Sashe 55
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Magiya tasaka masa, dan kadan ya zuba mata suka fara cin alalen tare, kullum haka yake biye mata yaci abinda ta girka na kwadayi ita kanta tasan jabir namiji ne wanda yasan hakkin mace domin tunda ta samu cikin nan ta daina dafa abinci kullum sai kayan kwadayi daga wainar fulawa sai dan malele, alala, dambu, dan wake da sauransu amma bai taba kin cin abinda ta girka ba, ko kuma yin korafi, sam bai taba yiba.
Yammacine na ranar litinin tana zaune afalon jabir tana shan kafi kaza wanda yasha kifi da albasa tsabar kwadayi ma harda attaruhu tasa asuyar, tasha kwalliya sosai cikin leshi ja da adon baki ajiki,
Jabir ne ya turo kofa ya shigo bakinsa dauke da sallama,
Inda take ya karaso yana kallonta hadida aika mata da wani zazzafan sako ta cikin kwayar idonsa,
"Binti me kikesha ne haka?" Ya tambayeta bayan ya kamo hannunta,
"Abbu kafi tsire ne"
"Binti bakya tsoron yasaki gudawa? Wannan abun ai daga ganinsa zai batawa mutum cikinsa ko ba kuli kuli bane?"
"Abbu shine amma fa da dadi sha kaji"
Hannunta ya saki ya mike yana girgiza kansa "haba binti nikuwa yaushe zansha wannan abun? Kema dan akwai daliline"
Dakinshi ya wuce yana jiyota tana cewa "wallahi abbu akwai dadi saboda har wani zaki zakin maggi yake yi"
Murmushi yayi ya wucewarsa cikin daki, minti kadan ya fara kwalla mata kira cikin sanyayyiyar muryarshi, sanin bazata jiyoshi ba yasashi tashi ya leka falon, har yanzu tana zaune inda ya barta tana shan kafi kazarta,
"Binti zo"
Mikewa tayi ta tashi sai kuma taji wani irin ciwo ya murde mata cikinta da mararta,
Rike cikin tayi tana salati "wash abbu" shine kawai abinda ta iya fada jini yafara bin kafarta.
_Masu karatu kuyi min afuwa naso kammala book dinnan awannan shafin amma hakan bai samu ba, gaisuwa mai tarin yawa gareki khadija magaji bk da dukkan masoyan wani haske_
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[10/22, 9:21 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_121-125_
~~~Durkushewa tayi awurin tana rike da cikinta yayinda jini yake gudu ajikinta yana bin kafarta kamar an bude fanfo,
Da sauri jabir ya karaso inda take yana tambayarta,
"Binti menene? Me ya sameki?" Sai alokacin idonshi yakai kan jinin da yake bin kafafunta,
"Innalillahi" yafada arazane, dasauri ya saketa ya nufi dakinsa domin dauko rigarsa, yana tafiya yana saka rigar ko hula bai tsaya dauka ba, hijabinta daya hango akan kujera ya dauko ko saka mata baiyi ba ya dauketa irin daukar da ake yiwa jarirai,
Yana dauke da ita ya nufi tsakar gida da ita, kamashi tayi ta rikeshi gam numfashinta yana kai kawo yana fita dakyar,
Tunda mai gadi ya hangoshi ya tabbatar babu lafiya dan haka yayi maza ya fara kwalawa mal idi driver kira, shima a sukwane ya zaburo yazo ya shiga motar ya figesu mai gadi ya hangame musu gate suka fita,
_Nasara clinic_ shine asibitin da suka nufa, har lokacin bahijja murkususu take yi ajikin jabir tana sake kankameshi abin gwanin ban tausayi,
Suna zuwa asibitin jabir ya sake daukarta ya nufi ciki da ita yana shiga wata nurse ta garo gadon da ake saka marassa lafiya ya dorata akai aka garata suka doshi wani daki _(antenatal)_ ,jabir binsu kawai yake yi yana yiwa bahijja addu'a acikin zuciyarsa, dole a waje ya tsaya aka shiga da bahijja cikin dakin.
