← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 67

Sashe 58

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Ganin yayi kan husnah gadan gadan yasa Bilkisu saurin mikewa ta tashi tasha gabanshi, kokarin tureta yayi yana cewa,

"Asma'u baza kiyi min bayanin abinda kukayi ba sai na hau ruwan cikinki?.... Bari na kamaki"

Rikeshi gamm Bilkisu tayi ta kalleshi da idanuwanta wadanda ke jajur, sannan ta kalli husnah,

"Zo ki fice.... Fitar min adaki..."

Sim sim husnah tawuce tana harare harare, duk fahad yana kallonta lallai yarinyar nan munafuka ce wato saima ta nuna ita sam batayi hakaba sharri akayi mata shifa yatsani zama da mutum munafiki wanda baya kaunar zaman lafiya, har husnah tafice Bilkisu na rike dashi, hannuwanshi duka biyu ta kama tasaka cikin nata,

"Kai kuma ai bahaka akeyi ba.... Meyasa zaka kawota gabana har karinka marinta kana neman dukanta akaina....., bazata ji dadiba, gara ka tambayeta kaida ita idanma fadan ne sai kayi mata daga kai sai ita amma idan ka kawota gabana kayi mata fada ai tamkar kayi mata cin fuska ne......"

Kallonta yayi da idanuwanshi wadanda ke cikeda bacin rai shi yasan ba abanza yake kaunar Bilkisu ba, tanada sanyin hali da farar zuciya sam bata da mummunan nufi akan kowa,

"Kiyi hakuri kinji....insha Allah zanyi maganin abun..."

"Na hakura amma gaskiya gida zan tafi.... Gidannan yayi mana kadan mu biyu, matarka bata san ganina haushina takeji, nima kuma haushinta nakeji kaga zama wuri daya bazai yuyu ba... Ni kawai duk ranar da kasamu damar canja min gida sai indawo amma yanzu gida zan tafi...."

Murmushi yayi yajata bakin gado ta zauna shikuma ya tsugunna agabanta yana kallonta,

"Kawai sai kitafi gida kije kice musu kin kasa kishi da yar karamar kanwarki akanta kika dawo gida?"

"Ni ba akanta bane, fitinace bana so.... Kana jin fa abinda suka fada min wai ni yar iskace...."

"Kibar maganar nan pls.... Nidai ai nine na aureki ko? To ban zargeki da hakaba dan haka duk wanda ma zaice kinyi haka kar abin ya dameki tunda ni mijinki ban zargi haka daga gareki ba.......ni nasan atsaftace kike soo don't worry about that...."

Shiru tayi batace komai ba har lokacin idonta bai bar fitar da kwalla ba saboda ba ataba jifanta da wata muguwar magana makamanciyar wannan ba,

"Ina zuwa...." Ganin yamike yasata rikoshi,

"Fahad karfa kace zaka daki yar mutane.... Babu kyau duka...."

"Ni ba dukanta zanyi ba, ina zuwa..."

Dakin husnah yakoma wacce itama sai yanzun takoma bayan tagama jin duk abubuwan da suka fada shida Bilkisu, zama yayi agefen gadonta ita kuma tana tsaye atakure duk atsorace take dashi dan bata taba sanin cewa yanada zuciya har hakaba,

"Husnah abinda kikayi kin kyauta kenan? Meyasa zaki fada mata haka? Kin san zunubin dake cikin wannan maganar kuwa? Ko court fa takaiki za a iya yimiki bulala saboda kazafi kika yimata......."

"Dama ai ita kafi so shiyasa kullum abayanta kake, baka son laifinta...."

"Husnah ba maganar ita nafi so bane... Maganace ta gaskiya.... Bilkisu ba sa'arki bace bai kamata kizo ki rinka fada mata magana irin hakaba..."

"Gaskiya ya fahad wallahi kaima tagama dakai inbanda haka ya daga fada maka magana zaka hau kai ka zauna batare da kayi bincike ba? Ni kasan abinda ta fada min?"

Mikewa yayi cikin fushi,

"Karya kikeyi babu abinda ta fada miki.... Kin san wani abu husnah? Wallahi zan yi mugun bata miki rai akan wannan maganar, matsawar kina son mu shirya to yazama wajibi ki iya bakinki bana son rashin kunya kuma bazan taba lamunta ki raina min mataba saboda ai ko bata girmeki ahaifeba ta rigaki zuwa gidan nan anan kika tarar da ita, ita bata takura miki ta hanaki kwanciyar hankali ba sai kece zaki takura mata? Da lokacin da zan auroki ta tada fitina tanuna bata yarda ba kina tunanin zan aureki ne?, wallahi tun wuri ki shiga hankalinki......"

"Amma dai ya fahad ai....."

"Will you shut up ko sai na bigeki.... Ban san bakida kunyaba ai sai yau... Mun kusa fara fada dake asma'u"

Mikewa yayi cikeda fushi sai kuma taga yakoma ya zauna hannunshi kan kirjinshi, babu shiri yazame ya kwanta kan gadon kafafuwanshi akasa hannunshi dafe da chest dinshi, lumshe idanuwa yayi yana jin bugun zuciyarshi yana fita ahankali ba normal ba, tsugunnawa husna tayi gabanshi ta dafa shi,

"Sannu ya fahad.... Dan Allah kayi hakuri.... Yau kasha maganinka?"

Kai ya daga mata hakan yasata sake matsawa kusa dashi,

"Ka kara wani pls..."

"Nabarshi a kaduna..."

"A'a akwai wani anan... In dauko maka?"

"Kar yazama over dose husnah kinga dazu nasha wani..."

