi sirrinka ne...."
Wani kallo tayi masa wanda ita kadai tasan ma'anarsa,
"Miji...? Miji kuma?"
Tsayawa yayi da cin abincin da yakeyi ya kalleta,
"Ina da wani sunanne da wuce wannan awurinki? Duniya da sauran jama'ar cikinta sun gama shaidawa ni fahad mijinki ne asalima harda sadaki na baki naira dubu talatin lakadan ba ajalan ba right....?"
"To ko in dawo maka da abinka?"
Girgiza kanshi yayi ya langabe kai yaci gaba da cin abincinshi,
"A'a, ni ai ban baki dan kisake dawo min dashi ba ranki yadade..."
Shiru tayi taci gaba da danne dannen wayar da takeyi tun dazu, zuwa can yasake kallonta yace,
"Kefa nake jira ki karya mu fita, dagaske yau zamu bar gidan nan mukoma namu..."
Tsam ta tsaya da abinda takeyi itama takai kallonta gareshi,
"To yanzu idan nashiga ciki me zanyi? Kasan dai ni ba sanin al'adarku nayi ba..."
"Karki damu zaki sani sannu ahankali"
"Dan rainin wayo...." Tafada acikin ranta sannan ta ajiye wayar hannunta ta janye flate din gabanshi zuwa gabanta ta dauki fork tasoma ci, kallonta yatsaya yi kafin ya nisa,
"Ranki yadade ai ba koshi nayiba..."
"Duk abincin da kaci daga daren jiya zuwa yanzu?"
"To ai na kwana biyu rabona da abinci fa"
Kafada ta daga,baiyi kasa agwiwa ba yasake mayar da nasa cokalin cikin flate din yaci gaba da ci atakaice dai shi yaci fiyeda rabin abincin, yarigata tashi dan haka yasake kintsawa sosai yasha hula sai kamshi yake, abokanshi sai kiranshi sukeyi awaya ana tayashi murna da fatan alkhairi, hannayensa duka biyu ya zuba cikin aljihun rigarshi yana zagaye dakin yana jiranta tagama, saida tagama jan ajinta da shan kamshinta sannan ta mike bayan tasake gyara fuskarta sosai,turare tasake fesawa jikinta sannan ta dauki babban mayafi tayafa tarufe fuskarta, dariya yafarayi ahankali wayarta kawai ta dauka amma yace mata,
"Da dai kin dauki handbag din naki da zaifi..."
Batare da tace komai ba ta dauka tafita, rufe dakin yayi sannan suka nufi cikin gidan ai tana jiyo hayaniyar mutane tayi azamar sake lullube fuskarta saura kadan tayi karo da itacen da aka girke domin dafa sanwa, hannunta yayi saurin rikowa dama tun adaren jiya yake da wannan burin sakamakon tafiya da hankalinshi da kunshinta yayi, babu damar yin musu domin bata ganin gabanta sosai kanta akasa yake sannan mayafin mai duhune sosai, har dakin ayiyah ya shigar da ita ya zaunar da ita nan fa aka shiga zuba guda ana shewa, shidai ficewa yayi yabar dakin duk kuma sai taji wani iri wato wurima da wanda kasani dadi gareshi amma idan akace baka san kowaba to baka iya sakewa, tana jiyoshi atsakar gida suna yarawa da kakanninsa wato abokan wasanshi yana cemusu,
"Ni duk kunyi min tsufa, ga matata can duk tafiku kyau kuje ku ganta gyalenta kadai ya isa ya siyeku gaba daya...."
Daga haka yagudu bata sake juyo maganarshi ba, duk kuma sai tashiga kadaici danma anata zuwa gaisheta kamar wata sarauniya, tana zaune shiru shiru sa'arta daya Maryam da Mariya na kewaye da ita nan tayi masa text massage tana daga tukunkune cikin mayafi,
_Wai kana inane?_
Babu jimawa saiga reply yadawo mata dashi,
_Ina zuwa nan bada jimawa ba._
"Malam dan bani wuri zanyi wanka..."
