Sashe 7
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Acan gidan GM kuwa Ummu al'amin ta dan sauko kadan amma fa ba hakura tayi ba zuciyarta ce kawai ta bata shawarar ta nunawa abu al'amin cewar ta hakura ta yarda yayi aurenshi amma kuma zata rinka yi musu zagon kasa shida amaryar, hakan yasata yin dariyar mugunta ta tashi ta nufi sashensa wanda yake kusa da nata, acan cikin dakinsa ta sameshi yana duba wani littafi na tafsirin suratul hud, da sallama ta shiga ta zauna kusa dashi gamida riko hannunsa, littafin ya rufe ya jiyo yana kallonta "ummu ya akayi"
"Abu al'amin kayi hakuri da abinda nayi maka akan maganar aurenka hakika nasan kai adali ne kawai sharrin shaidan ne yasa na fada maka wannan maganar amma kayi hakuri, Allah ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"
Hancinta yaja yace "ya wuce ummu kidaina bani hakuri, nasan kishiya tana da zafi awurinku mata amma haka zaku daure ku rinka karbarta aduk yanayin da tazo muku"
Jikinshi ta shiga tana murmushin kissa.
***
Tunda biki ya rage saura sati uku mahaifin goodness ya kirawo yayarta anty bilkisu tazo yaje ya ciro yan kudadensa da ya jima yana tarawa saboda auren goodness ya basu yace suje kasuwa su iyo mata siyayyar kayan kitchen domin GM yace kayan daki da sauran tarkace ba sai an kawo mata ba zai zuba komai murna wurin anty bilki harda kuka saboda jin wanda yar uwarta zata aura,tabbas tasan goodness tana daf da samun *WANI HASKE* acikin rayuwarta wadda zai yi sanadiyyar haska danginsu baki daya, nan aka shiga gudanar da shirye shiryen biki mama ta shirya ta tafi okene domin yin tsubbuce tsubbucenta tareda tahowa da dangi, amma har yanzu goodness da GM basu haduba sai lokaci zuwa lokaci goodness tana kiransa da layin zain dinsa tayi shiru tana sauraren muryarsa,
Kudi kimanin naira dubu dari uku GM ya aiko dashi akan ayi komai da komai domin shidai ba bidi'a zaiyi ba wannan kudin da zai aiko dashi za ayi mata duk wata hidima data kamata, tsalle da murna wurin goodness ba a iya musaltawa, anty bilki kuwa sai gyara yar kanwarta take saboda shirin kota kwana sannan sun shiga kasuwa sun jido kaya hadaddu sabbi english wears akwati biyu dogayen riguna ne yan kanti sai riguna da wanduna da skirts da sleeping dress da inner wears domin goodness bata iya saka atamfa ko leshi ba, ma sai da biki ya rage saura sati daya ta dawo ita da mutanensu daga okene tana dawowa gida ya kancame da danginsu ko ina agidan ka juya wani yare suke yi wanda nidai ummi A'isha bana fahimtar sa.
Tunda ma tadawo kullum sai sunje church anyiwa goodness addu'a da haka har ranar bikin tazo ranar a church suka kwana anata addu'o'i, washe gari ranar friday aka daura auren goodness da GM bayan an idar da sallar juma'a a masallacin mahaifin GM, ana gama daura auren ya koma gida yana sanye da farin yadi mai laushi da kyau, da gudu al'amin yazo yana bashi labari
"Abbu wancan gidan wasu sunzo sunje sunata shara aciki abbu, abbu makotan munne?"
Hannunsa ya kama yana murmushi "al'amin surutu, eh makotanmu ne"
"To abbu wasu fa basuda hijabi irin na ummu na"
Ras gabanshi ya fadi shi sai yanzu ma ya tuna da cewar fa ashe ba musulma ya aura ba, "al'amin ya isa haka kayi shiru babu kyau yawan magana"
Yafada tareda jan hannunshi zuwa sashensa.
Biki yayi biki domin ma ta cashe iya cashewa a church yayinda goodness kuma taci ado cikin wedding gown fara gashi anyi mata gyaran gashi tasha attach mai kyau, kafarta da hannayenta duk an gyara mata, musamman ma ta kaita aka yi mata gyaran fuska, su gyaran gira ne duk sai da aka yi mata fuskarta tasha make up tayi kyau har ta gaji, kasancewar a church zasu gudanar da bikin yasa anty bilki ta bisu a dole amma indai bata manta ba rabonta da church tun tana yar mitsitsiya lokacin da ma take zuwa da ita.
