← Book details Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 64

Sashe 34

Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Agaida al'amin" tana gama fadin haka ta kashe wayar gabaki daya cikeda kishi, abin dariya ya bawa jabir,

Motsin da yaji abayansa ne yasashi juyawa nan yaga Ummu tsaye tana rikeda labulen dakin, tana kallonshi da alama duk taji hirar da suka yi da binti.

_Masu karatu sai mun hadu ashafi nagaba (shafin soyayya)._

_*Ummi Shatu*_👌🏻
[10/24, 5:26 PM] Manshat: [9/29, 9:02 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE..!*

_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_

_86-90_

~~~Jiyowa yayi yana kallon ummu al'amin,

"Har kin tashi daga baccin?"

"Wallahi kuwa amma yanzu zan koma, naji kana waya da antyn al'amin"

"Ehhh nida itane, yau rikici take ji, da alama yarintar ta motsa" ya fada yana murmushi,

"Yarinta?" Ta tambayeshi,

"Ehh mana, ai dan bakiga shirmen da tai tayi bane itada al'amin lokacin da yana can"

Murmushi tayi ta juya ta koma cikin dakin, tashi shima yayi yabi bayanta.

Kishi fal dankare acikin kirjin goodness tunanin jabir kawai take yi da tuno kyakkyawar surarsa mai daukar hankali, gaba daya hankalinta ya gama tashi gani take kamar dagaske auren zai sake yi,

Wayarta ta sake kunnawa ta fara kiransa, yana kwance ajikin ummu ya daga wayar,

"Binti" shine kawai abinda yace,

Cikeda shagwaba tafara magana "abbu dagaske kake yi?" Ta tambayeshi wanda ita kanta bata san lokacin data yi tambayar ba,

"Wai me?" Shima ya tambayeta, tashi yayi daga kusa da Ummu ya koma falo,

"Abbu wai meyasa kake cemin katuwa ne?" Tafada ashagwabance, jin shagwabar da take yi masa yake har cikin ransa,

"Ke katuwa ce mana,ko baki sani ba?"

"Abbu nidai ka fada min idan dagaske kake yi"

"Wai menene dagaske"

"Ta ukun da kace zaka yi"

Dariya ce taso subuce masa jin maganarta, gashi duk tabi ta damu bata san shi da wasa yake yi mata ba,

"Dagaske mana, bayan itama zan sake aurar wata kinga hudu kenan"

Kirji ta dafe da karfi, sai kuma ta kashe wayar kit ta ajiyeta agefe, tunani tafara tana dafe kuncinta, kishine tsababa acikin ranta,

Wayar ta sake dauka ta kirashi,

"Yau ba zaki barni inyi bacci bane?" Ya fada lokacin da ya daga wayar,

"Abbu yanzu nida Anty bamu isheka ba har sai ka sake wani auren?"

Tafada tamkar zata fashe da kuka, har sai da yaji mamakinta aranshi yana tunanin kishi irin nata,amma burgeshi shagwabarta take yi,

"Ehhh" yafada kansa tsaye yana dan nazarinta,

"To a ina take?"

"Tana Nigeria ki bari idan nadawo zaki rakani wurinta"

Ranta taji yayi bakikkirin amma ta daure tace,

"Yaushe zaka dawon?"

"Acikin next week zan dawo"

"Allah ya kaimu, agaida ummu al'amin"

Wayar ta katse bata jira amsarshi ba, ruf da ciki tayi akan doguwar kujerar shi, kishine kawai ke dawainiya da ita,

"Mtsssss me za ayi da auren mai mata yanzun ma tasan yana can tare da matarsa ita kuma gashi tun zuwanta gidan babu abinda ya taba hadasu"

Tafada acikin ranta, haka ta zauna ta bata lokaci da yawa tana cikin yanayi na bacin rai,

Lokacin da taje bacci ma ta dade bata yi baccin ba juyi kawai take tana tunanin jabir, pillow taja ta rungume tana tuno mijinta abin sonta.

*