Kamar bazai tashiba zuwa can dai yamike da wayarshi ahannu yayi waje, saida ta tabbatar da ficewar yayi sannan ta kwashi duk abubuwan da zata bukata tashiga bathroom, harta fito tashirya tsaf tasaka wata pink din shadda riga da skirt bai shigoba, turarukanta na alfarma da sanyaya zuciya ta dauka ta shafe jikinta dashi sannan taciro mayafi ta zauna mayan ta maida akwatinta mazauninshi, handbag dinta ta bude ta ciro chingum ta saka abakinta ta dauko wayarta ta kunna. Bata dade da kunnawa ba kiran maama yashigo suka gaisa daga nan su Hindu suma suka kakkarba suka gaggaisa, bayan sun gama wayar dasu meenah saiga kiran khulsum,
"Amarya bakya laifi... Amarya kinsha kamshi"
Murmushi bilkisu tayi,
"Zan ramane wallahi, Allah yakaimu lokacin"
"Au danma na kiraki naji ya kika kwana?"
Kafin tabata amsa fahad yashigo direct bathroom yawuce tabishi da kallo,
"Ni lafiya lau natashi malama"
"Shikenan haka akeso ya angon namu?"
"Lallai kam, yana nan lafiya"
"To agaidashi ace sako injini nace ya kular min da kawata"
"Wannan sakon yafi karfina sai dai idan kun hadu ki fada masa da bakinki"
Khulsum nata tsokanarta tana ramawa daga karshe dai sukayi sallama takashe wayar, haka kawai sai kuma tunanin gida yafado mata nan taji kamar tafashe da kuka, Allah sarki rayuwa yanzu idan banda aure me zai rabata da gidansu, dakinta ne yafado mata arai da gadon da take kwanciya da komai nata dake cikin dakin, kiran da yashigo wayar tatane yakatse mata tunanin da takeyi, goggo maigado ce kanwar mahaifiyar Abba wacce aka yimata takwara da bilkisu, dauka tayi cikeda farin ciki domin goggo bilki halinta daban yake tafi iyallo kula da faran faran,
Har yafito daga wankan waya takeyi, tagaisa da wancan ta gaisa da wancan, kayanshi ya dauka yakoma toilet zuwa can yafito yana rataye kayan da ya cire saman kofar toilet din, cumb yadauka yagyara sumarsa sannan yajuya yana kallonta lokacin da yake kokarin shafa turaren amirul hub, ido suka hada ta wani janye nata cikeda sigar harara yana jinta lokacin da tagama wayar,
Zama yazo yayi gefen katifar domin saka sabuwar bakar safar dake hannunshi,
"Hajjaju kin tashi lafiya?"
"Alhamdulillah..."
"Ya bakunta?"
"Lafiya"
Murmushi yayi ya kalleta,
"Bari naje nakarbo miki breakfast anjima sai na rakaki kishiga cikin gidan ku gaisa dasu"
Jijjiga kai kawai tayi amma bata yi magana ba hakan yabashi damar mikewa yafita, yana shiga cikin gidan masu tsokanarshi suka fara suna fadin,
"Ga ango ga ango..."
Su Mariya kuwa rugowa sukayi suka rirrike hannunshi,
"Ya fahad muje mugaida Anty yanzu?"
"A'a Mariya ba yanzu ba, yanzu hutawa take zan kai mata abinci taci idan tagama zata shigo ku ganta"
Dakin ayiyah ya furmutsa yashiga duk da dakin tafare yake da baki amma haka ya tsattsallakesu ya isa gareta, cikeda farin ciki ta amsa gaisuwarsa sannan tace yaje yasamu yaya asabe yakarbi abincin karin kumallon bilkisu, fita yayi bai tsaya jin dan bikin da abokan wasa keyi masa ba wadanda ke cikin dakin, wurinsu anty fauzy yaje suna zazzaune kofar kitchen suna dama kunun farar shinkafa can gefe daya kuma masu suyar fanke nayi ga kosai shima anata sakawa,
"Ah kaga shalelen ayiyah ango..."
