Sashe 44
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ta daga masa sannan ahankali tace "adawo lafiya abbu".
Fita salla yayi ita kuma ta koma sashenta tayi tata sallar, anan ta zauna tafara yin azkar irin wanda jabir ya koya mata, dab da sallar isha ta tashi takoma sashensa tana sanye da zumbulelen hijabi mai hannu wanda ya saukar mata har kafafunta domin yanzu jabir ya kawo mata hijabai manya kala daban daban.
Asashensa tayi sallar isha, tana idarwa tafara karanta hadisin da ya koyar da ita adaren jiya wanda aka karbo daga baban hurairata Allah ya kara masa yarda wanda annabi Muhammad sallallahu alaihi wassalam yake cewa "yaku mutane ku yada sallama, kubayar da sadaka, kuyi sallar dare alokacin da mutane suke bacci, idan kukayi haka hakika zaku shiga aljanna da aminci"
Shigowar jabir ce ta katse mata tilawar karatun da takeyi, kafadunta ya kama ya mikar da ita tsaye,
"Tashi muyi salla binti"
"Abbu ni nayi sallata yanzun nan na idar"
Dan malalacin murmushi yayi mata "binti wannan ai daban, wannan ta nafila ce zamuyi, sannan ina son ki dage ki rinka yin sallar shafa'i da wutr domin tanada tsananin falala mai tarin yawa"
"Abbu zan rinka yi kaga shikenan basai nayi ta tsakar dareba irin wacce kake yi"
"Waya fada miki? Koda ace kinyi shafa'i da wutr to zaki iya tashi da daddare kisake yin sallolin nafilarki kuma zakiyi shafa'i,wutr ne kawai bazaki yiba domin sau daya ake yinsa idan mutum ya sake to yazama shafa'i, nasan mutane da dama suna son tashi yin sallar dare to amma idan har sukayi shafa'i da wutr sai su zaci Cewar shikenan babu damar yin wata sallar tunda sun rufe da wutr to ba haka bane mutum zai iya yin wasu sallolin acikin dare koda kuwa yayi shafa'i da wutr kawai dai ba ason ya sake yin wutr ne domin wanda yayi afarko ya wadatar"
Kai ta kada masa tafara gyara masa abin sallar yanda zai ishesu,
Limanci yayi yajasu sallar suka gudanar da sallolin nafila wanda hadda shafa'i da wutr, addu'o'i sosai jabir yayi musu wadanda ba zasu faduba,
Bayan ya shafane ya jiyo yana kallonta, "binti idan kin idar akwai kaya acikin babban falo kije ki dauko, ina fata dai bakiyi wani girkin ba? Saboda yau naga kinsha aiki da yawa"
Addu'ar ta shafa tana kokarin cire hijabin jikinta "hmm abbu banyi ba dama yanzu nake tunanin dafa mana indomie"
"To na hutar dake basai kin dafa ba"
Hijab din ta ajiye ta fita taje ta shigo da kayan da yazo musu dashi,
Kaza dukekiya ta gani guda biyu gasassu ga chocolates dinta kala kala sannan ga kayan marmari suma daban daban,
Baje kayan tayi tana kallon jabir "abbu yau ka hutar dani nagode da yanzu sai nasake shiga kitchen"
Yan yatsunta ya kamo "babu komai binti, ai naga sakonki ya sameni har office, me yasa kika bini dashi har can?"
"Bana son ka zauna da yunwane shiyasa kuma nasan kai ba cin abinci zakayi ba haka zaka wuni da yunwa nikuma bana son haka"
"Nagode binti, ga abinci nan kici nakine ke daya"
Idanuwanta ta ware "abbu wannan sunyi min yawa, bazan iya cinyesu ba"
Kankana ya dauka yakai bakinsa "ni kinga iya abinda nake sha'awa kawai, ita kadai zansha"
"Abbu kazar fa?"
"Takice yarinya, kici kayanki kinji"
Kai ta girgiza tafara yagar kazar tana ci har taci rabi nan taji tafara koshi,
"Abbu yau zaka doramin karatu ko sai gobe?"
