Sashe 40
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Abbu ka sosa min kunnena dan Allah" tafada cikin shagwaba,
"Jeki dakina ki dauko abin goge kunnen to"
Da saurinta ta tashi ta garzaya ta shiga bedroom dinshi ta dauko abin goge kunnen akan mirror dinsa ta kawo masa,
Bajewa tayi ajikinsa ta dora kanta akan cinyar sa yafara goge mata kunnen ta,
Sun dade ahaka har tsawon wani lokaci kafin ta tashi taje ta kwaso masa kayan karin kumallonsa ta kawo masa inda yake zaune,
"Abbu ba yanzu zaka fitaba ko?" Ta tambayeshi tana kallon fuskarsa wadda shikuma abincin gabanshi yake kallo,
"Yanzun nan zanyi wanka in fita,meya faru?"
Matsawa tayi kusa dashi, "abbu fita zakayi ka barni? Dan Allah ka tafi dani abbu" tana gama fadin haka sai hawaye sharrrrrr!
Juyawa yayi ya kalleta, "menene abin kuka binti? Ai masallaci zanje da sai mutafi tare"
Hannunta ya kamo ya rike cikin nashi, "abbu bana son katafi ka barni"
"Kiyi hakuri binti ai idan natafi ma zan dawo kinji"
Kai ta daga tana sake makale hannunsa cikin nata,
Tana nan tare dashi har ya kammala cin abincin yaje ya dauko littafi mai tsarki yadawo kusa da ita ya zauna, kwanciya ta sake yi ajikinsa yayinda shikuma ya bude alqur'anin yafara karanta suratul kahfi domin dacewa da hasken juma'ah,
Tana jin ya kammala karatun tafara sosa saman idonta har wurin ya dan fara kumbura idon yayi ja,
"Abbu kaga wurin da wannan kunamar ta cijeni shekaran jiya har yanzu bai warkeba"
Tashi zaune tayi tana nuna masa,
"Abbu zafi, sosa min"
Babu zato taji harshensa akan wurin yana juyawa,
"Abbu...!" Hannunsa yasa ya rufe mata bakinta yaci gaba da lasar fatar idonta da harshensa,
Ya jima yana yimata haka kafin ya tsaya ya kurawa gashin kanta ido wanda yayi masa kyau ainun,
"Binti bari naje nayi wanka, fita nake son yi"
Tashi tayi daga jikinsa ta matsa gefe, cikin bedroom dinshi ya shiga yayinda ita kuma ta rakashi da ido,
Tv ta kunna ta fara kallon African magic, har jabir ya fito ya sameta, kamshine yafara ziyartar hancinta hakan ya sanyata juyawa ta kalleshi, kamar kullum komai fari yasaka tun daga yadin jikinsa har takalmin kafarsa,
"Wowww...!" Tafada cikin zuciyarta,
"Abbu kayi kyau" tafada gamida tashi ta karasa gabansa ta tsaya tana kallonsa,
Hannunsa yasa ya fara shafa wurin da ya kumbura asaman idonta,hakan ya sata lumshe idanuwanta,
Kamar daga sama taji bakinsa kan nata yana tsotsar lips dinta,
Sunfi Minti biyar ahaka sannan yasaki bakin nata ahankali,
"Binti sai nadawo ko?"
Hannunsa ta kamo idonta cikeda kwalla, "abbu zaka tafi da farin cikina zaka barmin damuwa" tafada ahankali,
Hannuwan nata shima ya riko,
"Binti kinga yau juma'a zanje nayiwa mutane huduba kuma akwai gurin da nake son zuwa kafin lokacin masallacin yayi"
Dagowa tayi ta kalleshi yayinda kwallar da ta taru a idonta ta zubo kan kumatunta,
"Abbu wurin budurwar taka zakaje?" Tayi masa tambayar da ita kanta bata san lokacin da tayiba,
Lallausan murmushi yayi yasa hannunsa duka biyu akan kumatunta yafara share mata hawayen dake kan fuskar tata,
"Ni ba wurin macema zanje ba wurin namiji ne, wani dan kasuwa ne ya shirya wani dan kwarya kwaryar wa'azi domin fadakar da yan uwansa yan kasuwa akan illar tauye mudu da cin riba"
Murmushi tayi tadafe hannayensa dake kan kumatunta,
"Me zaka tafi ka barmin wanda zan rinka yi kafin kadawo?"