Church din an kawatashi da decoration yasha balam balam balloons manya manya kala kala, goodness tana tsugunne gaban pastor ta rufe idonta sauran jama'ar kuma suna zazzaune suna sauraren pastor ciki harda promise tsohon saurayin goodness wanda yaketa dariyar mugunta ganin mijin goodness bai zo church ba,zobuna guda biyu aka mikowa pastor (wedding ring) ya karba,zubunan masu kyau daya na gold daya na silver, na gold din goodness ta saka a dan yatsanta na tsakiya wato marriage, dayan zoben kuma akace na mijinta ne lallai lallai ta bashi yasa, tafi aka hau yi da ihu shikenan aure ya kullu nan aka shiga ihu aka saki kida ma tafito tana rawa kamar zata karye, sai around 3 suka baro church suka dawo gida, nan baban goodness ya kirata dakinsa yayi mata fada akan kar tace zata rinka biyewa ma bayan aurenta domin tana iya kashe mata aure, sannan su shirya anjima da daddare za akaita gidan mijinta, dai dai nan ma tashigo cikin dakin,
"Ah papa goodness whats are you talking about? Akai goodness yau without pastor visit her house and pray? Za akaita gidanta batare da pastor yaje yayi mata addu'a ba?"
Cikin fushi Baban goodness ya mike "ke chioma nafara gajiya da wannan rashin mutuncin naki, akanme pastor zaije gidanta? Ko kin san waye mijinta kuwa? Kina so ya saketa ne tun kafin akaita gidan? Kince wannan na yarda kince wannan nayarda to yanzu kam i won't accept this nonsense, i can't tolerate your nonsense, tun yaushe kuke addu'ar? Duk wacce kukayi bata isheku ba sai kun je gidanta kun kashe mata aure? It can't, impossible" yafada yana huci,wani ihu mama ta kurma ta dora hannu aka tana kuka,
"Oh chineke,papa goodness what do yo mean? You mean you can't allow pastor to visit goodness house to pray? Oh people, people pls come and aid me, oh God, chineke" tashi goodness tayi ta rike ma tana bata hakuri "oh ma, pls stop saying this, am sorry ma, kinji maganar da papa yafada idan kunje zai sakeni, kiyi hakuri ma, pls and pls"
Shiru ma tayi tareda share hawayen fuskarta "that's the reason why i have neva like your marriage with hausa man, i know there is too much crises around it, tun kina yar karama naso ki auri Christian wanda zakiyi rayuwar jin dadi amma see my dream didn't come true,my ambition for you to became a pastor's wife will neva Eva been....!" Tasake rushewa da kuka, nan anty Bilkisu ta shigo tana tambayar meya faru, haduwa sukayi suka cigaba da bawa ma hakuri amma dakyar ta hakura sannan aranta ta dauki aniyar ko bayan bikinne sai sunje da pastor gidan yayi addu'a.
Bayan magrib aka fara shirye shiryen kai amarya GM ya turo musu motoci guda hudu amma ma karfi da yaji ta hana goodness shiga daya daga cikin motocin sai wacce pastor ya kawo wacce tasha decoration tasha balloons ita ma ta saka goodness aciki itama ta shiga suka tafi, tunda akaje gidan kowa yake santi domin gidan ya tsaru yayi kyau sosai kai in banda rabo ma to da goodness ko a mafarki ba zata samu wannan mijin da wannan gidan ba to bahaushe yace rabo sai mai shi, kowa ya yaba wannan gidan, sashenta daban kuma shine na karshe, kayan funitures din da ya zuba mata ba na wasa bane kayane masu shegen kyau da tsada, babban falo guda daya da bedrooms guda biyu, sai kitchen da dining area, abin dai gwanin sha'awa komai green, nan ma ta shiga rawa harda guda, sun dade agidan suna ganin tsarin gidan sannan suka tafi suka bar goodness wanda take kuka biyu, na dadi da farin ciki.
Ko wanne irin zama za ayi tsakanin goodness da Abu al'amin? Mu saurari shafi na gaba.