"Duk yanda kikeso binti, amma karatunmu na yau daban yake dana ko wacce rana, karatun yau na musamman ne"
Cigaba tayi da shan chocolate dinta domin bata fahimci inda maganar tasa ta dosa ba, har ta kammala yana zaune yana kallonta, kanta ta dora asaman cinyarsa,
"Washh abbu cikina nakoshi da yawa"
Kanta ya fara shafawa yana yi mata lalube acikin gashinta
"Kinyi irin koshin da ba aso mutum yayi, annabi yace idan dayanku zaici abinci to ya raba cikinsa gida uku, kashi daya abinci kashi daya ruwa, kashi dayan kuma iska saboda gudun kada ya cutar da jikinsa"
Zaune ta tashi "hmm abbu komai dai a musulunci ana bashi hakkinsa, Allah abbu musulmai sunji dadin rayuwarsu"
"Tashi muje nasaki aiki a kitchen"
Tashi yayi yaja hannunta suka fita zuwa kitchen, shayin na'a na'a ta dafa masa da kayan kamshi sannan suka dawo sashensa, tana kwance akan cinyarsa akan doguwar kujera shikuma yana shan shayinsa ga tv kuma yana kallo,
Wayarshi ce tafara kara, yana dubawa yaga ummu ce,
"Ummu al'amin kin dawone daga siyayyar?"
Tana jin ya ambaci sunan ummu tafara kokarin mikewa, cup din shayin ya ajiye ya riketa ya mayar da ita jikinsa yaci gaba da wayarshi daga karshe sukayi sallama yana tambayarta al'amin tace yayi bacci tun jimawa,
Wayar ya kashe yana kallon bahijja bayan sunyi sallamar da ummu,
"Abbu bacci, zanje nayi wanka" tafada tana mutsusstuka idonta,
"Bari nagama nakaiki kiyi" bata sake magana ba ta zauna tana jiransa, kasancewar komai nashi cikin sanyi yake yinsa shiyasa ya dade bai gamaba,
Yana gamawa ya kama hannunta zuwa cikin bedroom dinsa,
"Ki shiga kiyi wankan" ya nuna mata bathroom dinsa,
"Abbu brush dina da kayan baccina fa"
"Duk zan baki binti, ai na tanadar miki komai saboda zuwan wannan ranar"
Sabon brush ya dauko ya mika mata hadeda babban towel sabo fil,
Karba tayi ta shiga bathroom din amma duk tana cikeda mamaki da al'ajabi,
"Binti yau bazaki bar kofar bathroom din abude ba? Ko yau babu tsoro?" Yafada cikin tsokana,
Batayi magana ba tasaka key ta kulle kofar, mayukan wanka ta gani masu kamshi dayawa kala kala, duk sai da tayi amfani dasu ta wanke jikinta tas sannan tayi brush ta tsaftace bakinta bayan ta shaftace jikinta da shaving stick, hatta bayan kunnuwanta sai da ta tsaftacesu kasancewar wurine dake rike kazanta dan haka dole sai ana kulawa dashi,
Sai da ta dauki tsawon lokaci tana gyara jikinta sannan ta fito duk a tsure take da jabir sai muzurai take yi.
Acikin dakin tasameshi kishingide agefen gado yana kallonta, irin kallon da yake binta yasata jin kunya,
"Abbu nafito" tafada adirirce,
"Ga rigar baccinki nan kishirya sai kisa"
Towel din jikinta ta gyara,
"Abbu to ka fita daga dakin"
"Tofa, wata sabuwa" tashi yayi yana kallonta yafita ya koma falo, gaban mirror ta karasa ta fara shafe jikinta da man shafawarsa na touch me mai dadin kamshi, turarurrukansa ta fara dubawa har ta samo wani guda daya mai suna taibah, shi ta dauka ta feshe jikinta dashi sannan ta feshe rigar baccinta,
Bathroom ta koma ta tsaya tafara duba rigar, tabbas rigar ta hadu sai dai kuma zatasha kunya yau domin rigar za a iya kiranta da shararatu, banbancinta da gidan sauro kawai ita rigace amma net shine yanayinta,
Rigar bata bukatar bra domin akwai ajiki sannan tanada dan karamin pant,kalarta pink colour,
Daurewa tayi tasaka rigar, tana gama sakawa ta juya tafara kallon jikinta ajikin mirror din cikin bayin, tayi kyau iya kyau abunka da yar duma duma sai kace oh oh, jin alamun za a bude kofar yasata saurin janyo towel ta lullube jikinta, jabir ne ya leko ya jawota waje,
"Haba binti me kika sake komawa yi acikin bathroom kuma?"
