Sashe 28
Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin irin dariyar da sukayi yasata tashi gaba daya tabar musu wurin kafadarta dauke da Minal, kamar da wasa take bin hanyar da tagani wacce zata kaika sassa daban daban dake cikin asibitin, aranta sai yaba tsari da haduwar asibitin take yi wani daki tawuce wanda shine na karshe ajerin dakunan dake bangaren, ahankali yamaida kofar yarufe yafito yana rikeda mukullin motarsa yana dan sosa kunnenshi na dama dashi, wani kamshine ya mamaye wurin, daf da zata sha wata kwana wacce zata kaika pharmacy wayarta ta subuce ta fadi kasan tiles din dake shimfide awurin kadan yarage yataka wayar tata saboda irin garawar da wayar tayi ita kadai amma sai Allah ya takaita, sunkuyawa yayi yadauko wayar yamika mata daidai lokacin da ta jiyo hannunta daya ta mika masa domin dayan tarike Minal dashi, tun daga kafarshi tasoma kallonshi, farin takalmine akafar tashi yana sanye da shadda ruwan kasa da hula sai farin glass dake idonshi, kamar hadin baki idanuwansu suka sarke cikin na juna, wata faduwar gabace mai girma ta saukar mata wacce tayi sanadiyyar sakin Minal dake hannunta sai shine yayi azamar tare minal din ya rungume yana yiwa bilkisu wani irin kallo mai dauke da alamomin tambayoyi daban daban, cikin rawar jiki da rawar baki ta furta,
"Hamood...."
Shi dinma cikeda rawar baki yace,
"Bilkisu.... Kece ko kuwa mafarki nake?
*Book dinnan na kudine idan kina bukata kibiya saiki karanta.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA.....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*26&27*
***Daga ita harshi kasa sake furta koda kalma daya sukayi sai kallon juna da suketa faman yi kamar yaune suka soma ganin juna,
"Bilkisu kin sakani acikin mutukar damuwa, Allah yasa ba aure kikayi har kika haihu ba..."
"Haba hamood har yaushe zanyi aure inhaihu batare da saninka ba, najiraka najiraka har nagaji, na nemeka duk inda nasan zan iya samunka amma nagaza daga karshe dole tasa na fidda wani mijin nayi au..."
Arazane ya kalleta har yana cin tuntuben matsawa kusa da ita,
"Wai kina nufin kinyi aure? Wannan shine abinda bazan taba iya jurewa ba bilkisu, rashinki agareni babbar matsala ce wadda bata da magani... Bazan taba iya jurewa ba"
"Hamood nikaina wannan auren nayi shine kawai arashinka amma tunda...."
"Bilkisu karki cemin komai, yazama dole ki dawo gareni muje mu shimfida daddadar rayuwar da muka jima muna tsarawa kanmu, yazama dole mu cika burinmu da alkawarin da muka jima muna yiwa juna..... Dole ki kashe aurenki kidawo gareni domin kece farin cikina..."
Duk da ba acikin nutsuwarta takeba domin jikinta inbanda rawa babu abinda yakeyi amma hakan bai hanata murmusawa ba,
"Hamood wallahi kaine burina, kaine mijin da nadade ina yiwa kaina mafarkin samu dan haka yanzu lokaci yayi, kai dai kawai kabani dan lokaci kankani zanyi handling komai...."
"Bilkisu sai nake ganin kamar idan kika tafi yanzu bazan sake ganinki ba..."
"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka ni takace kai nawane kamar yadda muka dade muna yiwa juna fata, bani Minal intafi saboda kar wani acikin sisters dina yazo yaganmu"
"To ai sai kibani number dinki saboda ta wannan hanyar ne kadai zan rinka sanin halin da kike ciki..."
Batayi musuba ta rubuta masa awayarshi tabashi takarbi Minal, yana tafe yana waiwayenta itama haka har suka bacewa juna tana shawo kwana sukayi kicibus da meenah wacce tataho nemanta domin zasu tafi gida abban minal yazo daukarsu,
"Adda maigado ina kika shigane mukayita dubaki shiru gashi wayarki taki shiga?"
Murmushin dole ta kakalo takalli meenah,
"Wayarce tafadi wlhi inajin sim din yagoce..."