"Binti kiyita yiwa annabi salati tunda kinga yau juma'ah annabi kuma yace mu yawaita yimasa salati musamman ma ranar juma'a domin salatin da muke yimasa yana zuwa gareshi shiyasa annabi yace duk wanda ya yawaita salati agareshi to ranar gobe alqiyama zai samu cetonshi, idan kuma hakan bai samuba to kiyita fadin subhanalli wabi hamdihi, subhanallahil azim, domin annabi yace kalmomine masu saukin fada akan harshe sannan masu soyuwa awurin Allah kuma masu nauyi akan sikeli ranar auna ayyukan bayi"
Wani dadi taji ya ratsata agaskiya mutum mai ilmi yanada dadin zama sannan komai nashi akan tsari yake ita ta dade da fahimtar haka,
"Abbu to karka dade pls" hannunsa ta sauke daga kumatunta tafara murza yatsunshi, hatta hannun nashi kamshin turare yake zubawa,
"Binti bari mana karki karya min alwala ta ko kin manta abinda nafada miki jiya?"
Sakin hannunshi tayi tajuya cikeda kunya,
"Yanzu abbu dan wannan abun sai ya bata maka alwala"
Tafada bayan ta juya masa baya,
"Ehh mana binti, sai nadawo kinji"
"Ka kula da kanka abbu, Allah ya dawo min dakai gida lafiya"
Ba karamin dadin addu'ar da tayi masa yaji ba,
"Nagode binti"
Fita yayi ya tafi saboda yaga idan yaci gaba da tsaiwa awurinta zai dade bai tafiba, gaban window taje ta tsaya tana kallonsa lokacin da yake kokarin shiga cikin motarsa,
Har saida taga fitarsa daga gidan sannan tabar jikin window din tashiga bedroom dinshi tafara gyarashi tanayi tana yiwa annabi salati domin kwadayin samun rabon da taji jabir yace ana samu muddin aka dimanci yiwa annabi salati musamman ma aranar juma'a.
Gyara sashen jabir tayi tatas ta fesheshi da air freshener mai dadi sannan ta kulle ta dauki kwanukan data kawo masa breakfast ta fita zuwa sashenta,
"Oh Allah Sarki abbu" tafada tana dan murmushi akan fuskarta,
Sai da ta kammala gyaran sashenta ko ina yayi tsaf tsaf sannan ta zauna zaman kallo,
Tana nan zaune taji kiran mamansu ya shigo cikin wayarta wanda har sai da taji gabanta ya fadi domin bata san abinda zata fadawa ma ba,
Dakyar ta iya dauka jikinta har wani rawa yake yi, wata uwar tsawa taji ma ta daka mata da karfi sannan cikin zafin rai tafara magana,
"Goodness kinci amanata kin saba alqawarin da kika yimin tun farko, amma kisani sai na dauki mataki akanki"
Ido goodness ta zazzaro gamida toshe bakinta da hannuwanta, shikenan yanzu ma tasan ta musulunta saura kawai ta jirayi dan karamin yakin da zai afku, ta raya hakan acikin ranta,
Cikin tsawar data fi ta farko ma tace,
"Bakya jin abinda nake fada ne? Kiyi min magana tun kafin nazo har cikin gidan ki inci mutuncinki"
"Ma am so sorry pls, wallahi ba yin kaina bane kawai *wani haske* ne ya fado cikin rayuwata,amma kiyi hakuri ma"
"Ki rufe min baki munafuka, da ai cewa kikayi zaki rinka zuwa church din duk ranar Sunday amma yanzu gashi kin daina zuwa"
Wani sanyi taji ganin har yanzu 'ma' bata san ta musulunta ba,
"Ma zanzo, banida lafiya ne shiyasa nake zuwa church din bayan gidana amma idan nawarke zan zo"
"Saura idan kin warke ki k'i zuwa"
Tana gama fadin haka ta yanke wayar, tagumi goodness tayi tana tunanin gashi yanzu akan rashin zuwa church kadai ma tana fada to inaga idan taji ta karbi addinin gaskiya, ta jima tana tunani aranta Kafin ta tashi ta shiga kitchen,
Jalop din cous cous tayi wanda yasha kayan lambu aciki in banda kamshi babu abinda ke tashi, dan kadan ta zuba ta koma falo ta zauna, wayarta ta jawo ta shiga kiran jabir,
Cikin sanyin muryarshi taji yafara yi mata magana "amincin Allah ya tabbata agareki yake wannan yarinya"
Murmushi tayi mai dan sauti "abbu ba zaka dawo gida kaci abinci ba?"