Yana nan tsaye yana kai komo awurin yama rasa abinyi kwata kwata shi kawai ta lafiyar bintinshi yake yi domin bai san acikin wanne hali take ba ahalin yanzu,
Wurin minti talatin yana tsaye a inda yake wani kyakkyawan likita ya fito dan gayu dashi mai mutukar kyau da iyayi (saurayin adda Benazir), hannu ya bashi suka gaisa kafin yajashi zuwa cikin office dinshi yana goge gumin dake fita ajikin goshinsa,
Bayan sun zauna ne dr din ya dubi jabir cikeda damuwa akan fuskarsa yafara jawabi kamar haka,
"Dafarko dai ranka ya dade ina mai baka hakuri sakamakon munyi iya kokarinmu na ganin mun ceto ranta da lafiyar abinda ke cikinta amma unfortunately abin ya gagara...!"
Kallonsa jabir yayi wanda idanuwanshi suka sauya kala daga fari zuwa ja,
"Dr ban fahimci abinda kake nufi ba"
"Abinda nake nufi anan shine madam dinka ta samu miscarriage, tarasa cikin dake jikinta"
Cikin damuwa jabir yadafe kumatunsa da hannunsa guda daya acikin ranshi yana karanta addu'a domin samun sassauci,
"To dr menene musabbabin faruwar hakan, menene ya haifar da hakan?"
Wadannan sune jerin tambayoyin da jabir ya jerowa likitan alokaci guda,
"Ehh to gaskiya shine abinda muka kasa fahimta, har yanzu bamu gano abinda ya haddasa mata wannan miscarriage dinba saboda ahalin yanzu ta lafiyarta muke yi sannan kuma kasancewar ta zubar da jini da yawa to tana bukatar akara mata jini, da ruwa"
"Shikenan dr, thank you"
Tashi jabir yayi yana mika masa hannu domin yin musabaha, fita yayi ya tafi wurin mal idi driver suka koma gida ya dauko kudin da za ayi amfani dashi domin da saboda tsabar rudewa ko kudin ma bai samu ya dauko ba,
Asibitin suka dawo alokacin har ansamo jinin da yayi daidai dana bahijja ana kara mata, wata takarda aka bashi wacce ke dauke da jeren magungunan da ake bukata hakan yasashi nufar pharmacy domin siyo duk magunan da ake bukata,
Yana waje yana jira bai samu ganinta ba har mangaruba tayi, salla yaje yayi ya dawo yana zuwa ya samu dr din yana fitowa daga dakin da bahijja take anan yake sanar dashi cewar zai iya shiga ya ganta,
Jiki asanyaye jabir yasaka kai ya shiga cikin dakin, hangota yayi kwance hannunta daya makale da abin karin ruwa ana kara mata, dayan hannun kuma ta dafe cikinta dashi daga gani kuka take yi,
Gefen gadon ya karasa ya zauna akusa da ita yakai hannunshi kan goshinta yana shafawa,
"Binti na sannu..!"
Bude idonta tayi hawaye yana sauka daga idanuwan nata ta kalleshi,
"Abbu shikenan cikin ya zube ko?"
Duk da yana cikin damuwar shima amma sai da yayi murmushin karfin hali yaci gaba da shafa goshinta zuwa gashin kanta,
"Babu komai binti kar ki damu, wannan wata jarrabawa ce daga wurin Allah, watakila samun babyn ayanzu bashine alkairi agaremu ba shiyasa Allah ya hanamu ya kwace abunshi cikin sauki"
Idonta ta runtse wasu hawayen suna gudu akan kumatunta,
"Abbu yanzu shikenan na rasa wannan cikin? Wannan wacce irin...!"