_*Ummi A'isha*_👌🏻
[10/28, 9:27 PM] +234 810 100 9022: [8/24, 10:31 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_31-32_
~~~ Bayan kowa ya tafi an bar iya goodness acikin dakinne ta mike gamida tattare doguwar gown din dake jikinta wacce ta kasance light blue da adon _flowers_ pink colour ajiki, tashi tayi ta fara zagaya dakunan da suka kasance mallakinta,
Kamar a mafarki take ganin abubuwan da suke faruwa, wai yau itace ta zama matar GM mutumin da yafi karfin ajinta, falo ta fita wanda girmansa kadai abin kallone yasha kayan alatun more rayuwa an zuba komai green, dayan dakin ta shiga shima ciki yana dauke da dan madaidaicin gado shima komai naciki kalarshi green, fitowa tayi ta shiga kitchen, kitchen din ya tsaru kamar a kasar turai ga kayan amfani nan birjik masu amfani da wutar lantarki,
"Thank you God" ta fada tareda runtse idanuwanta nan take hawayen farin ciki suka fara sauka akan kumatunta, wani sanyi taji yana ratsa babban dan yatsan kafarta yana haurawa cikin kwakwalwarta,
Cikin dakinta ta koma ta zauna akan gadonta tana tunanin yadda zata iya hada idanuwa da GM a matsayin mijin aurenta,tana nan zaune har taji bacci ya fara barazanar dauketa domin agajiye take lis gashi kwana biyun nan kullum a church suke kwana dan haka basa samun damar yin bacci, ko gown din jikinta bata cire ba haka ta matsa can tsakiyar gadonta taja pillow ta dora kanta ta kwanta take bacci yace muje zuwa.
A bangaren angon kuwa daidai lokacin da ya jiyo hayaniyar yan kawo amaryar yana zaune a cikin falonshi al'amin yana kwance akan cinyarshi yana koya masa wani littafin hadisi na fawakiha kusan duk hadisan dake ciki saukaka ne kuma gajeru basuda tsayi,jin al'amin yayi shiru ya tabbatar masa da cewar yayi bacci daukeshi yayi ya kwantar dashi akan doguwar kujera ya tafi jikin window ya daga labule ya fara hangen yan kawo amaryar,
Baya iya gano amaryar domin an kakkareta sai dai yana hango sauran matan wadanda duk cikinsu mace daya ce mai lullubi ajikinta, yana nan tsaye har suka shiga part din nata suka fito suka tafi daidai lokacin ummu al'amin ta shigo falon tana cewa,
"Bari na dauki al'amin saboda naga amaryar ta iso tun dazu, Abu al'amin Allah ya baku zaman lafiya"
"Abu al'amin kayi hakuri da abinda nayi maka akan maganar aurenka hakika nasan kai adali ne kawai sharrin shaidan ne yasa na fada maka wannan maganar amma kayi hakuri, Allah ya baka ikon yin adalci a tsakaninmu"
Hancinta yaja yace "ya wuce ummu kidaina bani hakuri, nasan kishiya tana da zafi awurinku mata amma haka zaku daure ku rinka karbarta aduk yanayin da tazo muku"
Jikinshi ta shiga tana murmushin kissa.
***
Tunda biki ya rage saura sati uku mahaifin goodness ya kirawo yayarta anty bilkisu tazo yaje ya ciro yan kudadensa da ya jima yana tarawa saboda auren goodness ya basu yace suje kasuwa su iyo mata siyayyar kayan kitchen domin GM yace kayan daki da sauran tarkace ba sai an kawo mata ba zai zuba komai murna wurin anty bilki harda kuka saboda jin wanda yar uwarta zata aura,tabbas tasan goodness tana daf da samun *WANI HASKE* acikin rayuwarta wadda zai yi sanadiyyar haska danginsu baki daya, nan aka shiga gudanar da shirye shiryen biki mama ta shirya ta tafi okene domin yin tsubbuce tsubbucenta tareda tahowa da dangi, amma har yanzu goodness da GM basu haduba sai lokaci zuwa lokaci goodness tana kiransa da layin zain dinsa tayi shiru tana sauraren muryarsa,
Kudi kimanin naira dubu dari uku GM ya aiko dashi akan ayi komai da komai domin shidai ba bidi'a zaiyi ba wannan kudin da zai aiko dashi za ayi mata duk wata hidima data kamata, tsalle da murna wurin goodness ba a iya musaltawa, anty bilki kuwa sai gyara yar kanwarta take saboda shirin kota kwana sannan sun shiga kasuwa sun jido kaya hadaddu sabbi english wears akwati biyu dogayen riguna ne yan kanti sai riguna da wanduna da skirts da sleeping dress da inner wears domin goodness bata iya saka atamfa ko leshi ba, ma sai da biki ya rage saura sati daya ta dawo ita da mutanensu daga okene tana dawowa gida ya kancame da danginsu ko ina agidan ka juya wani yare suke yi wanda nidai ummi A'isha bana fahimtar sa.