"Binti ai ban gama abinda nake yi ba, ko zan dawo gidan nan ina jin sai dare"
Kamar zata fashe da kuka tace "Allah ya kaimu, Allah ya dawo dakai lfy"
"Binti karfa kiyi kuka kinji, pls kar kibari hawayenki su zuba"
Kwallar data cicciko idonta tayi kokarin maidawa, "to abbu" tafada ashagwabance,
"Yawwa binti shagwababbiya" yace da ita yana murmushi, itama maganar tasa murmushin tasakata,
Zare wayar tayi daga kunnenta tana tunanin jabir green snake ne under the green grass, saboda babu wanda zaiyi tsammanin haka yake domin shi din wani shiru shiru ne kamar ruwa sam bashida hayaniya gashi ko magana bai fiya zagewa yayiba ashe soyayya ce tsububu acikinsa,
Tunda ta kammala cin abincin ta kwanta tafara shakar bacci sai 5 ta tashi,
Wanka tayi taci kwalliya cikin riga da wando wadanda suka kamata sosai suka bayyanar da surar jikinta afili,
Part din jabir takoma ta zauna afalonsa ta dauki daya daga cikin littafin da yake koya mata tafara bitarsa, tana nan zaune har 7 tayi amma jabir shiru bai dawo ba,
8:30 tana nan a inda take azaune dif taji an dauke wuta atsorace ta tashi zata fita takoma sashenta domin acan tabaro wayarta, tana zuwa bakin kofa taji anbude kofar alamun za ashigo, babu tsammani tajita ajikin mutum, wata uwar kara tasaka mai firgitarwa,
Bakinta ya toshe da hannunsa hadida sake rungumeta acikin kirjinsa,
"Haba binti irin wannan kara haka ai sai ki kashe min dodon kunne" yarada mata acikin kunnenta, ajiyar zuciya ta saki mai karfi,kamar wacce zata yi kuka tafara magana,
"To ai abbu kaine baka yi magana ba shiyasa ban zata kai bane"
"Binti nadauka kina wajenki shiyasa ban zaci kina nan ba, amma dai ki daure ki rage tsoron nan pls"
Haske ne ya gauraye dakin sakamakon injin da aka kunna, kanta ya dago yana mai kallon jikinta ita dai ahar kullum cikin kananan kaya take,
Hannunta ya kama suka koma cikin falon,
"Binti idan mutum ya tsorata addu'a yake yi ba ihu ba kinji"
Kai ta daga masa tana kallonsa "abbu nakawo maka abinci ko? Tun safe baka kara cin abinci ba"
"To binti kawo min amma bari nayi wanka kafin ki dawo"
Cikin bedroom dinshi ya shiga ita kuma tafita zuwa sashenta.
Abincin ta hado masa ta dauko acikin dan madaidaicin kwando ta dawo sashensa, afalo ta dire kayan ta shiga cikin bedroom din daidai lokacin shikuma yafito daga bathroom daga shi sai gajeren wando ja,
Hannuwanta biyu tasaka ta rufe fuskarta gamida juya masa baya,
"Yi hakuri abbu ban san cewar baka gama ba da bazan shigo ba"
Kusa da ita yaje ya juyo da ita, "bude idonki binti, ai ya halatta ki ganni acikin ko wanne irin yanayi kamar yadda nima zan iya ganinki acikin kowanne irin hali,wanda ba muharraminki ba shine ya haramta ki gani acikin irin wannan lokacin"
Ahankali ta bude idonta amma kasa take kallo ta kasa dagowa ta kalleshi, shidai kunyarta tana burgeshi domin bata iya kallonsa indai babu kaya ajikinsa,
"Jeki dakina ki dauko abin goge kunnen to"
Da saurinta ta tashi ta garzaya ta shiga bedroom dinshi ta dauko abin goge kunnen akan mirror dinsa ta kawo masa,
Bajewa tayi ajikinsa ta dora kanta akan cinyar sa yafara goge mata kunnen ta,
Sun dade ahaka har tsawon wani lokaci kafin ta tashi taje ta kwaso masa kayan karin kumallonsa ta kawo masa inda yake zaune,
"Abbu ba yanzu zaka fitaba ko?" Ta tambayeshi tana kallon fuskarsa wadda shikuma abincin gabanshi yake kallo,
"Yanzun nan zanyi wanka in fita,meya faru?"