Towel din yafara ja yayinda ita kuma ta rike kam, dakyar ya janye towel din hakan ya sata saurin rufe fuskarta da tafukan hannayenta,
"Masha Allah, binti irin wannan kyau haka?"
Sake damke idonta tayi tana doddoka kafafunta akasa,
"To jeki ki kwanta kinji"
Hannunta ya kama ya rakata har inda ta saba kwanciya ya saketa ya juya, cikin bathroom din shima ya shiga yayi wanka bayan ya tsaftace kowanne lungu na jikinsa,
Fitowa yayi yanata faman kamshi, gaban mirror yaje ya fara shafe jikinsa da mayuka masu kamshi,
Kayan baccinshi ya dauko yasaka ya karasa gefenta ya kwanta gamida janta jikinsa,
"Binti ko har kinyi baccine bayan ba muyi hira ba yau?" Yarada mata ahankali yana wasa da zip din rigarta, tana jinsa tayi shiru tayi luf,
"Nasan idonki biyu, jiyo kiji"
Yafada ahankali, jin shiru yasashi jiyo da ita tana fuskantarsa, cakulkuli yafara yi mata cikin sauri ta rike hannunsa bayan tafara dariya,
"Abbu kabari dan Allah"
"Au dama kina jina shine kikayi min shiru?"
"Bazan karaba yi hakuri abbu"
"Yawuce binti, shikenan saura karatunmu da muka fara rannan ko?"
Bata iya yin magana ba hakan ya sashi kashe wutar dakin bayan ya lalubi bakinta cikin nashi.
***
K'arfe 8 daidai ta bude idonta, dakin shiru babu motsin komai aciki,sama ta daga kanta take kallo take abubuwan da abbu yayi mata suka fara dawo mata, hawayen farin ciki tafara yi fuskarta dauke da murmushi domin wannan rana ta jiya da yau ranakune masu mutukar muhimmanci acikin rayuwarta,
Dakyar ta juya jikinta daga barin da take kwance nan taga tsakiyar gadon tamkar an yanka kaza,
"Hmmmmm abbu kenan" shine abinda kawai tafada ahankali tafara kokarin tashi, lallabawa tayi ta shiga toilet tana dingisawa, ruwan zafi ta tara mai mutukar zafi amma bata saka dettol aciki ba kasancewar ta taba jin wani likita yana bayani kan illolin dettol ajikin mace shiyasa ba ason ayi sit bath dashi amma babu laifi ayi wanka dashi ko kuma awanke kaya domin yana da karfi yana kashe bacteria kowacce iri ciki harda mai amfani da marar amfani, gishiri kawai ta zuba acikin ruwan zafin ta shiga ta zauna domin shi gishiri har maganin kaikayin dake damun mutum yake yi haka kuma yana riga kafin ciwon cutar sanyi,
Ta dade acikin ruwan har sai da ya huce sannan tafita tayi wanka tayi brush amma duk agaggauce take yin wadannan abubuwan saboda bata son jabir ya shigo ya isketa bata shirya ba kuma haka ya kamata ga kowacce mace domin lokacin da aka tashi daga bacci agaskiya lokacine dake bayyanar da munin mutum kasancewar daga bacci aka tashi zaka samu wata ma launin fuskarta ya sauya idonta yayi ja wata harda kwantsa, sannan ita kanta yanayin fuskar wani iri yake zama har sai anyi wanka,
Fitowa tayi daga cikin bayin tayi maza tafara bincikar kayan sawarsa, wata farar t shirt ta zaro mai layi layi ajiki mai dogon hannu da maballaye ajiki, cikin sauri ta saka rigar sannan ta zaro jeans blue shima tasaka sai dai kayan tsayinsu yayi mata yawa kasancewar jabir dogone ajin farko,
Fita salla yayi ita kuma ta koma sashenta tayi tata sallar, anan ta zauna tafara yin azkar irin wanda jabir ya koya mata, dab da sallar isha ta tashi takoma sashensa tana sanye da zumbulelen hijabi mai hannu wanda ya saukar mata har kafafunta domin yanzu jabir ya kawo mata hijabai manya kala daban daban.