Dariya yayi yaduka agabansu yana cewa,
"Kai yaya asabe bari kiran angon nan dan Allah"
"To ya kwanan amarya?"
"Tana nan lafiya, yanzu ma abincin ta nazo karba"
"Dakyau ango mijin amarya..."
Mikewa yayi tsaye yana kallon anty Fauzy wacce rufe bakinta kenan,
"Anty fauziyya kema haka zakice? Shikenan bani abincin natafi"
"Za abaka ai daina gaggauta, da alama gaba daya hankalinka na can..." Anty juwairiyya dake cikin kitchen itada anty kubra tafada tana dariya, shi sam baima gansu ba wallahi sai yanzu ashe suna ciki suna hadawa amarya breakfast,
"Ohh God....,ashe yan sa ido ana ciki..."
"Mudai ga abincin amaryarka sai ka sakar mana Mara muyi fitsari" Anty kubra tafada lokacin da take fiffito masa da abincin, kayan sunyi masa yawa dole sai su mariya yakira suka tayashi dauka domin bazai yuyu yadauka shi kadai ba, har cikin dakin suka kai masa abin mamaki sai yaga bilkisu ta sake dasu sosai harda cemusu su zauna suci abincin tare, harara ya zabga musu babu shiri suka fice simi simi, tabe baki tayi tagyara kishingidar da tayi, shi wallahi wannan mulkin nata dariya yake bashi, abubuwan da aka girka yafara dubawa, chips ne aka yimasa wani hadi na musamman da dan salad sai farfesun kayan cikin saniya sai bread da ruwan zafi,
"Ranki yadade ga abincin... Bismillah"
"Ok..."
A flate daya ya zuba musu komai yasa fork yafara ci, wayarshi ce ta katse masa hanzari, husnah ce bai san lokacin da ya girgiza kai ba yace,
"Allah sarki husnah bakiyi fushi ba?"
"A'a prince banyiba, angama biki lafiya? Allah sanya alkhairi yabada zaman lafiya agaida min da ita"
Jin abinda husna tace sai tausayinta yasake kamashi bai san da biyu ta kirashi ba dan saida kawayenta suka tirsasata sukace tayi masa kirsa irinta mata ta nuna bata dauki auren da yayi da zafiba karta nuna masa komai amma da zarar burinta yacika ta nuna musu tafisu iya wulakanci, wannan dalilinne yasata dannar zuciyarta ta kirashi amma fa can kasan ranta kishine fal dankare da tsanar bilkisu wadda bata ma san da ita ba,
"Amin husnah nagode sosai..."
"Babu komai Prince ai kafi haka agareni"
Ita dai bilkisu kallonshi ta tsaya tanayi yayinda shikuma keta yiwa husna godiya, cin abincin shi yaci gaba dayi zuwa can wayarshi tasake yin kara ya dauka yana dariya bayan yasaka a hands free,
"Kai gwauro ya akayi...?" Yafada yana dariyar shakiyanci, daga can bangaren salim yace,
"Malam wallahi yau kasan wanda zaiyi maka gadin gidanka nidai nagaji tahowa zanyi"
"Karka damu yau masu gidanne zasu kwana aciki, insha Allah yau anan zamu kwana kai kuma kaje ka karata da tsohuwar katifarka..."
"Ohh hakama zakace? To babu komai ai akwai gaba..."
"Wasa nake abokina... Yanzu kadan bada jimawa ba za akawo muku breakfast kaida babban yaya, dan Allah amika min gaisuwa"
Kit yakashe wayar yana yiwa salim dariyar shakiyanci, ita kallonshi ma kawai ta tsaya tana yi tana mamakin yanda yake da bakin tsiya,
"Hajjaju ya akayi ne? Nace kizo kici abinci kin ki ban saniba ko kina jin nauyina ne, amma ai ko za ayi fulako bai cancanta ayiwa mijiba domin shi sirrinka ne...."