Matsawa tayi kusa dashi, "abbu fita zakayi ka barni? Dan Allah ka tafi dani abbu" tana gama fadin haka sai hawaye sharrrrrr!
Juyawa yayi ya kalleta, "menene abin kuka binti? Ai masallaci zanje da sai mutafi tare"
Hannunta ya kamo ya rike cikin nashi, "abbu bana son katafi ka barni"
"Kiyi hakuri binti ai idan natafi ma zan dawo kinji"
Kai ta daga tana sake makale hannunsa cikin nata,
Tana nan tare dashi har ya kammala cin abincin yaje ya dauko littafi mai tsarki yadawo kusa da ita ya zauna, kwanciya ta sake yi ajikinsa yayinda shikuma ya bude alqur'anin yafara karanta suratul kahfi domin dacewa da hasken juma'ah,
Tana jin ya kammala karatun tafara sosa saman idonta har wurin ya dan fara kumbura idon yayi ja,
"Abbu kaga wurin da wannan kunamar ta cijeni shekaran jiya har yanzu bai warkeba"
Tashi zaune tayi tana nuna masa,
"Abbu zafi, sosa min"
Babu zato taji harshensa akan wurin yana juyawa,
"Abbu...!" Hannunsa yasa ya rufe mata bakinta yaci gaba da lasar fatar idonta da harshensa,
Ya jima yana yimata haka kafin ya tsaya ya kurawa gashin kanta ido wanda yayi masa kyau ainun,
"Binti bari naje nayi wanka, fita nake son yi"
Tashi tayi daga jikinsa ta matsa gefe, cikin bedroom dinshi ya shiga yayinda ita kuma ta rakashi da ido,
Tv ta kunna ta fara kallon African magic, har jabir ya fito ya sameta, kamshine yafara ziyartar hancinta hakan ya sanyata juyawa ta kalleshi, kamar kullum komai fari yasaka tun daga yadin jikinsa har takalmin kafarsa,
"Wowww...!" Tafada cikin zuciyarta,
"Abbu kayi kyau" tafada gamida tashi ta karasa gabansa ta tsaya tana kallonsa,
Hannunsa yasa ya fara shafa wurin da ya kumbura asaman idonta,hakan ya sata lumshe idanuwanta,
Kamar daga sama taji bakinsa kan nata yana tsotsar lips dinta,
Sunfi Minti biyar ahaka sannan yasaki bakin nata ahankali,
"Binti sai nadawo ko?"
Hannunsa ta kamo idonta cikeda kwalla, "abbu zaka tafi da farin cikina zaka barmin damuwa" tafada ahankali,
Hannuwan nata shima ya riko,
"Binti kinga yau juma'a zanje nayiwa mutane huduba kuma akwai gurin da nake son zuwa kafin lokacin masallacin yayi"
Dagowa tayi ta kalleshi yayinda kwallar da ta taru a idonta ta zubo kan kumatunta,
"Abbu wurin budurwar taka zakaje?" Tayi masa tambayar da ita kanta bata san lokacin da tayiba,
Lallausan murmushi yayi yasa hannunsa duka biyu akan kumatunta yafara share mata hawayen dake kan fuskar tata,
"Ni ba wurin macema zanje ba wurin namiji ne, wani dan kasuwa ne ya shirya wani dan kwarya kwaryar wa'azi domin fadakar da yan uwansa yan kasuwa akan illar tauye mudu da cin riba"
Murmushi tayi tadafe hannayensa dake kan kumatunta,
"Me zaka tafi ka barmin wanda zan rinka yi kafin kadawo?"