Tunda satin da jabir zai dawo ya kama tafara shirin tarbarsa, kullum sai ta shirya masa kayan dadi amma shiru sai taji babu alamunsa, yauma sai da tayi masa girki tayi kwalliya sosai amma har 9 shiru,

Wayarshi ta kira yana dauka ta fara kukan shagwaba,

"Abbu bazan sake yi maka girki ba har sai ka dawo, kullum sai nayi sai kaki dawowa"

Sai da tsikar jikin jabir ta tashi saboda yanda take masa wannan kukan shagwabar,

"Binti dama ai cemiki nayi acikin satin nan ban fada miki date dinba, kidaina wahalar da kanki, ki bari kawai duk ranar da nadawo sai kiyi min girkin ina gidan, kinji?"

"Nidai abbu ban yarda ba ka fada min" ta sake fada cikin shagwaba,

"To ai kinga saura 3 days week din ya kare, dan haka may be gobe zan dawo ko jibi ko...."

"No abbu nidai ban yarda ba ka fadamin Allah"

Lumshe idanunshi yayi acikin ranshi yana cewa "yarinyar nan tana son tayar min da hankali fa" amma afili sai yace,

"Kwana uku ne fa kawai binti ai kinga nabaki satar amsa"

"Ok to nadauki jibin, gobe bazan yi maka girkin ba, sai jibi, idan ranar ma baka dawowa shikenan ko ranar da zaka dawo bazan yi maka ba"

Duk wadannan maganganun cikin kukan shagwaba tayi su,

"Haka kika tsara?"

"Ehh abbu" tasake fada cikin sigar farko, ita kanta wani iri takeji ajikinta bare kuma jabir wanda ko kwakkwaran motsi ya kasa,

"Ohhhhh abbu my cooking, girkina ya fara konewa, bye bye" wayar ta katse ta ruga kitchen da gudu inda take dafa indomie guda daya tal dan shegen kwadayi,

Bin wayar jabir yayi da kallo yana murmushi tareda tuno shiririta irin ta goodness.

Aranar da zai dawo wani boutique ya shiga ya kwaso mata english wears hadaddu _(sexy dress)_ masu kyau da aji domin yasan bata saka atamfa ko shadda kullum cikin kananan kaya take,

Wasu kyawawan braziers yagani amma yana tantamar ko zasu yi mata daidai kuwa saboda yaga ita din bata wasa bace, braziers din sunyi masa kyau sosai domin masu daukar hankaline, diba kawai yayi aranshi yana tunanin idan sunyi mata kadan tasan yadda zata yi dasu,

Akwati guda ya ciko mata da kananan kaya bayan shima ya lodi nashi, gida ya koma inda ummu ke jiranshi ita da al'amin duk tabi ta damu saboda tafiyar da zaiyi ya barta,

Hannunta ya kama ya kwantar da kanta agefen kafadarshi al'amin kuma yana kan cinyarshi,

"Haba Ummu menene abin damuwa ne?"

"Abu al'amin dan Allah kadawo hajji, zamu yi kewarka nida al'amin"

Murmushi jabir yayi "ummu ba lallai ne nazo aikin hajji ba saboda wasu dalilai masu yawa, kiyi hakuri idan sabuwar shekara ta kama zan turo muku kudi sai kuzo gida"

"Yawwa abu al'amin Allah ya saka da alkairi, Allah ya kaika lfy"

Ya dade tare dasu yana rarrashinsu kafin yayi wanka Ya shirya suka rakashi har airport, wani kwalin chocolate al'amin ya bashi wai ya kaiwa goodness, murmushi jabir yayi,

"Ohh Al'amin ka rasa abinda zaka bawa antyn naka sai chocolate?"

"Abbu anty mayyar chocolate ce wani lokacin ko abinci bata ci sai dai tai ta shan chocolate"

"To shikenan al'amin zan kai mata"

Sallama yayi musu ya shige cikin jirgi, Ummu harda yar kwallar ta yayinda al'amin keta daga masa hannu, suna nan tsaye har jirginsu ya tashi,sai da suka ga tafiyarsa sannan suka koma Gida.

K'arfe uku na yamma jirginsu ya sauka yayiwa driver waya yaje ya daukoshi,

Tana falonshi ta baje akasan carpet tana bacci daga ita sai yar body hug dinta baka da short trouser milk colour, dama tana hutun salla,