Wani kallo tayi masa wanda ita kadai tasan ma'anarsa,
"Miji...? Miji kuma?"
Tsayawa yayi da cin abincin da yakeyi ya kalleta,
"Ina da wani sunanne da wuce wannan awurinki? Duniya da sauran jama'ar cikinta sun gama shaidawa ni fahad mijinki ne asalima harda sadaki na baki naira dubu talatin lakadan ba ajalan ba right....?"
"To ko in dawo maka da abinka?"
Girgiza kanshi yayi ya langabe kai yaci gaba da cin abincinshi,
"A'a, ni ai ban baki dan kisake dawo min dashi ba ranki yadade..."
Shiru tayi taci gaba da danne dannen wayar da takeyi tun dazu, zuwa can yasake kallonta yace,
"Kefa nake jira ki karya mu fita, dagaske yau zamu bar gidan nan mukoma namu..."
Tsam ta tsaya da abinda takeyi itama takai kallonta gareshi,
"To yanzu idan nashiga ciki me zanyi? Kasan dai ni ba sanin al'adarku nayi ba..."
"Karki damu zaki sani sannu ahankali"
"Dan rainin wayo...." Tafada acikin ranta sannan ta ajiye wayar hannunta ta janye flate din gabanshi zuwa gabanta ta dauki fork tasoma ci, kallonta yatsaya yi kafin ya nisa,
"Ranki yadade ai ba koshi nayiba..."
"Duk abincin da kaci daga daren jiya zuwa yanzu?"
"To ai na kwana biyu rabona da abinci fa"
Kafada ta daga,baiyi kasa agwiwa ba yasake mayar da nasa cokalin cikin flate din yaci gaba da ci atakaice dai shi yaci fiyeda rabin abincin, yarigata tashi dan haka yasake kintsawa sosai yasha hula sai kamshi yake, abokanshi sai kiranshi sukeyi awaya ana tayashi murna da fatan alkhairi, hannayensa duka biyu ya zuba cikin aljihun rigarshi yana zagaye dakin yana jiranta tagama, saida tagama jan ajinta da shan kamshinta sannan ta mike bayan tasake gyara fuskarta sosai,turare tasake fesawa jikinta sannan ta dauki babban mayafi tayafa tarufe fuskarta, dariya yafarayi ahankali wayarta kawai ta dauka amma yace mata,
"Da dai kin dauki handbag din naki da zaifi..."
Batare da tace komai ba ta dauka tafita, rufe dakin yayi sannan suka nufi cikin gidan ai tana jiyo hayaniyar mutane tayi azamar sake lullube fuskarta saura kadan tayi karo da itacen da aka girke domin dafa sanwa, hannunta yayi saurin rikowa dama tun adaren jiya yake da wannan burin sakamakon tafiya da hankalinshi da kunshinta yayi, babu damar yin musu domin bata ganin gabanta sosai kanta akasa yake sannan mayafin mai duhune sosai, har dakin ayiyah ya shigar da ita ya zaunar da ita nan fa aka shiga zuba guda ana shewa, shidai ficewa yayi yabar dakin duk kuma sai taji wani iri wato wurima da wanda kasani dadi gareshi amma idan akace baka san kowaba to baka iya sakewa, tana jiyoshi atsakar gida suna yarawa da kakanninsa wato abokan wasanshi yana cemusu,
"Ni duk kunyi min tsufa, ga matata can duk tafiku kyau kuje ku ganta gyalenta kadai ya isa ya siyeku gaba daya...."
Daga haka yagudu bata sake juyo maganarshi ba, duk kuma sai tashiga kadaici danma anata zuwa gaisheta kamar wata sarauniya, tana zaune shiru shiru sa'arta daya Maryam da Mariya na kewaye da ita nan tayi masa text massage tana daga tukunkune cikin mayafi,
_Wai kana inane?_
Babu jimawa saiga reply yadawo mata dashi,
_Ina zuwa nan bada jimawa ba._