Jerawa sukayi suka tafi meenah sai hira take yimata amma ina hankalinta ita gaba daya ba awurin yakeba, sam yanzu bata cikin nutsuwarta, ganin hamood yatada mata tsohuwar soyayyar da ta jima tanayi masa domin yanzu ji take zata iya yin komai dan ta kashe kaddararren auren nan na fahad taje ta auri hamood dinta,
Sama sama suka gaisa da baban minal sukayi sallama da kannen nata suka tafi suna tafiya tanemi wuri ita kadai ta zauna tana tunanin menene abinyi? Anty fauzy ce tataho wurinta tana murmushi,
"Hajjaju to ga mijinki can yatashi yana ta yiwa mutane daru akan shan magani sai kije kibashi..."
Mikewa tayi zuciyarta tana suya domin sam fahad bai dace da itaba hamood shine wanda yadace yazama mijinta domin irin mai shekarunsa takeso 35 a matsayinta na yar shekara 30 ba wai fahad ba dan 25,zuciyarta babu dadi tashiga dakin da yake duk yabi ya ruda mutane, ganinta yasa su ayiyah fita aka barsu su biyu sai salim na cikon uku, zama tayi gefen gadon ta dauki maganin ta mika masa baiyi musuba yakarba yana babbata fuska.
Tamkar zaiyi kuka haka yake taune maganin yana korawa da ruwa har ya shanye su tass komawa yayi yamaida kansa bisa pillow ya kwantar yana hararar salim wanda ke zaune yana kallonsu,
"Baby zansha sweet bakina daci...."
Batace masa komai ba amma yaga amsar maganarshi acikin idanuwanta,sake bata rai tayi tajanyo handbag dinta ta bude ta ciro yar karamar milk chocolate tabashi. Tunda magrib takawo jiki tace zata tafi gida babbata rai fahad yashiga yi domin shi idan ta son ranshi za abi abar bilkisu ta kwana dashi ba ya Abba ba,yauma kamar jiya dasu mariya aka hadata dan su bita su tayata kwana duk da ita bata so hakanba domin tana son sakewa tayi waya da hamood sosai adaren yau,
Sam yau batayi garajen hada daki dasu maryam ba domin a falo tayi shimfidarta sukuma tabarsu acikin bedroom, zama tayi ta harde kafafuwanta kan katifar da fahad yake kwana, tana sanye da rigar bacci fara tas mai santsi iya gwiwa sai bakar hula akanta, daman jiran kiranshi takeyi shiyasa kiran na shigowa tayi murmushi ta dauka tana kwantar da murya saboda dare ne,
"My sweetheart yakike? Yanzu dan Allah menene abinyi? Ni nafi son kiyi gaggawar dawowa gareni"
Murmushin jin dadi tayi,
"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka very soon zan zama mallakinka"
"Are u sure?"
"Am 100% sure hamood...."
Dariya sukayi atare lokaci guda, sun jima sun bata lokaci sosai suna shan hira domin har wurin karfe 1 nadare suka kai yana sanar da ita abubuwan da suka faffaru saida bacci ya takurawa bilkisu sannan sukayi sallama.
Washe gari da safe bayan ta sallami su mariya sun tafi sake kwanciyarta tayi har saida hamood yakirata sannan tatashi, bayan sun gama waya tashiga wanka tashirya sannan tatafi asibiti amma yau bataje da wuriba kamar jiya shi dai fahad yana kwance ya kosa yaga zuwanta, dauke da basket din abinci ta shiga dakin tasha yaluwar Arabian gown mai manyan stones ajiki tayane kanta da wani mayafi mai kauri milk colour, tunda suka gaisa da ya Abba bata sake furta komai ba, fahad sai kallonta yake taki kulashi wannan dalilinne yasashi niyyar jan magana, shagwabe fuska yayi,
"Baby inata kiranki ban sameki ba, dama zan fada mikine ki taho min da kayana gashi yanzu sai na ya abba nasa saboda dazu ya gyara min jikina..."
Jijjiga kai tayi tana kallon wayarta,
"May be network problem ne"
"To kibani abinci inci saboda zan sha magani"
Dariya Abba yayi yana tattara kayansa zai fita,
"Yaro yasamu sauyin yanayi wato yanzu da kanka ma kake cewa abaka magani kasha ah lallai angaida bilkisu..."
Murmushin yake tayi tatashi ta zuba masa potatoes plan din da ta iyo sannan ta hada masa tea dan kadan, yauma kamar jiya da taimakonta yaci abincin sannan yasha magani, haka tawuni acikin wani hali, hali na rashin walwala domin ita bata ki a sallami fahad ayauba su koma gida inyaso ayita takare, yauma magrib nayi ta tafi gida itada su maryam, lokacin bacci nayi suka sha hirarsu da hamood.