Sauri yayi ya rufe mata baki da hannunshi,
"Haba binti ita jarrabawa akan mumuni ai tazama wajibi, mutum indai mai imani ne Allah baya taba barinsa kara zube domin Allah cewa yayi _"'Ashe mutane sunyi zaton abarsu suce munyi imani alhalin ba za a jarrabesu ba? Kuma lalle mun jarrabi wadanda ke gabaninsu domin lalle Allah yasan wadanda sukayi gaskiya kuma lallai yasan makaryata"' (suratul ankabut aya ta 3)_ dan haka wannan abun jarrabace daga wurin Allah binti, mutukar kayi imani to dolene sai Allah ya jarrabeka shiyasa acikin suratul bakara sura ta biyu aya ta _155-157_ Allah subhanahu wata'ala yake cewa:
_Kuma lalle ne muna jarrabarku da wani abu guda daga tsoro, da yunwa da nakasa daga dukiya da rayuka da 'yayan itace, kuma kayi bushara ga masu hakuri, wadanda suke idan wata masifa ta samesu sai suce lalle ne mu ga Allah muke kuma lalle ne mu zuwa gareshi masu komawa ne, Allah yace wadannan akwai albarku akansu daga ubangijinsu da wata rahama kuma wadannan sune shiryayyu"'_
Kinga bai kamata ki rinka irin wadannan maganganun ba, addu'a ya kamata kiyi domin shi lamarin mumini akwai abin sha'awa da ban mamaki inji annabi Muhammad acikin wani hadisi haka yafada yace saboda idan wata musifa ta samu mumini sai yayi hakuri ya dogara ga Allah sai Allah ya canja masa da abinda yafi zama alkairi agareshi, idan kuma wani abin farin ciki ya sameshi sai yayi farin ciki ya godewa Allah hakan sai ya sake zama alkairi agareshi, hakika babu mai samun irin wannan garabasar face mumini"
Hannun jabir ta riko da dayan hannunta wanda bashine wanda ake yi mata karin ruwan ba, "abbu nahakura, wallahi nahakura, Allah ya bani ladan jarrabawar da yayi min, Allah yasa hakan shine yafi zama alkairi agareni, agareka da kuma rayuwarmu gaba daya"
Kissing din goshinta yayi yana murmushi "amin binti,haka ya kamata dukkan musulmi ya zama wurin rungumar kaddarar da ubangiji ya aiko masa da ita"
"Abbu marata tana yimin ciwo ga wani irin fitsari da nakeji"
Kanta ya shafa yana yi mata sannu, ya dade azaune awurinta har sai da yaga bacci yayi awon gaba da ita sannan ya tashi ya fita,abincin da zata ci yaje ya samo mata da sauran tarkace irin wanda marar lafiya zai nema.
Kwananta uku a asibitin jabir yana kulawa da ita amma koda wasa bai fadawa kowa abinda ya faru ba, hatta gidansu bai sanar musu ba, haka itama gidansu bai fada ba, Ummu al'amin kuwa kusan kullum sai sunyi waya amma bai taba sanar da ita rashin lafiyar ba,
Yanzu taji sauki sosai ta dawo normal bayan likitoci sunyi mata wankin ciki, ganin ta warware taji sauki yasa aka sallamesu zuwa gida amma har lokacin basu san makasudin zubewar cikin ba shi dama jabir baya son yawan bincike domin yasan koma menene dai to Allah ne ya shiryo faruwar hakan.
Suna komawa gida ta shiga aikace aikace kasancewar jikinta ya warware sosai,
Tana kitchen tana goge goge jabir ya shigo daga shi sai wando baki iya gwiwarsa da farar t shirt mai gajeren hannu,
"Binti sarkin aiki, daga dawowa kuma sai afara da aiki?"
"To abbu idan nabari waye zai yimin?"
Ta bayanta yaje ya shiga jikinta ya rungumeta,
"Kibari anjima zan tayaki kiyi,amma yanzu kizo muje in nuna miki wani abu"
Make kafada tayi tana murmushi
"nidai abbu basai ka nuna min ba,Allah nasan wayo zaka yimin" ta karasa maganar cikeda shagwaba,
"Binti bakya son babyn ne? Naga harda kuka kikayi lokacin da wancan cikin ya zube, ko bakya son kiyiwa al'amin kani?"
