← Book details Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 2 OF 67

Sashe 2

Kamar Da Wasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Labour kema fa da laifinki gaskiya, why not bazaki baiwa hamood dinki damar yafito kuyi aureba tunda kuna son juna? Haba dan Allah, shekara da shekaru kuna abu daya sai kace wasu wannan..., ai yakamata yanzu ace yabaro kasar Chinan nan yadawo kunyi aure inyaso sai ku koma tare idan bai gaji da zaman canba"

Saida ta sake bata fuska sannan ta kalli khulsum,

"Zanyi miki rashin mutunci idan kika kara kirana da labour dinnan, nafada miki bana so"

"Atoh kiyi min mana wayasa lokacin da kina secondary school din da aka baki labour prefect din kika karba? Ai da sai kice bakya so abaiwa wata"

Dariya tayi ta dauke kanta daga kallon khulsum,

"Kin san me kawata? Hamood shima burinsa yanzu kawai yaga yadawo Nigeria munyi aure, kuma nanda 3 months fa zai dawo, sai dai shi yafi son yayi komai na aurensa dakanshi, baya son uncle dinsa yayi masa acewarsa lokaci yayi da yakamata uncle barewa yahuta tunda tun yana dan 7 years yake yimasa wahala sannan dukkan karatunshi da wanda yayi a Nigeria da wanda yayi a outside duk shine yake sponsoring shiyasa yace sai yadawo yasamu aiki tayadda zai iya yiwa kanshi aure sannan zai kai maganar gaban uncle dinshi"

Dan karamin tsaki khulsum taja,

"To kuma sai me dan yafadawa uncle dinshi yanzu? Minister nefa, ai yanada kudin da zaiyiwa samari goma irinsa aure"

"Hakane khulsum amma kigane wani abu guda daya, abunfa da kunya kuma da nauyi ace tun kana dan karami mutum ke dawainiya dakai sannan ka girma nanma kace komai shi zaiyi maka alhalin bashi ya haifeka ba kawai zumunci ne"

"Ehh to hakane kuma da wannan dan wannan, to Allah dai yadawo dashi lafiya musha biki"

"Amin, yanzu dai tunda magrib takusa ni ina ganin mubari zuwa gobe sai mu shiga central market mu siyo kayan da zamu saka abikin dan gaskiya basaka ankon nan nasu zamuyi ba tunda nasune suda friends dinsu"

"To shikenan babu damuwa Allah yakaimu, Allah kuma yasa mutashi da wuri daga aikin nan"

"Amin,Kuma wallahi commitment dina yawa gareshi goben nan dan har dinki nake son kaiwa ga sauran siyayyar yaran nan da ban karasa ba ta kayan kitchen dinsu"

"Babu komai dai kawai Allah yanuna mana goben komai mai saukine"

"Amin ya Allah"

Daidai lokacin suka tare wani mai keke napep suka shiga domin tafiya gida.

*_Ummi Shatu_*
[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © _*HASKE WRITERS ASSO*_ _(Home of expert & perfect writers)_

*KAMAR DA WASA...!*

*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*

*2*

***Har suka kusa zuwa gida magana daya suketa yi shine maganar zuwan kakarsu iyallo,

"Mai gado Allah kina bani dariya yau dinnan" khulsum tafada tana tuntsurewa da dariya,

Harararta Bilkisu tayi daidai lokacin da suka isa kofar gidansu bilkisun yayinda gidansu khulsum ke can wata unguwa daban gaba da ta su Bilkisu,

"Banida lokacinki sai anjima saura kuma gobe karki fito da wuri"

Daga haka tafice daga keke napep din tabar khulsum na yimata dariya, ji tayi kamar kada ta shiga gidan sakamakon ganin motar ya mudan da tayi, sam ita ta tsani takura da naci amma babu yadda ta iya dole tashiga tana tafiya sadaf sadaf, atsakar gida ta hangoshi zaune kan farar kujerar roba yadora daya kan daya yayinda ammah ke cikin kitchen suna yar hira dashi,

"Sannu da aiki ammah..."

