← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 67

Sashe 30

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Bari infada miki fa kibar ganin ina kyaleki bafa tsoronki nakeyi ba kawai ina rabuwa dake ne saboda ina respecting dinki ko kina tunanin idan karamar yarinya nake aure age mate dina ko wadda na girma the same way zanyi treating dinta kamar yadda zanyi treating naki? amma wallahi idan kika kaini bango zaki fahimci bakida wayo zaki gane shayi ruwane, tunda kika zo gidan nan abinda kika gadama shi kikeyi ban taba takura miki ba to nima baki isa kin takura min ba, saki ne kuma baza ayiba idan kina iyawa ki saki kanki mana, haba kin takura min dayawa alhalin nikuma bahaka nake yimiki ba daidai da hakkina wannan ba taba bani akayi ba saboda Kin rainani amma ban taba takura miki akan hakanba bayan kuma inada karfin da zan kwata da karfin tsiya..."

Zaro idanuwa tayi tana hawaye cikeda masifa da jin haushinsa tace,

"Dama abinda ke ranka kenan so kake kayi min fyade to kazo kayi idan baka da imani..."

"Zaki gane banida imani sai ranar da na daureki nayi kaca kaca dake nayi round biyar akanki ranar ne zaki san banida imanin...."

Daga haka yawuce cikin bedroom yabarta anan tana sharbar kuka amma hankalinta yayi mugun tashi da jin kalamansa na karshe gaskiya idan fahad yayi mata haka ya cuceta idan ya rabata da martabarta bazata taba yafe masa ba kai wallahi muddin yanemi aikata mata abinda yafada saita raunata shi, zama tayi awurin taci gaba da risgar kuka har tsawon wani lokaci. Shikuwa fahad lokacin da yashiga daki dariya ma dramar su tabashi wato bilkisun nan shegen tsorone da ita sai son girman tsiya domin ya hango tsoronshi karara acikin idanuwanta da dukkan fuskarta gaba daya. Wanka yashiga yayi yafito yunwa na ciciyarshi domin bai wani ci isasshen abinci ba, daga shi sai gajeren wando da farar vest yafita yana janye singiletin zuwa saman kirjinsa sai shasshafa cikinsa yake yi,tana zaune inda yabarta bai ko kalleta ba yawuce dining kamar yadda ya tsammata batayi girki ba sai dafaffen shayin na'a na'a cikin tea flask wanda yanzu shi tamayar abincinta, babu yadda ya iya shi dinma tea din yasha ya dauki slice bread yashafa butter ajiki yaci yana tasowa ta mike tsaye duk da atsorace take dashi amma haka tayi karfin halin yimasa magana,

"Kabani wayata tun muna shaida juna...."

Banza yayi da ita yanufi bedroom,

"Wallahi ko kanaso ko baka so sai ka...."

Juyowa yayi yadawo da baya tana ganin haka ta dora hannu akai tafasa ihu saboda duk atunaninta abinda yafada dazu zai aikata, tsayawa yayi gabanta ya zuba mata ido,nan taja baya cikin sauri,

"Daina gudu karki damu yanzu babu abinda zanyi miki amma duk ranar da nahau kanki wallahi sai kin gane bakida wayo ai nafada miki sai nayi round 5, idan banda rashin tunani irin naki ya za ayi kinada aure ki zauna kina sauraron tatsoniyar wani jahili awaje? Me hakan yake nufi? To wallahi this is the last warning babu ke babu shi, ban son dakikanci da shashanci..."

Idonta fall hawaye muryarta adashe ta kalleshi,

"Fahad ni kake fadawa haka? Ni kake addressing da dakikiya jahila shashasha?"

Sauke idanuwansa kasa yayi sannan cikin sanyin murya yafurta,

"Am very sorry...."