Tunda ma tadawo kullum sai sunje church anyiwa goodness addu'a da haka har ranar bikin tazo ranar a church suka kwana anata addu'o'i, washe gari ranar friday aka daura auren goodness da GM bayan an idar da sallar juma'a a masallacin mahaifin GM, ana gama daura auren ya koma gida yana sanye da farin yadi mai laushi da kyau, da gudu al'amin yazo yana bashi labari
"Abbu wancan gidan wasu sunzo sunje sunata shara aciki abbu, abbu makotan munne?"
Hannunsa ya kama yana murmushi "al'amin surutu, eh makotanmu ne"
"To abbu wasu fa basuda hijabi irin na ummu na"
Ras gabanshi ya fadi shi sai yanzu ma ya tuna da cewar fa ashe ba musulma ya aura ba, "al'amin ya isa haka kayi shiru babu kyau yawan magana"
Yafada tareda jan hannunshi zuwa sashensa.
Biki yayi biki domin ma ta cashe iya cashewa a church yayinda goodness kuma taci ado cikin wedding gown fara gashi anyi mata gyaran gashi tasha attach mai kyau, kafarta da hannayenta duk an gyara mata, musamman ma ta kaita aka yi mata gyaran fuska, su gyaran gira ne duk sai da aka yi mata fuskarta tasha make up tayi kyau har ta gaji, kasancewar a church zasu gudanar da bikin yasa anty bilki ta bisu a dole amma indai bata manta ba rabonta da church tun tana yar mitsitsiya lokacin da ma take zuwa da ita.
Church din an kawatashi da decoration yasha balam balam balloons manya manya kala kala, goodness tana tsugunne gaban pastor ta rufe idonta sauran jama'ar kuma suna zazzaune suna sauraren pastor ciki harda promise tsohon saurayin goodness wanda yaketa dariyar mugunta ganin mijin goodness bai zo church ba,zobuna guda biyu aka mikowa pastor (wedding ring) ya karba,zubunan masu kyau daya na gold daya na silver, na gold din goodness ta saka a dan yatsanta na tsakiya wato marriage, dayan zoben kuma akace na mijinta ne lallai lallai ta bashi yasa, tafi aka hau yi da ihu shikenan aure ya kullu nan aka shiga ihu aka saki kida ma tafito tana rawa kamar zata karye, sai around 3 suka baro church suka dawo gida, nan baban goodness ya kirata dakinsa yayi mata fada akan kar tace zata rinka biyewa ma bayan aurenta domin tana iya kashe mata aure, sannan su shirya anjima da daddare za akaita gidan mijinta, dai dai nan ma tashigo cikin dakin,
"Ah papa goodness whats are you talking about? Akai goodness yau without pastor visit her house and pray? Za akaita gidanta batare da pastor yaje yayi mata addu'a ba?"
Cikin fushi Baban goodness ya mike "ke chioma nafara gajiya da wannan rashin mutuncin naki, akanme pastor zaije gidanta? Ko kin san waye mijinta kuwa? Kina so ya saketa ne tun kafin akaita gidan? Kince wannan na yarda kince wannan nayarda to yanzu kam i won't accept this nonsense, i can't tolerate your nonsense, tun yaushe kuke addu'ar? Duk wacce kukayi bata isheku ba sai kun je gidanta kun kashe mata aure? It can't, impossible" yafada yana huci,wani ihu mama ta kurma ta dora hannu aka tana kuka,
"Oh chineke,papa goodness what do yo mean? You mean you can't allow pastor to visit goodness house to pray? Oh people, people pls come and aid me, oh God, chineke" tashi goodness tayi ta rike ma tana bata hakuri "oh ma, pls stop saying this, am sorry ma, kinji maganar da papa yafada idan kunje zai sakeni, kiyi hakuri ma, pls and pls"
Shiru ma tayi tareda share hawayen fuskarta "that's the reason why i have neva like your marriage with hausa man, i know there is too much crises around it, tun kina yar karama naso ki auri Christian wanda zakiyi rayuwar jin dadi amma see my dream didn't come true,my ambition for you to became a pastor's wife will neva Eva been....!" Tasake rushewa da kuka, nan anty Bilkisu ta shigo tana tambayar meya faru, haduwa sukayi suka cigaba da bawa ma hakuri amma dakyar ta hakura sannan aranta ta dauki aniyar ko bayan bikinne sai sunje da pastor gidan yayi addu'a.
