← Book details Kaddara Ta Riga Fata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 66

Sashe 58

Kaddara Ta Riga Fata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dr Hussain yana kawuwa nan ya sunkuyar da kanshi yana zubar da hawaye mai masifan yawan gaske, duk illahirin jikin shi rawa, yana wani kuka ko mace albarka, murya a bayyane yana cewa, "shikenan Aishan mu, Allah sarki Aishan mu".

Hummy ganin yanayin da Dr ya shiga ya sakani tafiya inda yake da sauri na rungume kanshi ina kuka nace, "Mutuwa tayi? Aishan dama ta mutune baby? Wayyo baby na kayi shiru don Allah, ina su Ummi"? Na faɗa ina ƙara rungume shi a jikina, shi kuma baiƙi ba ya manna kan shi a ƙirjina yana kuka mai sautin gaske.

Gaba É—aya su Abbi kukan suke shi da su Ummi, faisal ma kuka ya keyi kaman mace, Amaal kuma zuwa tayi ta rungume Ummi tana nata kukan.

Jijjiga kai Daddy yake tayi yana faɗin "wannan shine ikon Allah, wannan duniya ƙaramar wurine, ikon Allah humaira wani ƙaddaran ne yake shirin maimaita kanshi kuma, yau kuma mai nake sake ji da gani a rayuwata?" yana kuka ya ƙarasa wurin Dr Hussain ya ɗaga shi daga jikin Hummy, duban irin yadda idon Dr ya koma ya saka shi jawo jikin shi ya rungume shi ƙam a jijinshi yana kuka yana bubbuga bayan Dr.

Ni Aunty nice juyawa nayi na dubi miss xerks da ta wangale baki tana shaftara kuka kaman ance mata yau za' a mata auren dole da Hassan nace, "besty zo mu koma nigeria muyi kukan sai mudawo gobe idan Allah ya kaimu muji me yake faruwa ne? Hala ma mum sayyeed da jikar kulu suna ta vibration dom suji me yake wakana, haka muka fita sum sum sum mu ka bar su suna kukan su.

*©AUNTY NICE CE*✍🏻✍🏻✍🏻
[9/9, 21:42] Bsty: *°🔘°ƘADDARA TA RIGA FATA°🔘°*
     *1442H/2020M.*
   
®☄
*GASKIYA WRITERS ASSOCIATION✍*
_{Gaskiya ɗaya ce daga ƙinta sai ɓata, burinmu mu faɗakar da al'umma domin ribantar duniya da kuma lahira.}_
       ```🎐G•W•A🎐```
*_GASKIYA DOKIN ƘARFE•_*🏇🏼

*NA MARUBUCIYA:-*
*AUNTY NICE✍🏼*
*@wattpad AuntyNice.*

*SADAUKARWA GA ƳAƳA NA HASKEN ZUCIYA TA:-*
*NABEELAH ARABI*
*NUHU ARABI*

Wattpad:- *GaskiyaWritersAsso.*
Gmail:[email protected]
Youtube Channel:- *GASKIYA 24TV.*
Bakandamiya:-
*GASKIYA WRITER'S ASSOCIATION.*

*SHAFI NA 46📑*

*__________📖* Uncle Abdallah kuma da Abba ganin nida su Ummi duk mun suma a wurin sai sukaji hankalinsu yayi matuƙar tashi, jiki na ɓari Abba ya ƙira number Dr su, shi kuma Uncle Abdallah yadda kasan tsohon soja haka jikin shi yake rawa, daga ya dubi Aisha sai yaji kaman yayi ta ihu don tsananin tausayinta da shiga tashin hankali, a zuciyar shi kuma yana ayyana duk wanda yake da hannu a cikin raping ɗin Aisha da akayi wallahi bazai barshi ya sarara ba.

Dr su biyu suka zo, da yake Daddy ya gaya mishi case ɗin da yawa, zuwan su gaba ɗaya suka fara aikin ceto rayuwar mu, babu ɓata lokaci nida Aunty hauwa muka farfaɗo, amma Ummi dole suka ɗauketa akayi mota da ita, muna tashi daga ni har Aunty hauwa da gudu mukayi wurin Aisha, zuwa lokacin naga an rufe mata jikinta da bedsheet, ba kaman zuwan mu tana kwance haihuwar uwarta ba, rungumeta Aunty hauwa tayi tana kuka kamar ranta zai fita, nima haka na haɗasu na rungume ina tayata kukan, da ƙyar Uncle Abdallah ya sa muka sake ta, shi ya ɗauketa mukayi hanyar zuwa asibitin Dr Basheer, wato *CITY CLINIC* da yake wannan asibitin su Ummi suke zuwa, muna zuwa asalin babban likitan wato Dr Basheer yayi kan Aisha shi da wasu nurses guda 2, ita kuma Ummi ɗayan Dr sani ya rufu akanta.

