← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 67

Sashe 18

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zaman shiru taci gaba dayi sai dai idan ankirata awaya ta daga amma tana jiyo hirar mutane awaje group group. Wurin sha daya da wani abu tafara jiyo guda sosai da karfi aifa nan mata aka kifa kwarya ana kida mai dadi wasu kuma na rera wakar aure,

Wasa wasa gudar nan har cikin dakin da take ta cikin mayafin ta samu nasarar hangoshi sanye da babbar riga da hula, har inda take yatako yazo ya dagata, tsakar gida suka fita inda ake yin wannan kidan, daya bayan daya ake zuwa ana zuba musu kudi shi sai asaka masa acikin aljihunshi ita kuma cikin jakarta, sunfi minti talatin tsaye ana zuwa zuba musu kudin nan ita har tagama kosawa da wannan tsaiwar danma jingine take jikinsa amma babu wanda zai gane, saida kaf dangi na uwa da na uba suka gama zuba musu kudin sannan aka maida ita daki, shi kam ficewa yayi bata kara jin alamunshi ba har azahar lokacin ne kuma aka maida ita dakinshi dake can soro wai tayi salla taci abinci, kamar kuwa sun san tana da bukatar komawa dakin domin amatse take da ta canja pad din jikinta dan ita atabar pad tadade ajikinta to tayi awa uku,neat tasamu dakin anshare angyarashi an fitar da kwanukan abincin daren jiya ankunna turaren wuta na tsinke.

Bayan su anty juwairiyya da suka rakota sun fita wanka tashiga tayishi sauri sauri tafito dan kar wani yashigo ai kuwa tana fitowa tana kokarin manna pad jikin pant dinta yashigo, danma lullube take da mayafi, bai kalleta ba yawuce gaban akwatinshi sannan ya janyo kayanshi dake rataye jikin kofa yasaka cikin akwatin, kasa saka pant din tayi agabanshi sai bathroom tawuce tasaka sannan tafito lokacin yana rufe akwatin,

"Ranki yadade kiyi sauri ki shirya yanzu za akawo miki abinci...."

Bai karasa rufe bakinsa ba yaji knocking abakin kofa, tashi yayi daga gaban akwatin,

"Inajin ma gashi nan ankawo... Bari mugani"

Kofar yabude yafita ai kuwa su mariyane dauke da kwanukan abinci, karbowa yayi yashigo dashi lokacin tana saka bangles, ajiye mata yayi yajuya ya dauko wasu kayanshi dake kan drewar din dakin,

"To hajjaju nabarki lafiya, sai mun hadu a sabon gida..."

Zama tayi tana kallonshi,

"Ban ganeba, wai kana nufin ni kadai zan zauna adakin nan shiru har lokacin da za araka ni gidanka?"

Murmushi yayi,

"Ehh mana, kodai kinfi son nazauna mu zauna tare? Kibari zan turo miki su Mariya suzo su tayaki zama"

Daga haka yadauki kayanshi har katuwar akwatin yafice, bai jima da fita ba sai gasu mariya sunzo ai kuwa tasha hira domin yaran sunada surutu shiyasa taji dadin zama dasu inbanda labarin gidan da na makaranta ba abinda suke bata. Har la'asar tana tare da yaran amma mutane na dan shigowa musamman baki masu tafiya suna yimata sallama da fatan alkhairi shiyasa zuwa karfe biyar na yamma gidan tsit sai mutane kadan na kusa amma bakin nesa kam duk sun tafi, bayan sallar magrib su anty Fauzy suka zo suka shigar da ita cikin gida lokacin ma baba yadawo har turakarsa suka kaita ta gaidashi sannan aka maida ita dakin ayiyah, ayiyah kam sai nan nan take da suruka matar auta guda komai tagani ta tura mata gabanta da haka har motar daukarta tazo, anty Fauzy da anty Kubra ne zasu rakata, daki daki aka bi da ita tayiwa kowa sallama sannan aka fita da ita bayan anfitar da kayanta,Baffa ne yayan salim a motarshi shi yadaukesu yakaisu wanda tafiyar bata da wani tazara sosai can, koda sukaje su basu wani jimaba suka yimata sallama suka fita, hamdala tayi acikin zuciyarta ta bude fuskarta tana bin dakinta da kallo wanda yasha kayan alatu domin gadonta kadai abin kallone gashi dakin babu laifi da girmanshi saboda ya cinye komai dan iya mirror dinta kadai duniyane wurin da ya lashe ba dan kadan bane cire mayafin tayi ta fita falo wanda shima ba laifi ga dining area taciki ga kitchen nan ga store cikeda kayan abinci domin komai biyar biyar abba yayi mata kama tun daga kan shinkafa, taliya, macaroni, indomie, crate din kwai,semovita manja, man gyada komai biyar,