"Gaskiya nidai abbu, nidai, nidai....!"
Juyo da ita yayi ya dauketa akafadarshi ya fita da ita yana kwaiwayonta,
"Nidai, nidai, nidai binti" dariya tafara kyakyatawa batare da ta shirya ba.
Yammacine na ranar litinin tana zaune afalon jabir tana shan kafi kaza wanda yasha kifi da albasa tsabar kwadayi ma harda attaruhu tasa asuyar, tasha kwalliya sosai cikin leshi ja da adon baki ajiki,
Jabir ne ya turo kofa ya shigo bakinsa dauke da sallama,
Inda take ya karaso yana kallonta hadida aika mata da wani zazzafan sako ta cikin kwayar idonsa,
"Binti me kikesha ne haka?" Ya tambayeta bayan ya kamo hannunta,
"Abbu kafi tsire ne"
"Binti bakya tsoron yasaki gudawa? Wannan abun ai daga ganinsa zai batawa mutum cikinsa ko ba kuli kuli bane?"
"Abbu shine amma fa da dadi sha kaji"
Hannunta ya saki ya mike yana girgiza kansa "haba binti nikuwa yaushe zansha wannan abun? Kema dan akwai daliline"
Dakinshi ya wuce yana jiyota tana cewa "wallahi abbu akwai dadi saboda har wani zaki zakin maggi yake yi"
Murmushi yayi ya wucewarsa cikin daki, minti kadan ya fara kwalla mata kira cikin sanyayyiyar muryarshi, sanin bazata jiyoshi ba yasashi tashi ya leka falon, har yanzu tana zaune inda ya barta tana shan kafi kazarta,
"Binti zo"
Mikewa tayi ta tashi sai kuma taji wani irin ciwo ya murde mata cikinta da mararta,
Rike cikin tayi tana salati "wash abbu" shine kawai abinda ta iya fada jini yafara bin kafarta.
_Masu karatu kuyi min afuwa naso kammala book dinnan awannan shafin amma hakan bai samu ba, gaisuwa mai tarin yawa gareki khadija magaji bk da dukkan masoyan wani haske_
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[10/22, 9:21 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_121-125_
~~~Durkushewa tayi awurin tana rike da cikinta yayinda jini yake gudu ajikinta yana bin kafarta kamar an bude fanfo,
Da sauri jabir ya karaso inda take yana tambayarta,
"Binti menene? Me ya sameki?" Sai alokacin idonshi yakai kan jinin da yake bin kafafunta,
"Innalillahi" yafada arazane, dasauri ya saketa ya nufi dakinsa domin dauko rigarsa, yana tafiya yana saka rigar ko hula bai tsaya dauka ba, hijabinta daya hango akan kujera ya dauko ko saka mata baiyi ba ya dauketa irin daukar da ake yiwa jarirai,
Yana dauke da ita ya nufi tsakar gida da ita, kamashi tayi ta rikeshi gam numfashinta yana kai kawo yana fita dakyar,
Tunda mai gadi ya hangoshi ya tabbatar babu lafiya dan haka yayi maza ya fara kwalawa mal idi driver kira, shima a sukwane ya zaburo yazo ya shiga motar ya figesu mai gadi ya hangame musu gate suka fita,
_Nasara clinic_ shine asibitin da suka nufa, har lokacin bahijja murkususu take yi ajikin jabir tana sake kankameshi abin gwanin ban tausayi,
Suna zuwa asibitin jabir ya sake daukarta ya nufi ciki da ita yana shiga wata nurse ta garo gadon da ake saka marassa lafiya ya dorata akai aka garata suka doshi wani daki _(antenatal)_ ,jabir binsu kawai yake yi yana yiwa bahijja addu'a acikin zuciyarsa, dole a waje ya tsaya aka shiga da bahijja cikin dakin.