Daga haka tanemi wucewa dakinta, maganar amma ce ta dakatar da ita,

"Ke mai gado, bakiga yayanki bane zaki wuce baku ko gaisa ba?"

Juyowa tayi tadawo da baya, fuskarta babu fara'a,

"Yaya mudan ina wuni? Anzo lafiya? Yasu iyallo?"

Ta hada gaisuwar gaba daya lokaci guda, murmushi yayi ya amsa mata yana yi mata wani kallo mai cikeda sha'awa,

"Lafiya lau mai gadon zinare, ya aikinku?"

Tana tafiya take amsa masa da "lafiya"

"Manyan yan jarida kenan, ku da anganku anga labarai"

Bata amsa masa ba ta soma cuku cukun zaro key din dakinta daga cikin handbag dinta adaidai lokacin taji sallamar Hindu da minah har da mamaa wacce ke rikeda hannun yarta hudah yar kimanin shekara daya da rabi, yarinyar na hango Bilkisu ta kwace daga hannun mamaa tatafi da gudu wurin Bilkisu, dakatawa tayi daga bude kofar da takeyi ta dauketa fuskarta dauke da fara'a,

"Hudah na oyoyo daga ina haka?"

Kafin hudah tayi gwarancinta su mamaa suka karaso,

"Adda maigado yau baki taso da wuriba" inji mama,

"Wallahi fa mamaa aikinne sai ahankali, daga ina kuke?"

"Bakin kasuwa mukaje suka kai nadin gwaggwaro"

Murmushi tayi tawuce dakinta tana cewa,

"Amaren kamshi kenan"

Akan gadonta ta ajiye hudah ta kunna mata cartoon awayarta ta bata sannan ta zage ta fada wanka, tana wankanne meenah ta shigo sadaf sadaf ta dora mata wata farar takarda akan sallayarta tafice.

Bayan tafito doguwar riga kawai ta saka marar nauyi ta dauki hijabinta domin tanata jiyo kiraye kirayen salla daga masallatai daban daban, hudah kuwa tana zaune tana kallon cartoon dinta sai dariya takeyi,

Kan sallaya tahau har zata fara sallar idonta yakai kan farar takardar da meenah ta ajiye dauka tayi ta warware ta tafara karantawa,

_Adda labour yaya mama ce tace wai baza abamu komai bane na hadin amare? Wai kibada kudi zata siyo mana kaza ta dafa mana_

Murmushi tayi ta yaga takardar ta watsa ta cikin dustbin, dama kusan duk lokacin da zasu tambayeta abu indai na kunya ne sai dai su rubuta mata sai su ajiye mata wurin da zata gani ko su tura mata text, ko pad zasu tambayeta sai dai su rubuta mata shiyasa kafin lokacin ma yayi take siyo musu ko tabasu kudin su siya domin tana mutukar kaunar kannen nata saboda suma suna sonta sannan suna bata girmanta tsakaninsu babu reni hatta mamaa da tayi aure harda baby bata yimata reni bare rashin kunya, sallar magrib tayi bayan ta idar ta kara da nafila, tana kokarin shafa addu'a mamaa ta shigo,

"Yarinyar momy kallo takeyi awayar momy?"

Mamaan tafada lokacin da take zama agefen gadon Bilkisu,

"Ai kin jita shiru, nawane zai isheku dafa kazar?"

"Adda labour yafi dubu biyu zuwa uku?"

"To shikenan zan baki kafin ki tafi, shekaran jiya fa har naturawa wannan matar da tayi miki hadin kayayyakin nan lokacin bikinki kudi suma tayi musu kuma nasan itama harda kazar zata dafo musu"

"To shikenan ai iya natan ya isa tunda yama fi kyau nifa na bikina har na haifi hudah yana jikina..."

Harararta Bilkisu tayi,

"Ban son fitsara"

"Yi hakuri Adda maigado subutar baki ce" daga haka ta shige bathroom domin yin alwala.