Asashensa tayi sallar isha, tana idarwa tafara karanta hadisin da ya koyar da ita adaren jiya wanda aka karbo daga baban hurairata Allah ya kara masa yarda wanda annabi Muhammad sallallahu alaihi wassalam yake cewa "yaku mutane ku yada sallama, kubayar da sadaka, kuyi sallar dare alokacin da mutane suke bacci, idan kukayi haka hakika zaku shiga aljanna da aminci"
Shigowar jabir ce ta katse mata tilawar karatun da takeyi, kafadunta ya kama ya mikar da ita tsaye,
"Tashi muyi salla binti"
"Abbu ni nayi sallata yanzun nan na idar"
Dan malalacin murmushi yayi mata "binti wannan ai daban, wannan ta nafila ce zamuyi, sannan ina son ki dage ki rinka yin sallar shafa'i da wutr domin tanada tsananin falala mai tarin yawa"
"Abbu zan rinka yi kaga shikenan basai nayi ta tsakar dareba irin wacce kake yi"
"Waya fada miki? Koda ace kinyi shafa'i da wutr to zaki iya tashi da daddare kisake yin sallolin nafilarki kuma zakiyi shafa'i,wutr ne kawai bazaki yiba domin sau daya ake yinsa idan mutum ya sake to yazama shafa'i, nasan mutane da dama suna son tashi yin sallar dare to amma idan har sukayi shafa'i da wutr sai su zaci Cewar shikenan babu damar yin wata sallar tunda sun rufe da wutr to ba haka bane mutum zai iya yin wasu sallolin acikin dare koda kuwa yayi shafa'i da wutr kawai dai ba ason ya sake yin wutr ne domin wanda yayi afarko ya wadatar"
Kai ta kada masa tafara gyara masa abin sallar yanda zai ishesu,
Limanci yayi yajasu sallar suka gudanar da sallolin nafila wanda hadda shafa'i da wutr, addu'o'i sosai jabir yayi musu wadanda ba zasu faduba,
Bayan ya shafane ya jiyo yana kallonta, "binti idan kin idar akwai kaya acikin babban falo kije ki dauko, ina fata dai bakiyi wani girkin ba? Saboda yau naga kinsha aiki da yawa"
Addu'ar ta shafa tana kokarin cire hijabin jikinta "hmm abbu banyi ba dama yanzu nake tunanin dafa mana indomie"
"To na hutar dake basai kin dafa ba"
Hijab din ta ajiye ta fita taje ta shigo da kayan da yazo musu dashi,
Kaza dukekiya ta gani guda biyu gasassu ga chocolates dinta kala kala sannan ga kayan marmari suma daban daban,
Baje kayan tayi tana kallon jabir "abbu yau ka hutar dani nagode da yanzu sai nasake shiga kitchen"
Yan yatsunta ya kamo "babu komai binti, ai naga sakonki ya sameni har office, me yasa kika bini dashi har can?"
"Bana son ka zauna da yunwane shiyasa kuma nasan kai ba cin abinci zakayi ba haka zaka wuni da yunwa nikuma bana son haka"
"Nagode binti, ga abinci nan kici nakine ke daya"
Idanuwanta ta ware "abbu wannan sunyi min yawa, bazan iya cinyesu ba"
Kankana ya dauka yakai bakinsa "ni kinga iya abinda nake sha'awa kawai, ita kadai zansha"
"Abbu kazar fa?"