Gaba daya fahad yakasa gane kanta a yan kwanakin nan ada tana sakar masa fuska suyi wasa da dariya wani lokacin har tsokanarta yakeyi amma yanzu tadaina sai shan kunu da daure fuska, ita kuma anata bangaren kawai so take yawarke a sallameshi suje gida ayi wacce za ayi domin hamood yace baya son bikinsu ya dauki dogon lokaci yafiso ayishi kwana kusa, kullum sai sunyi waya dashi fiyeda sau uku wani lokacin ne ma idan tana cikin mutane bata yarda ta dauka. Yau kam tun kafin taje asibitin husna taje duba fahad itada kawayenta domin kullum idan taje shagonsu bata samunshi sai ace baizo ba daga karshe dai su hamza suka fada mata fahad baida lafiya, wahala sosai tayi masa kamar ba student ba domin harda girki da fruits ta siya ta kai masa, suna tafiya bilkisu na zuwa shiyasa basu haduba tadai ga kayan dubiya amma bata san waye yakawo ba.
Satin fahad biyu a asibiti aka sallameshi domin jiki yayi kyau kuma babu laifi ya murmure sosai kamar ba majinyaci ba, tunda suka koma gida ya fuskanci akwai matsala domin bilkisu ta kafa ta tsare, duk da dai batace masa komai ba amma daure fuskar da take tayi ya isa yasanar dashi akwai matsala shi dai baice mata komai ba har dare, yana zaune gaban dressing mirror bayan yafito daga wanka da kayan bacci ajikinshi riga armless da wando iya cinya tashigo dakin, zama tayi gefen gado tana kallonshi so take tayi masa maganar amma bata san ta inda yadace tafara ba dole sai hakura tayi domin ta sake dan bashi lokaci. Bayan kwana biyu tadawo daga aiki yana kwance falo tawuce bedroom yau dai ta daura aniyar sanar dashi inyaso komai ta fanjama fanjam domin hamood ya matsa da son ganin fitowarta, fitowa tasake yi daga cikin bedroom tazo ta zauna tana fuskantarsa,
"Fahad.... Dan Allah inaso zamuyi magana..."
Kai yadaga mata bayan ya tattaro gaba daya hankalinsa gareta,
"So nake ka sawwake min..."
Kallonta yayi cikin rashin fahimta,
"Kamar ya fa...?"
"Ina nufin so nake ka sakeni...."
Tashi zaune yayi babu shiri yana kallonta,
"In sakeki? Laifin me kikayi min da zan sakeki? Anya kuwa kin san abinda kike fada?"
"Nasan abinda nake fada mana, auren ne bana bukatarsa yanzu shiyasa nace ka sawwake min"
Murmushi taga yayi sannan yamike yana mika,
"Allah ya kyauta, ni wallahi da zaki taimaka ma da kin hau kaina kinyi birgima sosai ko zan samu gajiyar dake jikin nan nawa marar dalili ta baje amma nasan bayi zakiyi ba, bari kawai natafi filin ball naje na basar acan...."
"Hamood...."
Shi dinma cikeda rawar baki yace,
"Bilkisu.... Kece ko kuwa mafarki nake?
*Book dinnan na kudine idan kina bukata kibiya saiki karanta.*
*_Ummi Shatu_*
© *HASKE WRITERS ASSO.*
*KAMAR DA WASA.....!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
*26&27*
***Daga ita harshi kasa sake furta koda kalma daya sukayi sai kallon juna da suketa faman yi kamar yaune suka soma ganin juna,
"Bilkisu kin sakani acikin mutukar damuwa, Allah yasa ba aure kikayi har kika haihu ba..."
"Haba hamood har yaushe zanyi aure inhaihu batare da saninka ba, najiraka najiraka har nagaji, na nemeka duk inda nasan zan iya samunka amma nagaza daga karshe dole tasa na fidda wani mijin nayi au..."
Arazane ya kalleta har yana cin tuntuben matsawa kusa da ita,
"Wai kina nufin kinyi aure? Wannan shine abinda bazan taba iya jurewa ba bilkisu, rashinki agareni babbar matsala ce wadda bata da magani... Bazan taba iya jurewa ba"
"Hamood nikaina wannan auren nayi shine kawai arashinka amma tunda...."
"Bilkisu karki cemin komai, yazama dole ki dawo gareni muje mu shimfida daddadar rayuwar da muka jima muna tsarawa kanmu, yazama dole mu cika burinmu da alkawarin da muka jima muna yiwa juna..... Dole ki kashe aurenki kidawo gareni domin kece farin cikina..."