Ni dai ranan na koma kaman mace, kafaɗan Aunty hauwa kawai na kwantar da kai na sai kuka muke ta rerawa nida ita, daga Abba har Uncle Abdallah kallon mu sukeyi ba tare da sun iya furta komai ba, gaba ɗaya kansu suke ji ya kulle, waye zai shigo har cikin gidan ya iya wucewa har ɗakin Aisha yayi mata wannan mummunan illar ba'a ganshi ba? Gaskiya abun yayi matuƙar ɗaure musu kai, kawai sunyi shiru ne suna jiran farfaɗowar Aisha da Ummi ne kawai, sai su shiga bincike.

Ummi bata daɗe ba ta farfaɗo, amma Aisha sai da tayi rabin awa tukun ta farfaɗo, hakan ma tana farfaɗowa suka mata alluran kashe zafi don su samu su mata ɗinkin wurin, domin ba ƙaramin jin ciwo tayi ba, bayan an gama komai su Abba suka bi Dr basheer har cikin office ɗin shi, inda yayi musu bayanin BPn Ummi yayi mummunan hawa, ya kamata a kiyaye abinda zai dinga tayar musu hankali, sannan case ɗin Aisha kuma yayi musu jajen abinda ya faru, sannan ya ce su neme police a cikin case ɗin, don ma abinda ya kamata suyi ne tun farko, wato saida police tukun ya karɓi Aisha, a haka muka wuce zuwa ɗakin da Ummi take kwance idonta a rufe kaman mai bacci, amma kuma ba baccin ta keji ba, kawai tana sauraren kukan da Aunty Hauwa ta keyi ne, wanda ta kejin shi kaman zai fasa mata heart ɗinta.

Gefen Aunty hauwa Uncle Abdallah ya zauna yana ta rarrashinta, yana kuma roƙonta da ta je wurin Aishan ta zauna da ita, shi kuma Abba zuwa yayi ya riƙe hannun Ummi, wanda tana jin zuwan shi inda ta ke ta buɗe idon ta a hankali , ƙurawa Abba ido tayi nata idon ma ya fara zubar da hawaye.

"kiyi haƙuri Fatima, insha Allahu yanzu zamuje mu miƙawa police case ɗin, kuma ina da tabbacin zasu gano wanda ya shiga har gidan ya aikata wannan mummunan aikin wa Doughter, insha Allahu zamu bi mata hakkin ta", Abba ya faɗa yana jijjiga kan shi alaman abinda yake faɗa babu fashi, hannu Ummi ta miƙo mishi ya ɗaga ta, zama tayi fuskanta ɗauke da wani irin ƙunci, amma sai da tayi ɗan murmushi kaɗan, ido ta ƙurawa Aunty hauwa na zuwa wani lokaci, sannan ta dawo da kallonta kaina da nake tsaye a bakin ƙofan ɗakin tun shigowan mu ina kuka a tsaye a wurin, sannan ta karkaɗa kanta, ta dawo da kallonta kan Abba, hannuta ta ɗaga ta ɗaura a kan saitin zuciyarta, "Abba wani police zaku nema akan wanda yayi fyaɗe wa ƴata? Bayan wanda ya aikata yana cikin gidan da kuke?" runtse ido ta sakeyi hawaye yana zuba a fuskanta da gudun gaske.

Da sauri Abba ya dubeta yace, "ban gane me kike faÉ—a ba Fatima? Kina nufin kinga shigowan wani ne cikin gidan, ko kuma me kike nufi"? Ya faÉ—a gaba É—aya hankalin shi a tashe.