Daukar hudah tayi ta fita domin yunwa take ji, atsakar gida ta iskesu saman katuwar tabarma wata na sallah wata kuma ta idar rashin ganin ya mudan yasata zargar kila ko yatafi, zaunar da hudah tayi tashiga kitchen, faten doya da wake shi akayi da rana yanzu kuma da daddare tuwon shinkafa ne miyar zogale, tuwon ta zuba ta dauko tadawo wurin hudah ta soma bata itama tana ci da haka har amma tafito ta samesu. Zama tayi kusa da ita tana tsokanar hudah,

"Acici kinzo zaki cinye min abinci nida mijina, to maza kiyi kibar min gidana...." Ta karashe maganar tana jan kunnenta daya, rike kunnen da taja hudah tayi tana guduwa jikin bilkisu, janyeta tayi tana kallon amma,

"Zo baby na rabu da amma kinji, maza ci tuwo idan baki koshi bama inkaro miki"

"Badai tuwo na ba tunda ba ita ta tuka minba"

Kowa na wurin saida yayi dariya saboda jin abinda tace, mamaa ma fitowar tayi tana dariya nan tasamu gefen tabarma ta zauna,

"Yawwa mai gado wai nikam meyasa kikeda taurin kaine? Meyasa duk ranar da dan uwanki mudassir yazo bakya sakar masa fuska ku gaisa? Iya gaisawar ce fa kadai daga ita shikenan babu wani abu, dan Allah ki gyara"

"To ammah insha Allah" daga haka taci gaba da cin tuwonta tana sauraren zantukan da su mamaa keyi wanda baya rasa nasaba da shirye shiryen bikin su Hindu lokaci lokaci ta kan dan saka baki harta kammala cin tuwon tatashi taje tana wanke musu hannu itada hudah daga nan dakinta tawuce tabaje akan gado bayan ta dauko yar madaidaiciyar laptop dinta, tana ji yara suna go slow din shigowa dan kiran hindu da meenah wanda ko ba afada ba tasan angwayen ne masu kiran. Aikinta taji gaba dayi na rubuta takardar neman hutu har na tsawon sati biyu wato (casual leave) saboda bikin su meenah domin tana bukatar isasshen lokaci so take idan biki yarage saura kwana uku saita nema kamar dai yadda tayi abikin mamaa. Har misalin karfe 9 saura idonta na kan laptop din tana wani aikin daban, shigowar mamaa ce ta katseta ta tashi zaune tana gyara hudah wacce ke makale ajikinta tana bacci,

"Adda maigado faruk yazo zamuje mu tafi, ko inbar miki hudah ta kwana?"

"Ke wai ban hanaki fadar sunan mijinki kai tsaye ba, tunda ga yarku ai gara kirinka sakayawa da abban hudah wallahi idan kuma baki gyaraba wata rana sai kinji sunan nan abakin yarki"

"Wallahi Adda bana fada agida anan ne dai nake fadar sunanshi"

"Nidai na fada miki ai, dauketa kutafi da ita kinga gobe zan fita aiki kuma idan nafita bazata yarda da kowaba sai kuka zata ishi mutane dashi da dai weekend ne sai kibarta"

Daukar hudah mamaa tayi suka fita bayan bilkisu tasaka hijabinta, atsakar gida suka samu ammah da Faruk mijin mamaa suna gaisawa. Yana ganin bilkisu ya soma dariya yana cewa,

"Barka da fitowa babbar yaya, anwuni lafiya"

"Lafiya lau faruk ya mutanen gida, ya aiki"

"Lafiya lau anty mai gado"

Dunguma sukayi gaba dayansu suka fita banda amma,suna fita tun daga compound din gidan kamshin turaren su hindu ya budadesu suda angwayensu kowacce suna tsaye agefe itada angonta suna hira,

Dukkaninsu saida suka matso suka gaisa da bilkisu kafin takoma gida, tana shiga daki ta iske miss called din hamood zama tayi gefen gadonta tana kokarin bin kiran yasake kiranta nan ta daga bayan ta lumshe idonta tana saurarensa, kamar koda yaushe sun shafe lokuta masu yawa suna hira har saida bacci yaci karfinta sannan sukayi sallama.
Chapter 2 · 0% Book details