Yana nan tsaye yana kai komo awurin yama rasa abinyi kwata kwata shi kawai ta lafiyar bintinshi yake yi domin bai san acikin wanne hali take ba ahalin yanzu,
Wurin minti talatin yana tsaye a inda yake wani kyakkyawan likita ya fito dan gayu dashi mai mutukar kyau da iyayi (saurayin adda Benazir), hannu ya bashi suka gaisa kafin yajashi zuwa cikin office dinshi yana goge gumin dake fita ajikin goshinsa,
Bayan sun zauna ne dr din ya dubi jabir cikeda damuwa akan fuskarsa yafara jawabi kamar haka,
"Dafarko dai ranka ya dade ina mai baka hakuri sakamakon munyi iya kokarinmu na ganin mun ceto ranta da lafiyar abinda ke cikinta amma unfortunately abin ya gagara...!"
Kallonsa jabir yayi wanda idanuwanshi suka sauya kala daga fari zuwa ja,
"Dr ban fahimci abinda kake nufi ba"
"Abinda nake nufi anan shine madam dinka ta samu miscarriage, tarasa cikin dake jikinta"
Cikin damuwa jabir yadafe kumatunsa da hannunsa guda daya acikin ranshi yana karanta addu'a domin samun sassauci,
"To dr menene musabbabin faruwar hakan, menene ya haifar da hakan?"
Wadannan sune jerin tambayoyin da jabir ya jerowa likitan alokaci guda,
"Ehh to gaskiya shine abinda muka kasa fahimta, har yanzu bamu gano abinda ya haddasa mata wannan miscarriage dinba saboda ahalin yanzu ta lafiyarta muke yi sannan kuma kasancewar ta zubar da jini da yawa to tana bukatar akara mata jini, da ruwa"
"Shikenan dr, thank you"
Tashi jabir yayi yana mika masa hannu domin yin musabaha, fita yayi ya tafi wurin mal idi driver suka koma gida ya dauko kudin da za ayi amfani dashi domin da saboda tsabar rudewa ko kudin ma bai samu ya dauko ba,
Asibitin suka dawo alokacin har ansamo jinin da yayi daidai dana bahijja ana kara mata, wata takarda aka bashi wacce ke dauke da jeren magungunan da ake bukata hakan yasashi nufar pharmacy domin siyo duk magunan da ake bukata,
Yana waje yana jira bai samu ganinta ba har mangaruba tayi, salla yaje yayi ya dawo yana zuwa ya samu dr din yana fitowa daga dakin da bahijja take anan yake sanar dashi cewar zai iya shiga ya ganta,
Jiki asanyaye jabir yasaka kai ya shiga cikin dakin, hangota yayi kwance hannunta daya makale da abin karin ruwa ana kara mata, dayan hannun kuma ta dafe cikinta dashi daga gani kuka take yi,
Gefen gadon ya karasa ya zauna akusa da ita yakai hannunshi kan goshinta yana shafawa,
"Binti na sannu..!"
Bude idonta tayi hawaye yana sauka daga idanuwan nata ta kalleshi,
"Abbu shikenan cikin ya zube ko?"
Duk da yana cikin damuwar shima amma sai da yayi murmushin karfin hali yaci gaba da shafa goshinta zuwa gashin kanta,
"Babu komai binti kar ki damu, wannan wata jarrabawa ce daga wurin Allah, watakila samun babyn ayanzu bashine alkairi agaremu ba shiyasa Allah ya hanamu ya kwace abunshi cikin sauki"
Idonta ta runtse wasu hawayen suna gudu akan kumatunta,
"Abbu yanzu shikenan na rasa wannan cikin? Wannan wacce irin...!"