"Takice yarinya, kici kayanki kinji"
Kai ta girgiza tafara yagar kazar tana ci har taci rabi nan taji tafara koshi,
"Abbu yau zaka doramin karatu ko sai gobe?"
"Duk yanda kikeso binti, amma karatunmu na yau daban yake dana ko wacce rana, karatun yau na musamman ne"
Cigaba tayi da shan chocolate dinta domin bata fahimci inda maganar tasa ta dosa ba, har ta kammala yana zaune yana kallonta, kanta ta dora asaman cinyarsa,
"Washh abbu cikina nakoshi da yawa"
Kanta ya fara shafawa yana yi mata lalube acikin gashinta
"Kinyi irin koshin da ba aso mutum yayi, annabi yace idan dayanku zaici abinci to ya raba cikinsa gida uku, kashi daya abinci kashi daya ruwa, kashi dayan kuma iska saboda gudun kada ya cutar da jikinsa"
Zaune ta tashi "hmm abbu komai dai a musulunci ana bashi hakkinsa, Allah abbu musulmai sunji dadin rayuwarsu"
"Tashi muje nasaki aiki a kitchen"
Tashi yayi yaja hannunta suka fita zuwa kitchen, shayin na'a na'a ta dafa masa da kayan kamshi sannan suka dawo sashensa, tana kwance akan cinyarsa akan doguwar kujera shikuma yana shan shayinsa ga tv kuma yana kallo,
Wayarshi ce tafara kara, yana dubawa yaga ummu ce,
"Ummu al'amin kin dawone daga siyayyar?"
Tana jin ya ambaci sunan ummu tafara kokarin mikewa, cup din shayin ya ajiye ya riketa ya mayar da ita jikinsa yaci gaba da wayarshi daga karshe sukayi sallama yana tambayarta al'amin tace yayi bacci tun jimawa,
Wayar ya kashe yana kallon bahijja bayan sunyi sallamar da ummu,
"Abbu bacci, zanje nayi wanka" tafada tana mutsusstuka idonta,
"Bari nagama nakaiki kiyi" bata sake magana ba ta zauna tana jiransa, kasancewar komai nashi cikin sanyi yake yinsa shiyasa ya dade bai gamaba,
Yana gamawa ya kama hannunta zuwa cikin bedroom dinsa,
"Ki shiga kiyi wankan" ya nuna mata bathroom dinsa,
"Abbu brush dina da kayan baccina fa"
"Duk zan baki binti, ai na tanadar miki komai saboda zuwan wannan ranar"
Sabon brush ya dauko ya mika mata hadeda babban towel sabo fil,
Karba tayi ta shiga bathroom din amma duk tana cikeda mamaki da al'ajabi,
"Binti yau bazaki bar kofar bathroom din abude ba? Ko yau babu tsoro?" Yafada cikin tsokana,
Batayi magana ba tasaka key ta kulle kofar, mayukan wanka ta gani masu kamshi dayawa kala kala, duk sai da tayi amfani dasu ta wanke jikinta tas sannan tayi brush ta tsaftace bakinta bayan ta shaftace jikinta da shaving stick, hatta bayan kunnuwanta sai da ta tsaftacesu kasancewar wurine dake rike kazanta dan haka dole sai ana kulawa dashi,
Sai da ta dauki tsawon lokaci tana gyara jikinta sannan ta fito duk a tsure take da jabir sai muzurai take yi.