Ba karya gidan fahad yayi domin yarone mai zuciya shi dai barshi da kwalisa da iyayi amma yanada zuciyar neman na kanshi duk da baiyi karatu mai zurfi ba domin iyakacinshi diploma kawai sai sana'ar dinki da yasaka agaba kuma yayi sa'a sana'ar ta karbeshi, iyakar gata tasan iyayenta sun nuna mata domin komai mai kyau da tsada aka yimata ita kanta gidan ya burgeta dan dagwas dashi shi ba kato can ba kuma shi ba karami can ba abinta dai dai misali, tsakar gidan dan madaidaicine yasha interlocks harda flowers shuke sai pop shikenan sai kofar falo ma'ana dai safe content ne komai aciki, abu dayane yabata takaici bedroom guda daya zasuyi shearing tunda ga dayannan ba agama ba asalima data buda ko fulasta ba ayiba sai uban tarkacen kayan aikin gidan da aka zuba aciki aka rufe, alhalin gado guda biyu abba yasai mata kamar sauran yan uwanta gashi karshenta sai dai komawa akayi dashi gida......

*kamar da wasa na kudine idan har kin san baki biyaba dan girman Allah karki karanta.*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*

*KAMAR DA WASA...!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*19*

Cikin bedroom dinta takoma ta zage tashiga toilet tayi wanka tafito ta zauna tayi shirin bacci cikin wani night wear milk colour riga da wando,wandon iyakarshi cinya sai rigar da bata wuce cinyaba itama, handbag dinta ta janyo ta debo wayoyinta gaba daya ta kashe sannan ta rufe jakar da kamar ta zauna zaman kirga kudaden dake ciki wadanda aka zuzzuba mata tabari sai zuwa gobe ta kirga domin bacci kawai take ji, kashe wutar dakin tayi tai kwanciyarta bayan ta lulluba domin bata iya kwanciya da kaya ba ajikinta tasan babu mamaki cikin dare idan zafi ya dameta ta fige rigar ma gaba daya. Misalin karfe 10 saura fahad yashigo gidan tareda tawagar abokanshi wadanda suka iyo masa rakiya, key dinshi yadauko yabude gidan yashiga yana jin wani farin ciki na ratsashi, har falo suka shiga danma baiyi garajen kaisu dakiba kamar yasani yace kawai su tafi yasan yanzu tayi bacci amma sukace karyane kawai dai yana yimusu kora da haline, bedroom yawuce yana shiga ya kunna fitila awayarshi ya haska ya kunna wuta, bude ido daya tayi ta kalleshi jikinta lullube da duvet hular kanta ta cire saboda santsi,kitson ya zubawa ido kamar yasamu tv

"Yadai....?" Ta fada tana yamutsa fuska domin ba kadanba sosai tafara jin dadin baccin da ya katse mata ta hanyar kunna wuta itafa duk dadin barci da nisan da yayi matsawar zaka kunna wuta to sai ta tashi,

"Ah babu komai..."

Daga haka yakashe wutar yafita,

"Ai nafada muku dama tayi bacci, yanzu gashinan haka kawai kunsa na tashi baiwar Allah..."