"No bazai zamaba, dan Allah kasha magani"

Tashi tayi ta dauko masa harda ruwa yasha yasake kwanciya babu jimawa bacci yayi gaba dashi, ita wallahi tana son fahad har cikin ranta amma ta tsani bilkisun nan bata kaunarta ko kadan gashi shikuma taga kamar yafi sonta. Bilkisu na dakinta bata sanma abinda ke faruwa ba tadai ga shiru bai dawoba, tunani tayi abinda fahad fa yafada gaskiyane idan taje gida me zata cewa su ammah? Tunda ita dai bada fahad sukayi fada ba tasan su abba bazasu barta ta zauna ba ai jarabar iyallo ma kadai ta isheta tunda kullum tana hanyar zuwa gidan dan bata cikakken sati biyu bata zoba, tashi tayi ta maida kayanta ta ajiye ta hada tea din da tun rana tayi niyyar sha amma yaran nan suka bata mata budget, yau kwata kwata babu abinda tasaka acikinta tun safe, zama tayi tasha tea din sannan tashiga wanka. Abangaren fahad kam yana can yanata bacci dan ko sallar ishah baiyiba har yanzu yanata bacci har 11 sannan yatashi husnah na zaune kasa ta kifa kanta saman gado itama anan baccin yayi gaba da ita, tashi yayi duk jikinsa babu kwari,tashin husnah yayi tana tashi ta tsaya tana kallonsa,

"Tashi ki hau kan gado ki kwanta..."

Tashi tayi tahau kan gadon shikuma yamike saboda baiyi sallar ishah ba gashi ma yunwa yakeji,

"Kinyi sallah?"

Daga masa kai tayi hakan yasashi fita daga cikin dakin yana zaro wayarshi daga aljihunsa, dakin Bilkisu yashiga ga mamakinsa idonta biyu tadai yi shirin bacci da laptop kusa da ita tana rikeda cup din tea,kunnenta ta makala earpiece tana sauraron kundin tarihi na Malam Aminu Ibrahim daurawa, daga kai tayi ta kalleshi dama dogoyen kayane jikinsa riga da wando na wa gambari kalar ruwan toka,zama yayi gefenta ya zare earpiece din guda daya yasa a kunnenshi,

"Me kikeji?.... Kekuma kina son wannan malamin naga alama...."

"Yana fadar abubuwa masu amfanine sosai shiyasa...."

"Hakane.... Bacci fa nayi sai yanzu natashi saboda dazun nan bana jin dadine"

"Sorry..."

"Gashi yunwa nakeji.... Kinada abinci?"

"Ni banyi girkiba.... Zakasha tea?"

"Sai insha din ya na iya...."

Tashi tayi tasauka daga kan gadon tatafi zuwa wurin wani dan karamin show glass wanda kayan tea dinta ke ciki tun lokacin da suka hada kitchen da falo da husna ta kwashe kayan tea dinta tadawo dasu cikin daki,shikam fahad tunda tace masa yau batayi girkiba yasan abin yazo domin har yaganeta idan tana period wuni zatayi shan tea, tea ta hado masa lafiyayye harda bread ta kawo masa yana zaune yana kallonta, rigar baccinta bamai nauyi bace kuma ba mai shara shara bace iyakarta gwiwarta da hular bacci akanta, karbar tea din yayi yace,

"Thanks..."

Daga haka yafara sha ita kuma ta koma saman gado taci gaba da aikinta har yagama yawuce bathroom dinta yayi alwala yafito, rug din sallarta ya dauka ya dan kalleta,

"Zo muyi sallar ishah naga kema kamar bakiyi ba...."

Tasan halin nasa zai fara shiyasa tace masa,

"Ni ai tawa tariga taka zuwa..."

"Seriously?" Yafada yana murmushi, batayi magana ba tadai jijjiga kai hakan yasashi shimfida abin sallar yayi, kafin ya idar har ta kashe system din da wayarta ta kwanta, sallama yayi mata yafita bayan ya idar saboda adakin husnah yake kasancewar wancan zuwan adakin bilkisu yabar gari. Washe gari da safe husnah agaba tasashi tana bashi hakuri amma yace shi bashi zata bawa hakuri ba Bilkisu yake so taje tabawa hakuri, tashi tayi tafita nan yayi hanzarin bin bayanta saboda gudun samun matsala, Bilkisu na gaban drewar tana fito da kayan da zata saka daga ita sai daurin kirji dayake daga wanka tafito,bude kofa husnah tayi tashiga,

"Anty kiyi hakuri akan abinda yafaru..."

Juyowa Bilkisu tayi tai mata wani kallo sannan tace,

"Pls walk out from my room... I said get out..." Daidai lokacin fahad yashigo,

"Kiyi hakuri..." Inji husnah,

"Yawuce but kifitar min adaki pls..."

Juyawa husnah tayi tafita shikuma fahad yamaida kofar yakaraso ciki, karasa fitar da kayan da zatayi tajuyo ta kalleshi,

"Kai kuma fa? Me kake bukata?"

Girgiza kai yayi, "nothing"

"Ok bani wuri inshirya to..."

Kada kai yayi yafita, shifa yagane Bilkisu son girmanta ajininta yake wallahi, afalo yazauna ya kwanta yana danna wayarshi dan yaji motsin husnah acikin kitchen tana aiki, yana nan kwance Bilkisu tafito cikin shirinta na fita aiki, yau komai nata brown tasaka, kallonta yayi cikeda sha'awa,

"Kinyi kyau..."

Jin motsin husnah a kitchen yasata cewa,

"Thank u my dear..."

"Adawo lafiya but kamar bakiyi breakfast ba..."

"Bana jin yunwa karka damu, idan naje office zan karasa gida"
Chapter 58 · 0% Book details