Daga haka yajuya yashiga daki ya kwanta amma baya jin zai iya bacci adaren yau kamar yadda itama bilkisu baccin ya gagareta, inbanda sakawa da kwancewa babu abinda yakeyi har dare ya tsala. Kwana biyu haka nafaruwa har lokacin bai bata wayarta ba kuma bai sanarwa da kowa ba wani lokacin sai yaji kamar yafadawa koda wani daga cikin yayunshi ne amma sai wata zuciyar ta haneshi, gaba daya bilkisu ta hana kanta sukuni danma tana dan shakkarsa yanzu bata son yayi abinda yayita ikirarin zaiyi akanta, yau da safe yana daki kwance yamike yafito falo kwance ya sameta wayarta ya mika mata,

"Bilkisu ga wayarki.... Shi masoyi akoda yaushe yana kokarin ganin yayi abinda masoyinsa zai kasance cikin farin ciki koda kuwa shi din zai dawwama acikin bakin ciki, kamar yadda kika nema kije na sakeki saki daya...."

Cikeda farin ciki ta mike,batace komaiba tawuce bedroom taje tafara hada kayanta, duk abinda zata nema tazuba cikin babban akwati nan ta janyoshi tafito tana rikeda handbag dinta da akwatin,

"Ga akwatinan lefenka can harda sadakinka duk yana ciki..."

"Nabar miki saboda banyi miki dan nakwace ba..."

Bata sake cewa komai ba tasaka kai tafice daga cikin falon, wasu hawaye ne masu dumi suka zubo daga idanuwansa......

*Yar uwa littafinnan na siyarwa ne idan kina so ki biya saiki karanta*

*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*

*KAMAR DA WASA....!*

_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*

*28*

***Runtse idanuwansa yayi yana jin wani irin kunci acikin zuciyarsa, hawaye yayita yi awurin har saida yaji kansa yasoma sara masa sannan yasamu yatashi yana share fuskarsa da handkerchief din dake cikin aljihunsa, wayarsa kawai ya dauka sai keys dinshi yafita daga gidan dan baya jin zai iya sake awa daya acikin gidan tunda wacce yake zaune saboda ita bata nan, Babur dinshi yabuga yabar gidan bayan ya rufe ko ina, kai tsaye gidansu salim ya wuce yabude dakin salim din yashiga ya kwanta yana jin kansa na cigaba da sassara masa saboda kukan da yayi domin rabon da yayi kuka irin wannan har ya manta. Yana kwance yarasa meke yimasa dadi har salim yashigo ganin idanuwansa arufe yasashi zaton fahad din kila bacci yakeyi wannan dalilinne yasashi ficewa batare da yayi masa magana ba.

Har wurin 12 na rana fahad na kwance dakin salim saida yaji dan dama dama sannan yatashi yatafi gidansu, bai shiga cikin gidanba yabude dakinsu nada shida Abba yashiga yasake kwanciya babu wanda yasan yashigo gidan domin ko babur dinshi bai ajiye wurinda za aganiba, sai lokacin yasamu damar yin kukan bakin ciki nan yarinka yi kamar karamin yaro babu jimawa yafara jin zazzabi zazzabi ajikinsa amma dai yadaure bai tashiba har azahar tayi, anan daki yayi sallah dama wayarshi akashe take saboda bama yason wani ya kirashi, salim ne yabiyoshi gidan bayan yakoma dakinsa yaga baya nan sannan har gidansa yaje amma gidan akulle ga kuma wayarshi akashe. Yana kwance duk jikinsa nayi masa ciwo salim yashigo ganinsa kwance alamun ba kalauba yasa salim fara tambayarsa amma fur fahad yaki magana sai ko ido da yake bin salim dashi,ganin yaki magana yasa salim shiga cikin gida wurinsu ayiyah domin karbo musu abinci, ayiyah na tsame alalan da ta dafa cikin cooler ita kuma mamuh na dama kunun gyada suna aikinsu suna hirarsu, koda salim yafada musu abinci yazo karbar musu shida fahad wanda ke dakin abba basu kawo komai ba suka zuba musu yakoma wurin fahad, dakyar da fada da komai fahad yatashi suka ci alalan domin kwaya daya ma yaci sai dan kunun da ya kurba yakoma ya kwanta,juyin duniya salim yayi akan fahad yasanar dashi abinda ke damunsa amma yaki daga karshe salim yatashi yafita. Tunda salim yatafi fahad ke kwance ya rufe kofar dakin shiyasa babu wanda zai tsammaci cewar da akwai mutum aciki,ahaka yakwana yawuni har dare yayi sai dai idan lokacin sallah yayi yatashi yayi yakoma ya kwanta,har dare atakaice dai acikin wannan halin fahad ya kwana agidan babu Wanda yasani har saida safiya tayi lokacin da baba zai fita yazo saitin kofar dakin yajiyo fahad yana yin tari cikin mawuyacin hali, buga kofar baba yashiga yi wanda har karar bugun ta janyo hankalinsu ayiyah suka fito domin ganin meke faruwa, cikin mawuyacin hali yataso yazo ya bude kofar yana jin kamar zai fadi saboda rashin karfin da jikinsa ke fama dashi,wuri yasamu yazauna ya jingina da bango yana kallon su baba dake kokarin shigowa cikin dakin,