Bayan magrib aka fara shirye shiryen kai amarya GM ya turo musu motoci guda hudu amma ma karfi da yaji ta hana goodness shiga daya daga cikin motocin sai wacce pastor ya kawo wacce tasha decoration tasha balloons ita ma ta saka goodness aciki itama ta shiga suka tafi, tunda akaje gidan kowa yake santi domin gidan ya tsaru yayi kyau sosai kai in banda rabo ma to da goodness ko a mafarki ba zata samu wannan mijin da wannan gidan ba to bahaushe yace rabo sai mai shi, kowa ya yaba wannan gidan, sashenta daban kuma shine na karshe, kayan funitures din da ya zuba mata ba na wasa bane kayane masu shegen kyau da tsada, babban falo guda daya da bedrooms guda biyu, sai kitchen da dining area, abin dai gwanin sha'awa komai green, nan ma ta shiga rawa harda guda, sun dade agidan suna ganin tsarin gidan sannan suka tafi suka bar goodness wanda take kuka biyu, na dadi da farin ciki.
Ko wanne irin zama za ayi tsakanin goodness da Abu al'amin? Mu saurari shafi na gaba.
_*Ummi A'isha*_👌🏻
[10/28, 9:27 PM] +234 810 100 9022: [8/24, 10:31 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_31-32_
~~~ Bayan kowa ya tafi an bar iya goodness acikin dakinne ta mike gamida tattare doguwar gown din dake jikinta wacce ta kasance light blue da adon _flowers_ pink colour ajiki, tashi tayi ta fara zagaya dakunan da suka kasance mallakinta,
Kamar a mafarki take ganin abubuwan da suke faruwa, wai yau itace ta zama matar GM mutumin da yafi karfin ajinta, falo ta fita wanda girmansa kadai abin kallone yasha kayan alatun more rayuwa an zuba komai green, dayan dakin ta shiga shima ciki yana dauke da dan madaidaicin gado shima komai naciki kalarshi green, fitowa tayi ta shiga kitchen, kitchen din ya tsaru kamar a kasar turai ga kayan amfani nan birjik masu amfani da wutar lantarki,
"Thank you God" ta fada tareda runtse idanuwanta nan take hawayen farin ciki suka fara sauka akan kumatunta, wani sanyi taji yana ratsa babban dan yatsan kafarta yana haurawa cikin kwakwalwarta,
Cikin dakinta ta koma ta zauna akan gadonta tana tunanin yadda zata iya hada idanuwa da GM a matsayin mijin aurenta,tana nan zaune har taji bacci ya fara barazanar dauketa domin agajiye take lis gashi kwana biyun nan kullum a church suke kwana dan haka basa samun damar yin bacci, ko gown din jikinta bata cire ba haka ta matsa can tsakiyar gadonta taja pillow ta dora kanta ta kwanta take bacci yace muje zuwa.
A bangaren angon kuwa daidai lokacin da ya jiyo hayaniyar yan kawo amaryar yana zaune a cikin falonshi al'amin yana kwance akan cinyarshi yana koya masa wani littafin hadisi na fawakiha kusan duk hadisan dake ciki saukaka ne kuma gajeru basuda tsayi,jin al'amin yayi shiru ya tabbatar masa da cewar yayi bacci daukeshi yayi ya kwantar dashi akan doguwar kujera ya tafi jikin window ya daga labule ya fara hangen yan kawo amaryar,
Baya iya gano amaryar domin an kakkareta sai dai yana hango sauran matan wadanda duk cikinsu mace daya ce mai lullubi ajikinta, yana nan tsaye har suka shiga part din nata suka fito suka tafi daidai lokacin ummu al'amin ta shigo falon tana cewa,
"Bari na dauki al'amin saboda naga amaryar ta iso tun dazu, Abu al'amin Allah ya baku zaman lafiya"