Yana saka kansa cikin falon ya hangota, idonsa ya sauke akan lukuta lukutan cinyoyinta wadanda suke afili domin wandon data saka iya rabin cinyoyinta ya iya rufewa,

"Masha Allah"shine kawai abinda ya iya fada bayan ya lashi lips dinsa,

Ciki ya karasa ya tsaya akanta yana karewa halittarta kallo kamar yau ya soma ganinta,

Babu zato tayi wani juyi tare da wata mika nan rigar jikinta tayi sama cikinta ya bayyana,

"La ilaha ilallah, muhammadur rasulillah"

Shine abinda yaji ta fada, ahankali ta soma bude idonta, shidai jabir mutuwar tsaye yayi saboda jin abinda ta fada,

"Lahh abbu yaushe ka dawo?" Tafada tana kokarin tashi zaune,

Kan kujera ya karasa ya zauna yana kallonta,

"Yanzu shigowata kenan yar lukuta"

Bakinshi ta kalla ta hadiyi yawu ita dai aduniya tana son bakin nan na jabir, duk ranar data kamashi babu sauki ta ayyana hakan acikin ranta,

"Sannu da zuwa, bari naje nayi maka girki abbu" tashi tayi tana sake yin wata mikar ta fita, kitchen ta shiga duk tana cike da murnar ganinsa jinta take kamar anyi mata albishir da gidan aljanna,

Kasancewar tanada kayan amfaninta wanda zata bukata yasata dora jalop din shinkafa da kayan lambu, sai murna take har ta yanke hannunta wurin yanka cabbage,

Tana kokarin yanda zata yiwa yatsan nata jabir ya shigo cikin kitchen din,

"Yankewa kika yi?"

Boye hannun tayi ta bayanta ta jiyo tana kallonshi, bata son ya gani saboda kar yace sai ya saka mata hydrogen,

"No abbu" tafada tana raurau da idanuwanta,

"Ya salam" yafada acikin ranshi,

"Bani to ingani, bazan saka miki hydrogen ba Allah"

Fito da hannun tayi ta mika masa, rike hannun yayi ya fito da ita zuwa falonta, dan kyalle ya samu ya daure mata wurin ita dai tana daga tsaye tana kallonshi yana sanye da jallabiya ruwan kasa kansa babu hula amma ba karamin kyau yayi mata ba ahakan,

Kitchen ta koma ta ci gaba da girkin da take yi shikuma jabir ya fita zuwa masallaci domin lokacin sallar la'asar yayi,

Bayan ta sauke girkin sai da ta hada lemon kwakwarta kamar yadda ta saba amma na yau harda jabir tayi shi,

Wanka ta shiga tayi ta fito daure da towel sai ga jabir ya shigo sashen nata,

Dan doddoka kafafunta akasa tafara yi tana rike towel din jikinta,

"Abbu bana salla kabani pad"

Dama can ai ba sallar kike yi ba ya fadi hakan aranshi amma afili cewa yayi,

"Ke wai kullum acikin jini kike ne? Koda yaushe jini,koda yaushe jini sai kace wata marar lafiya"

Farr tayi da idanuwanta tana matse cinyoyinta gudun kar tayi staining,

"Abbu lafiyata k'alau, ni sau biyu nake yi awata"

Tab nashiga uku kenan, yafada aranshi danma shi ba mai yawan bukata bane, sai yayi wata bai bukaci mace ba wani lokacin ma zai iya yin fiyeda haka,

Kallonta yayi sai ya hango jinin yana bin cinyoyinta,

"Ina zuwa bari na kawo miki" juyawa yayi ya fita, yana fita ta fashe da dariya dama tana sane tayi masa haka saboda tun lokacin da yayi mata maganar wannan ta ukun da yace zai aura ta daura aniyar haukatashi da salonta kala kala wadanda anty Bilkisu ta koyar da ita,

Tana nan a inda yabarta har ya dawo yana rike da pad din guda biyu,

"Gashi,amma haka wannan abin yake yi miki rushing?"

"Ehhh abbu amma zuwa kwana ukune, yana yin kwana uku zai daina"
Chapter 34 · 0% Book details