"Dakyau mijin yar gata... Wato ma idan tana bacci ba atashinta" inji hamza na shagonsu, shi dai alla alla yake su tafi domin shima yana son ya kwanta ya huta, ai kuwa sun wahalar dashi kafin su tafi daga karshe daya bayan daya yarinka turasu sannan yamaida kofar gidan yarufe yadawo ciki itama kofar falon yarufe yashiga dakin, wannan karon bai kunna wuta ba kawai da fitilar wayarshi yayi amfani yashiga bathroom bayan yadauki kayan baccinshi, wanka yayi,yana cikin wankan yalura da pad din data jefar cikin dustbin duk da haka bai hakuraba saida ya dauki dustbin din yayi masa kallon kurulla daga karshe dai yagane menene, baki yatabe yasaka rigar baccinshi armless da wandonta duk jajaye, yana rike da kayan da yacire, drewar yabude ya watsa kayan sannan yafita falo dan bazai iya bacciba sai yaci wani abu, balangun da yazo dashi yabude kulli daya yaci yakoshi sannan yasha yoghurt guda daya sauran yasa cikin fridge, dakin yakoma yaje kan gadon yana shirin kwanciya yaji tace,

"Malam yadai?"

"Kamar ya? Kwanciya zanyi mana"

"Bana skwatin, ban iya kwana mutum biyu agado daya ba..."

Da mamaki yake kallonta duk da ba ganinta yakeba tunda dakin akwai duhu,

"Amma dai ai kema kin san gadon nan yayi miki girma ke kadai...."

"Dagaske fa nakeyi, dan naga kamar kai kadauki abin dawasa..., ga spare mattress nan kadauka sannan kaduba cikin drewar akwai sabbin bedsheets da blankets idan kana da bukata...and lastly ka kashe wannan hasken domin bana bacci da haske akaina" Daga haka tamaida kanta ta gyara kwanciyarta, fasa kwanciyar yayi ya nufi drewar yabude yadauki duk abinda zai bukata yana kunkuni, pillow yazo yadauka guda daya yayi hanyar falo yana cigaba da kunkuninsa,

"Amma bar miki dakin gaba daya kije ki cinye..... Nima bana bacci aduhu.....haka kawai dan takura zaki wanice ke kadai zaki kwanta akan gado...."

Katifar yadawo yadauka yaje yayi shimfidarshi afalo sannan yasake dawowa dakin, wannan karon wuta ya kunna dan neman magana,

"Me kuma yafaru?"

Tafada tana bude ido dakyar dan bacci,

"Sucket nake nema zan saka charge"

"Acan inda zaka kwanta din babune? Pls malam kashe min wuta bacci zanyi..."

"Ehhh ai dai kin tashi...."

Yafada cikin kunkuni yanda bazata jiba, wutar yakashe yafita yana ja mata kofa dama babu wani charge da zai saka kawai son yatasheta ne yasashi kunna wuta, akusada doguwar kujera ya shimfida katifar tasa ya kwanta yadora kafarsa daya akan kujerar yakunna data awannan daren yashiga instagram daga can yafita yakoma Facebook, bashi ya hakura ba sai wurin daya da rabi a lokacin yaji bacci yaci karfinshi, ajiye wayar yayi bayan yakashe yayi addu'a babu jimawa sai bacci. Daf da asubah yatashi saboda fitsarin da ya takurashi kusan ma shine yatasheshi, bedroom yashiga mutuniyar tasa tana tukunkune sanyin asubah da na fanka na kadata duk ta takure wuri daya, fankar yarage mata sannan yashiga bathroom din yayi abinda zaiyi yafito yakoma falo yayi kwanciyarshi bai kara motsawa ba sai karfe bakwai saura, yana bude ido yakalli agogo gani yayi sun zabga makara gashi ko salla baiyi ba, bedroom din yanufa kansa tsaye yakama handle yabude tana zaune kan gadon ta ziro kafafunta kasa tana daure kitsonta da tacire ribom din cikin dare batare da ta saniba dan hatta rigarma sai yanzu ta mayar, babu zato taganshi yashigo cikin azama ta yayibi duvet tarufe jikinta tana kallonshi,

"Meye haka? Ya zaka shigo min daki batare da taking excuse ba....."
Chapter 18 · 0% Book details