Sauri yayi ya rufe mata baki da hannunshi,
"Haba binti ita jarrabawa akan mumuni ai tazama wajibi, mutum indai mai imani ne Allah baya taba barinsa kara zube domin Allah cewa yayi _"'Ashe mutane sunyi zaton abarsu suce munyi imani alhalin ba za a jarrabesu ba? Kuma lalle mun jarrabi wadanda ke gabaninsu domin lalle Allah yasan wadanda sukayi gaskiya kuma lallai yasan makaryata"' (suratul ankabut aya ta 3)_ dan haka wannan abun jarrabace daga wurin Allah binti, mutukar kayi imani to dolene sai Allah ya jarrabeka shiyasa acikin suratul bakara sura ta biyu aya ta _155-157_ Allah subhanahu wata'ala yake cewa:
_Kuma lalle ne muna jarrabarku da wani abu guda daga tsoro, da yunwa da nakasa daga dukiya da rayuka da 'yayan itace, kuma kayi bushara ga masu hakuri, wadanda suke idan wata masifa ta samesu sai suce lalle ne mu ga Allah muke kuma lalle ne mu zuwa gareshi masu komawa ne, Allah yace wadannan akwai albarku akansu daga ubangijinsu da wata rahama kuma wadannan sune shiryayyu"'_
Kinga bai kamata ki rinka irin wadannan maganganun ba, addu'a ya kamata kiyi domin shi lamarin mumini akwai abin sha'awa da ban mamaki inji annabi Muhammad acikin wani hadisi haka yafada yace saboda idan wata musifa ta samu mumini sai yayi hakuri ya dogara ga Allah sai Allah ya canja masa da abinda yafi zama alkairi agareshi, idan kuma wani abin farin ciki ya sameshi sai yayi farin ciki ya godewa Allah hakan sai ya sake zama alkairi agareshi, hakika babu mai samun irin wannan garabasar face mumini"
Hannun jabir ta riko da dayan hannunta wanda bashine wanda ake yi mata karin ruwan ba, "abbu nahakura, wallahi nahakura, Allah ya bani ladan jarrabawar da yayi min, Allah yasa hakan shine yafi zama alkairi agareni, agareka da kuma rayuwarmu gaba daya"
Kissing din goshinta yayi yana murmushi "amin binti,haka ya kamata dukkan musulmi ya zama wurin rungumar kaddarar da ubangiji ya aiko masa da ita"
"Abbu marata tana yimin ciwo ga wani irin fitsari da nakeji"
Kanta ya shafa yana yi mata sannu, ya dade azaune awurinta har sai da yaga bacci yayi awon gaba da ita sannan ya tashi ya fita,abincin da zata ci yaje ya samo mata da sauran tarkace irin wanda marar lafiya zai nema.
Kwananta uku a asibitin jabir yana kulawa da ita amma koda wasa bai fadawa kowa abinda ya faru ba, hatta gidansu bai sanar musu ba, haka itama gidansu bai fada ba, Ummu al'amin kuwa kusan kullum sai sunyi waya amma bai taba sanar da ita rashin lafiyar ba,
Yanzu taji sauki sosai ta dawo normal bayan likitoci sunyi mata wankin ciki, ganin ta warware taji sauki yasa aka sallamesu zuwa gida amma har lokacin basu san makasudin zubewar cikin ba shi dama jabir baya son yawan bincike domin yasan koma menene dai to Allah ne ya shiryo faruwar hakan.
Suna komawa gida ta shiga aikace aikace kasancewar jikinta ya warware sosai,
Tana kitchen tana goge goge jabir ya shigo daga shi sai wando baki iya gwiwarsa da farar t shirt mai gajeren hannu,
"Binti sarkin aiki, daga dawowa kuma sai afara da aiki?"
"To abbu idan nabari waye zai yimin?"
Ta bayanta yaje ya shiga jikinta ya rungumeta,
"Kibari anjima zan tayaki kiyi,amma yanzu kizo muje in nuna miki wani abu"
Make kafada tayi tana murmushi
"nidai abbu basai ka nuna min ba,Allah nasan wayo zaka yimin" ta karasa maganar cikeda shagwaba,
"Binti bakya son babyn ne? Naga harda kuka kikayi lokacin da wancan cikin ya zube, ko bakya son kiyiwa al'amin kani?"
"Gaskiya nidai abbu, nidai, nidai....!"
Juyo da ita yayi ya dauketa akafadarshi ya fita da ita yana kwaiwayonta,
"Nidai, nidai, nidai binti" dariya tafara kyakyatawa batare da ta shirya ba.