← Book details Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 64

Sashe 64

Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read

"Binti duk auran da aka ginashi akarkashin koyarwar ma'aiki to haka yake kasancewa, shiyasa annabi yace maza su auri mace mai addini domin itace matar da kullum tana tsufa tana sake rike addininta, maimakon kaji tana fita daga ranka sai dai kaji tana sake shiga cikin ranka, sannan duk soyayyar da aka yita saboda Allah to tana dorewa"

Hannunshi ta matsa "nidai nayi sa'a, ina addu'a Allah yabarni dakai har lokacin da zan koma gareshi"

"Kizo muje mu kula da junanmu kidaina yi min maganar rabuwa"

Yace da ita gamida daukarta zuwa special room.

*ALHAMDULILLAH*

Anan nakawo karshen littafin wani haske ina addu'ar Allah yatara mu acikin ladan ya yafe mana kuskuren dake ciki, duk wacce ta karanta wani haske taji dadinshi to ta taimaka tayiwa ummi A'isha addu'a akan Allah ya biya mata bukatarta.

*SADAUKARWA*

Na sadaukar da wani haske gareki kawata *BAHIJJA BEBEELO* (marubuciyar D'a na kowane) dake da dukkan masoyan littafin wani haske, Allah ya raya miki yarinyarki iman, nagode kwarai da kaunarki agareni.

*TUKWICI NE*
agareki bestyna *PHERTYMAH XARAH* (marubuciyar littafin matar sadiq),Allah yakara dankon zumunci agaremu.

*DOMINKU NE*
Masoyana masu yi min fatan alkairi akoda yaushe.

*JINJINA GAREKI*

Uwar dakina *HAUWA M JABO* nagode da kulawarki.

*KINA RAINA*
Aminiyata mai share min kukana *CWT KAUSAR LUV*, hakika kinfi karfin kawa agareni, ke ta dabance awurina ina kaunarki kawata, Allah yabarmu tare,tabbas banda kamarki.

*FATAN ALKHAIRI*
Gareki tawan kawata *KHADIJA SIDI* nayaba miki sosai hakika ke ta musamman ce agareni.

Gaisuwa ta musamman gareku masoya yan uwana marubuta, ina addu'ar Allah ya kara muku basira da hazaka, yaci gaba da taimakonku acikin al'amuranku, ya kara muku baiwa mai amfani,ya baku lada aduk inda kuka yi daidai, ya yafe muku a inda kuka yi kuskure.

Gaisuwa mai dunbin yawa gareku masoya wadanda suke karanta rubutuna suna yimin fatan alkairi akoda yaushe, nagode muku sosai ina kaunarku mutuka kuma ina addu'ar Allah yabar zumuncin dake tsakaninmu, duk wanda yake kaunar ummi A'isha ko kuma yake kaunar rubutunta ko yaji tana burgeshi ko yaji yana sonta to UMMI A'ISHA loves you too, sai mun hadu acikin labari nagaba da yardar mai sama Rabbi Azimu.

DOCUMENT MADE BY SALMARH
Chapter 64 · 0% Book details