Duk da ba acikin nutsuwarta takeba domin jikinta inbanda rawa babu abinda yakeyi amma hakan bai hanata murmusawa ba,
"Hamood wallahi kaine burina, kaine mijin da nadade ina yiwa kaina mafarkin samu dan haka yanzu lokaci yayi, kai dai kawai kabani dan lokaci kankani zanyi handling komai...."
"Bilkisu sai nake ganin kamar idan kika tafi yanzu bazan sake ganinki ba..."
"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka ni takace kai nawane kamar yadda muka dade muna yiwa juna fata, bani Minal intafi saboda kar wani acikin sisters dina yazo yaganmu"
"To ai sai kibani number dinki saboda ta wannan hanyar ne kadai zan rinka sanin halin da kike ciki..."
Batayi musuba ta rubuta masa awayarshi tabashi takarbi Minal, yana tafe yana waiwayenta itama haka har suka bacewa juna tana shawo kwana sukayi kicibus da meenah wacce tataho nemanta domin zasu tafi gida abban minal yazo daukarsu,
"Adda maigado ina kika shigane mukayita dubaki shiru gashi wayarki taki shiga?"
Murmushin dole ta kakalo takalli meenah,
"Wayarce tafadi wlhi inajin sim din yagoce..."
Jerawa sukayi suka tafi meenah sai hira take yimata amma ina hankalinta ita gaba daya ba awurin yakeba, sam yanzu bata cikin nutsuwarta, ganin hamood yatada mata tsohuwar soyayyar da ta jima tanayi masa domin yanzu ji take zata iya yin komai dan ta kashe kaddararren auren nan na fahad taje ta auri hamood dinta,
Sama sama suka gaisa da baban minal sukayi sallama da kannen nata suka tafi suna tafiya tanemi wuri ita kadai ta zauna tana tunanin menene abinyi? Anty fauzy ce tataho wurinta tana murmushi,
"Hajjaju to ga mijinki can yatashi yana ta yiwa mutane daru akan shan magani sai kije kibashi..."
Mikewa tayi zuciyarta tana suya domin sam fahad bai dace da itaba hamood shine wanda yadace yazama mijinta domin irin mai shekarunsa takeso 35 a matsayinta na yar shekara 30 ba wai fahad ba dan 25,zuciyarta babu dadi tashiga dakin da yake duk yabi ya ruda mutane, ganinta yasa su ayiyah fita aka barsu su biyu sai salim na cikon uku, zama tayi gefen gadon ta dauki maganin ta mika masa baiyi musuba yakarba yana babbata fuska.
Tamkar zaiyi kuka haka yake taune maganin yana korawa da ruwa har ya shanye su tass komawa yayi yamaida kansa bisa pillow ya kwantar yana hararar salim wanda ke zaune yana kallonsu,
"Baby zansha sweet bakina daci...."
Batace masa komai ba amma yaga amsar maganarshi acikin idanuwanta,sake bata rai tayi tajanyo handbag dinta ta bude ta ciro yar karamar milk chocolate tabashi. Tunda magrib takawo jiki tace zata tafi gida babbata rai fahad yashiga yi domin shi idan ta son ranshi za abi abar bilkisu ta kwana dashi ba ya Abba ba,yauma kamar jiya dasu mariya aka hadata dan su bita su tayata kwana duk da ita bata so hakanba domin tana son sakewa tayi waya da hamood sosai adaren yau,
Sam yau batayi garajen hada daki dasu maryam ba domin a falo tayi shimfidarta sukuma tabarsu acikin bedroom, zama tayi ta harde kafafuwanta kan katifar da fahad yake kwana, tana sanye da rigar bacci fara tas mai santsi iya gwiwa sai bakar hula akanta, daman jiran kiranshi takeyi shiyasa kiran na shigowa tayi murmushi ta dauka tana kwantar da murya saboda dare ne,
"My sweetheart yakike? Yanzu dan Allah menene abinyi? Ni nafi son kiyi gaggawar dawowa gareni"
Murmushin jin dadi tayi,
"Karka damu hamood ka kwantar da hankalinka very soon zan zama mallakinka"
"Are u sure?"
"Am 100% sure hamood...."
Dariya sukayi atare lokaci guda, sun jima sun bata lokaci sosai suna shan hira domin har wurin karfe 1 nadare suka kai yana sanar da ita abubuwan da suka faffaru saida bacci ya takurawa bilkisu sannan sukayi sallama.