"Muhammadu... Ya akayi? Tun yaushe ka shigo cikin dakin nan?" Baba yafara tambayarsa cikin mamaki,

"Tun jiya ne baba..."

"Ikon Allah, to ya zakazo kashiga daki karufe kanka kai daya, ina matar taka?" Mamuh tafada cikeda mamaki,

"Na saketa...."

Ai gaba dayansu jin maganar tasa sukayi tamkar saukar aradu acikin kunnuwansu.

"Saki.....?"

Su ayiyah suka fada cikin razani har bakinsu na haduwa wurin tambayarsa,

"Muhammadu meyasa kayi haka? Meyasa ka yanke hukunci da kanka batare da ka tuntubemu ba?" Baba yafada cikin kwantar da murya,

"Baba kuyi hakuri dan Allah....."

Dukansu samun wuri sukayi suka zauna cikeda jimami, sunfi mintuna goma ahaka babu wanda ya iya yin magana zuwa can baba yaja gwauron numfashi cikeda damuwa yace,

"Fahad meyasa ka saki yarinyar nan yar mutunci yar gidan mutunci? Laifin me tayi maka haka...?"

Kasancewar dan jiri na daukarshi yasashi zamewa ya kwanta idanuwanshi taf da hawaye,

"Baba ni bata yimin laifin komai ba..... Kawai..... Kawai dai.... Kawai bazan cigaba da zama da ita bane...."

"Me? Fahad acikin hankalinka kake kuwa? Wannan wanne irin shashanci ne? Ina kataba ganin anyi haka? Kowa da yake zaune da abokin zamansa ba hakuri yakeyi ba?" Mamuh tafada cikin fada,

"A'ah yimasa ahankali.... Ai ba tatashi zamu biyaba, ni yanzu haka ta gidansu yarinyar zanbi inbaiwa mahaifinta hakuri sannan innemi bikonta adawo da ita dakinta tun abu baiyi nisa ba.... Saki nawa kayi mata?" Baba yakarashe maganar yana kallon fahad wanda idanuwanshi ke rufe,

"Baba babu aure atsakaninmu fa yanzu saboda saki.... Saki ukun...."

Ai tun kafin yarufe bakinsa su ayiyah suka rufeshi da fada ta inda suke shiga ba tanan suke fitaba shi baba sai shiru ma yayi yana saurarensu daga karshe ayiyah tatashi tafita cikin fushi, saida itama mamuh tafita sannan baba yadora da nasa fadan amma shi nasa cike yakeda nasiha, sun jima baba yana yimasa fada sannan yatashi yafita bayan yasanar dashi cewa gobe zaije gidansu bilkisu su gana da mahaifinta, agaba baba yasashi suka shiga cikin gida har dakin ayiyah yakaishi sannan yafita shikuma fahad ya kwanta nan saman daddumar dake shimfide a falon, sam ayiyah bata saurareshi ba bare ta kulashi sai can wurin azahar sannan tashigo wurinsa dauke da kwanon kunu wanda ta dama masa domin ta fahimci baici komai ba kuma yana tare da yunwa domin gashi nan duk yafige ya fita kamanninsa, yako ji dadin kunun nan domin da zafinsa haka ya zauna yasha da yawa sannan yakoma ya kwanta yana jin irin sarawar da kansa keyi masa.
Chapter 30 · 0% Book details