"Abban su kana tunanin akwai wani daban da zai aikata wannan mummunan aikin bayan ɗanmu Hassan? Tabbas Hassan shi ne yau ya saka hawaye mai zafi da ƙunan xuciyar da bamu san ranan ƙarshen shi ba a rayuwar mu, Hassan yau shi yasaka na kejin kunyar duban idon Abdallah da Hauwa, yake sani jin da wani idon zan dubi Baban Narabi, yayah zanji ranan da Allah ya haɗani da Baba Umar yaji irin saken da nayi na riƙon amanan da ya bani?" kuka Ummi ta saka mai ƙarfin gaske, wanda daga ni har Aunty hauwa ma kukan mu keyi, jiki na rawa Abba ya sake buɗe baki yace.

"Fatima ban fahimci me kike nufi ba, shin kinga Hassan ya shiga É—akin ta ne? Don Allah ki fahimtar dani Fatima, komai ya kulle mun", ya faÉ—a kaman shima raunin shi zai saka shi zubar da hawayen.

Juyawa Ummi tayi ta dubi kowa da yake cikin ɗakin, sannan ta dubi Abba tace, "gamu nan dukkan mu a hallare a ɗakin, shi kaga Hassan a cikin mu? Baka tunanin mai ya hana shi zuwa inda muke? Wallahi jikina ya bani Hassan ne ya aikata wannan mummunan illar wa rayuwar Aisha, domin yayi katanga wa ɗan'uwan shi na auren Aisha, shi kuma a bashi aurenta, kuma nayi alƙawari idan har nono na Hassan ya sha tou na haramta mishi auren Aisha har abada".

Waya da sauri Abba ya ɗauko ya shiga dialing number Hassan, wanda dukka layin shin a rufe suke, haka Abba ya ajiye wayan shi jiki a sanyaye, ɗago idon shi yayi ya dubi uncle Abdallah yace, "muje mu miƙa case ɗin zargin Hassan da mukeyi a wurin police" Abba ya faɗa jikin shi yana ta rawa, wani zufah mai azaban zafi yana karyo mishi.

Murmushi Uncle Abdallah yayi ya matsar da Aunty hauwa dake lafe a jikinshi ya ƙaraso inda Abba yake, hannu ya dafa a kafaɗan shi yace, "haba Yayah! Kana ganin ni da kaina zan iya shari'a da ɗana ne akan ƴata? Wallahi Allah ya sauwaƙa, nasan koda Baba Umar yana raye bayida abinda zaiyi sama da addu'a da haƙuri, ae Hassan ɗan mune, kuma idan ba rashin godiyar Allah irin namu ba, ta yayah zamuyi shari'a da kai? Don kuwa yin shari'a da Hassan tamkar da kai mukayi, wannan abun mun ɗauke shi a ƙaddaran rayuwar Aisha, kuma wannan shine *ƘADDARA TA RIGA FATA* munyi fatan haɗa aure tsakanin Hussain da Aisha, amma ƙaddaran da ta gifta tsakanin Hassan da Aisha ta saka dole mu haƙura mubar Hassan ya auri Aisha, mudai fatan mu Allah ya bata sauƙi, don ni tun ganin Aisha ban zargi kowa ba sai Hassan, saboda irin kalaman shi da yayi tayi a daren jiya, dama duk hankalina bai kwanta ba, Allah-Allah nake gari ya waye muje Narabi akan maganan auren Hussain da Aisha, toh amma ga abinda Allah ya aiko mana, dole muyi haƙuri".

"Idan kai kanaga ka haƙura tou ni ban haƙura ba, dole sai nayi shari'a da Hassan, kuma babu abinda zai hana auren Aisha da Hussain, don abinda yayi bai isa yasa mu chanja ra'ayin mu ba, nayi rantsuwa koda mazan duniya sun ƙare tou har abada Aisha bazata taɓa auren Hassan ba, sharrin shi ya koma kanshi", Abba ya faɗa yana miƙewa don tafiya wurin police.

Uncle ne ya ɗauki waya ya ƙira Baban Narabi, a handsfree ya saka, sannan yayi sallama ya gaida Baban, murya a raunane ya shiga zayyanawa Baban abinda yake faruwa, a ɗaya ɓangaren kuma sai, "innalillahi wa'innah ilahir raji'un" Baba yake ta maimaitawa, bayan Uncle ya gama gayawa Baban komai, sai Baban yace ya bashi Abba, nan Uncle ya gaya mishi wayar tana handsfree kowa yana jin shi, gyaran murya Baba yayi sannan yace.
Chapter 58 · 0% Book details