Washe gari da safe bayan ta sallami su mariya sun tafi sake kwanciyarta tayi har saida hamood yakirata sannan tatashi, bayan sun gama waya tashiga wanka tashirya sannan tatafi asibiti amma yau bataje da wuriba kamar jiya shi dai fahad yana kwance ya kosa yaga zuwanta, dauke da basket din abinci ta shiga dakin tasha yaluwar Arabian gown mai manyan stones ajiki tayane kanta da wani mayafi mai kauri milk colour, tunda suka gaisa da ya Abba bata sake furta komai ba, fahad sai kallonta yake taki kulashi wannan dalilinne yasashi niyyar jan magana, shagwabe fuska yayi,
"Baby inata kiranki ban sameki ba, dama zan fada mikine ki taho min da kayana gashi yanzu sai na ya abba nasa saboda dazu ya gyara min jikina..."
Jijjiga kai tayi tana kallon wayarta,
"May be network problem ne"
"To kibani abinci inci saboda zan sha magani"
Dariya Abba yayi yana tattara kayansa zai fita,
"Yaro yasamu sauyin yanayi wato yanzu da kanka ma kake cewa abaka magani kasha ah lallai angaida bilkisu..."
Murmushin yake tayi tatashi ta zuba masa potatoes plan din da ta iyo sannan ta hada masa tea dan kadan, yauma kamar jiya da taimakonta yaci abincin sannan yasha magani, haka tawuni acikin wani hali, hali na rashin walwala domin ita bata ki a sallami fahad ayauba su koma gida inyaso ayita takare, yauma magrib nayi ta tafi gida itada su maryam, lokacin bacci nayi suka sha hirarsu da hamood.
Gaba daya fahad yakasa gane kanta a yan kwanakin nan ada tana sakar masa fuska suyi wasa da dariya wani lokacin har tsokanarta yakeyi amma yanzu tadaina sai shan kunu da daure fuska, ita kuma anata bangaren kawai so take yawarke a sallameshi suje gida ayi wacce za ayi domin hamood yace baya son bikinsu ya dauki dogon lokaci yafiso ayishi kwana kusa, kullum sai sunyi waya dashi fiyeda sau uku wani lokacin ne ma idan tana cikin mutane bata yarda ta dauka. Yau kam tun kafin taje asibitin husna taje duba fahad itada kawayenta domin kullum idan taje shagonsu bata samunshi sai ace baizo ba daga karshe dai su hamza suka fada mata fahad baida lafiya, wahala sosai tayi masa kamar ba student ba domin harda girki da fruits ta siya ta kai masa, suna tafiya bilkisu na zuwa shiyasa basu haduba tadai ga kayan dubiya amma bata san waye yakawo ba.
Satin fahad biyu a asibiti aka sallameshi domin jiki yayi kyau kuma babu laifi ya murmure sosai kamar ba majinyaci ba, tunda suka koma gida ya fuskanci akwai matsala domin bilkisu ta kafa ta tsare, duk da dai batace masa komai ba amma daure fuskar da take tayi ya isa yasanar dashi akwai matsala shi dai baice mata komai ba har dare, yana zaune gaban dressing mirror bayan yafito daga wanka da kayan bacci ajikinshi riga armless da wando iya cinya tashigo dakin, zama tayi gefen gado tana kallonshi so take tayi masa maganar amma bata san ta inda yadace tafara ba dole sai hakura tayi domin ta sake dan bashi lokaci. Bayan kwana biyu tadawo daga aiki yana kwance falo tawuce bedroom yau dai ta daura aniyar sanar dashi inyaso komai ta fanjama fanjam domin hamood ya matsa da son ganin fitowarta, fitowa tasake yi daga cikin bedroom tazo ta zauna tana fuskantarsa,
"Fahad.... Dan Allah inaso zamuyi magana..."
Kai yadaga mata bayan ya tattaro gaba daya hankalinsa gareta,
"So nake ka sawwake min..."
Kallonta yayi cikin rashin fahimta,
"Kamar ya fa...?"
"Ina nufin so nake ka sakeni...."
Tashi zaune yayi babu shiri yana kallonta,
"In sakeki? Laifin me kikayi min da zan sakeki? Anya kuwa kin san abinda kike fada?"
"Nasan abinda nake fada mana, auren ne bana bukatarsa yanzu shiyasa nace ka sawwake min"
Murmushi taga yayi sannan yamike yana mika,
"Allah ya kyauta, ni wallahi da zaki taimaka ma da kin hau kaina kinyi birgima sosai ko zan samu gajiyar dake jikin nan nawa marar dalili ta baje amma nasan bayi zakiyi ba, bari kawai natafi filin ball naje na basar acan...."