"Binti kiyita yiwa annabi salati tunda kinga yau juma'ah annabi kuma yace mu yawaita yimasa salati musamman ma ranar juma'a domin salatin da muke yimasa yana zuwa gareshi shiyasa annabi yace duk wanda ya yawaita salati agareshi to ranar gobe alqiyama zai samu cetonshi, idan kuma hakan bai samuba to kiyita fadin subhanalli wabi hamdihi, subhanallahil azim, domin annabi yace kalmomine masu saukin fada akan harshe sannan masu soyuwa awurin Allah kuma masu nauyi akan sikeli ranar auna ayyukan bayi"
Wani dadi taji ya ratsata agaskiya mutum mai ilmi yanada dadin zama sannan komai nashi akan tsari yake ita ta dade da fahimtar haka,
"Abbu to karka dade pls" hannunsa ta sauke daga kumatunta tafara murza yatsunshi, hatta hannun nashi kamshin turare yake zubawa,
"Binti bari mana karki karya min alwala ta ko kin manta abinda nafada miki jiya?"
Sakin hannunshi tayi tajuya cikeda kunya,
"Yanzu abbu dan wannan abun sai ya bata maka alwala"
Tafada bayan ta juya masa baya,
"Ehh mana binti, sai nadawo kinji"
"Ka kula da kanka abbu, Allah ya dawo min dakai gida lafiya"
Ba karamin dadin addu'ar da tayi masa yaji ba,
"Nagode binti"
Fita yayi ya tafi saboda yaga idan yaci gaba da tsaiwa awurinta zai dade bai tafiba, gaban window taje ta tsaya tana kallonsa lokacin da yake kokarin shiga cikin motarsa,
Har saida taga fitarsa daga gidan sannan tabar jikin window din tashiga bedroom dinshi tafara gyarashi tanayi tana yiwa annabi salati domin kwadayin samun rabon da taji jabir yace ana samu muddin aka dimanci yiwa annabi salati musamman ma aranar juma'a.
Gyara sashen jabir tayi tatas ta fesheshi da air freshener mai dadi sannan ta kulle ta dauki kwanukan data kawo masa breakfast ta fita zuwa sashenta,
"Oh Allah Sarki abbu" tafada tana dan murmushi akan fuskarta,
Sai da ta kammala gyaran sashenta ko ina yayi tsaf tsaf sannan ta zauna zaman kallo,
Tana nan zaune taji kiran mamansu ya shigo cikin wayarta wanda har sai da taji gabanta ya fadi domin bata san abinda zata fadawa ma ba,
Dakyar ta iya dauka jikinta har wani rawa yake yi, wata uwar tsawa taji ma ta daka mata da karfi sannan cikin zafin rai tafara magana,
"Goodness kinci amanata kin saba alqawarin da kika yimin tun farko, amma kisani sai na dauki mataki akanki"
Ido goodness ta zazzaro gamida toshe bakinta da hannuwanta, shikenan yanzu ma tasan ta musulunta saura kawai ta jirayi dan karamin yakin da zai afku, ta raya hakan acikin ranta,
Cikin tsawar data fi ta farko ma tace,
"Bakya jin abinda nake fada ne? Kiyi min magana tun kafin nazo har cikin gidan ki inci mutuncinki"
"Ma am so sorry pls, wallahi ba yin kaina bane kawai *wani haske* ne ya fado cikin rayuwata,amma kiyi hakuri ma"
"Ki rufe min baki munafuka, da ai cewa kikayi zaki rinka zuwa church din duk ranar Sunday amma yanzu gashi kin daina zuwa"
Wani sanyi taji ganin har yanzu 'ma' bata san ta musulunta ba,
"Ma zanzo, banida lafiya ne shiyasa nake zuwa church din bayan gidana amma idan nawarke zan zo"
"Saura idan kin warke ki k'i zuwa"
Tana gama fadin haka ta yanke wayar, tagumi goodness tayi tana tunanin gashi yanzu akan rashin zuwa church kadai ma tana fada to inaga idan taji ta karbi addinin gaskiya, ta jima tana tunani aranta Kafin ta tashi ta shiga kitchen,
Jalop din cous cous tayi wanda yasha kayan lambu aciki in banda kamshi babu abinda ke tashi, dan kadan ta zuba ta koma falo ta zauna, wayarta ta jawo ta shiga kiran jabir,
Cikin sanyin muryarshi taji yafara yi mata magana "amincin Allah ya tabbata agareki yake wannan yarinya"
Murmushi tayi mai dan sauti "abbu ba zaka dawo gida kaci abinci ba?"
"Binti ai ban gama abinda nake yi ba, ko zan dawo gidan nan ina jin sai dare"
Kamar zata fashe da kuka tace "Allah ya kaimu, Allah ya dawo dakai lfy"
"Binti karfa kiyi kuka kinji, pls kar kibari hawayenki su zuba"
Kwallar data cicciko idonta tayi kokarin maidawa, "to abbu" tafada ashagwabance,
"Yawwa binti shagwababbiya" yace da ita yana murmushi, itama maganar tasa murmushin tasakata,
Zare wayar tayi daga kunnenta tana tunanin jabir green snake ne under the green grass, saboda babu wanda zaiyi tsammanin haka yake domin shi din wani shiru shiru ne kamar ruwa sam bashida hayaniya gashi ko magana bai fiya zagewa yayiba ashe soyayya ce tsububu acikinsa,
Tunda ta kammala cin abincin ta kwanta tafara shakar bacci sai 5 ta tashi,
Wanka tayi taci kwalliya cikin riga da wando wadanda suka kamata sosai suka bayyanar da surar jikinta afili,
Part din jabir takoma ta zauna afalonsa ta dauki daya daga cikin littafin da yake koya mata tafara bitarsa, tana nan zaune har 7 tayi amma jabir shiru bai dawo ba,
8:30 tana nan a inda take azaune dif taji an dauke wuta atsorace ta tashi zata fita takoma sashenta domin acan tabaro wayarta, tana zuwa bakin kofa taji anbude kofar alamun za ashigo, babu tsammani tajita ajikin mutum, wata uwar kara tasaka mai firgitarwa,
Bakinta ya toshe da hannunsa hadida sake rungumeta acikin kirjinsa,
"Haba binti irin wannan kara haka ai sai ki kashe min dodon kunne" yarada mata acikin kunnenta, ajiyar zuciya ta saki mai karfi,kamar wacce zata yi kuka tafara magana,
"To ai abbu kaine baka yi magana ba shiyasa ban zata kai bane"
"Binti nadauka kina wajenki shiyasa ban zaci kina nan ba, amma dai ki daure ki rage tsoron nan pls"
Haske ne ya gauraye dakin sakamakon injin da aka kunna, kanta ya dago yana mai kallon jikinta ita dai ahar kullum cikin kananan kaya take,
Hannunta ya kama suka koma cikin falon,
"Binti idan mutum ya tsorata addu'a yake yi ba ihu ba kinji"
Kai ta daga masa tana kallonsa "abbu nakawo maka abinci ko? Tun safe baka kara cin abinci ba"
"To binti kawo min amma bari nayi wanka kafin ki dawo"
Cikin bedroom dinshi ya shiga ita kuma tafita zuwa sashenta.
Abincin ta hado masa ta dauko acikin dan madaidaicin kwando ta dawo sashensa, afalo ta dire kayan ta shiga cikin bedroom din daidai lokacin shikuma yafito daga bathroom daga shi sai gajeren wando ja,
Hannuwanta biyu tasaka ta rufe fuskarta gamida juya masa baya,
"Yi hakuri abbu ban san cewar baka gama ba da bazan shigo ba"
Kusa da ita yaje ya juyo da ita, "bude idonki binti, ai ya halatta ki ganni acikin ko wanne irin yanayi kamar yadda nima zan iya ganinki acikin kowanne irin hali,wanda ba muharraminki ba shine ya haramta ki gani acikin irin wannan lokacin"
Ahankali ta bude idonta amma kasa take kallo ta kasa dagowa ta kalleshi, shidai kunyarta tana burgeshi domin bata iya kallonsa indai babu kaya ajikinsa,