Acikin dakin tasameshi kishingide agefen gado yana kallonta, irin kallon da yake binta yasata jin kunya,
"Abbu nafito" tafada adirirce,
"Ga rigar baccinki nan kishirya sai kisa"
Towel din jikinta ta gyara,
"Abbu to ka fita daga dakin"
"Tofa, wata sabuwa" tashi yayi yana kallonta yafita ya koma falo, gaban mirror ta karasa ta fara shafe jikinta da man shafawarsa na touch me mai dadin kamshi, turarurrukansa ta fara dubawa har ta samo wani guda daya mai suna taibah, shi ta dauka ta feshe jikinta dashi sannan ta feshe rigar baccinta,
Bathroom ta koma ta tsaya tafara duba rigar, tabbas rigar ta hadu sai dai kuma zatasha kunya yau domin rigar za a iya kiranta da shararatu, banbancinta da gidan sauro kawai ita rigace amma net shine yanayinta,
Rigar bata bukatar bra domin akwai ajiki sannan tanada dan karamin pant,kalarta pink colour,
Daurewa tayi tasaka rigar, tana gama sakawa ta juya tafara kallon jikinta ajikin mirror din cikin bayin, tayi kyau iya kyau abunka da yar duma duma sai kace oh oh, jin alamun za a bude kofar yasata saurin janyo towel ta lullube jikinta, jabir ne ya leko ya jawota waje,
"Haba binti me kika sake komawa yi acikin bathroom kuma?"
Towel din yafara ja yayinda ita kuma ta rike kam, dakyar ya janye towel din hakan ya sata saurin rufe fuskarta da tafukan hannayenta,
"Masha Allah, binti irin wannan kyau haka?"
Sake damke idonta tayi tana doddoka kafafunta akasa,
"To jeki ki kwanta kinji"
Hannunta ya kama ya rakata har inda ta saba kwanciya ya saketa ya juya, cikin bathroom din shima ya shiga yayi wanka bayan ya tsaftace kowanne lungu na jikinsa,
Fitowa yayi yanata faman kamshi, gaban mirror yaje ya fara shafe jikinsa da mayuka masu kamshi,
Kayan baccinshi ya dauko yasaka ya karasa gefenta ya kwanta gamida janta jikinsa,
"Binti ko har kinyi baccine bayan ba muyi hira ba yau?" Yarada mata ahankali yana wasa da zip din rigarta, tana jinsa tayi shiru tayi luf,
"Nasan idonki biyu, jiyo kiji"
Yafada ahankali, jin shiru yasashi jiyo da ita tana fuskantarsa, cakulkuli yafara yi mata cikin sauri ta rike hannunsa bayan tafara dariya,
"Abbu kabari dan Allah"
"Au dama kina jina shine kikayi min shiru?"
"Bazan karaba yi hakuri abbu"
"Yawuce binti, shikenan saura karatunmu da muka fara rannan ko?"
Bata iya yin magana ba hakan ya sashi kashe wutar dakin bayan ya lalubi bakinta cikin nashi.
***
K'arfe 8 daidai ta bude idonta, dakin shiru babu motsin komai aciki,sama ta daga kanta take kallo take abubuwan da abbu yayi mata suka fara dawo mata, hawayen farin ciki tafara yi fuskarta dauke da murmushi domin wannan rana ta jiya da yau ranakune masu mutukar muhimmanci acikin rayuwarta,
Dakyar ta juya jikinta daga barin da take kwance nan taga tsakiyar gadon tamkar an yanka kaza,
"Hmmmmm abbu kenan" shine abinda kawai tafada ahankali tafara kokarin tashi, lallabawa tayi ta shiga toilet tana dingisawa, ruwan zafi ta tara mai mutukar zafi amma bata saka dettol aciki ba kasancewar ta taba jin wani likita yana bayani kan illolin dettol ajikin mace shiyasa ba ason ayi sit bath dashi amma babu laifi ayi wanka dashi ko kuma awanke kaya domin yana da karfi yana kashe bacteria kowacce iri ciki harda mai amfani da marar amfani, gishiri kawai ta zuba acikin ruwan zafin ta shiga ta zauna domin shi gishiri har maganin kaikayin dake damun mutum yake yi haka kuma yana riga kafin ciwon cutar sanyi,
Ta dade acikin ruwan har sai da ya huce sannan tafita tayi wanka tayi brush amma duk agaggauce take yin wadannan abubuwan saboda bata son jabir ya shigo ya isketa bata shirya ba kuma haka ya kamata ga kowacce mace domin lokacin da aka tashi daga bacci agaskiya lokacine dake bayyanar da munin mutum kasancewar daga bacci aka tashi zaka samu wata ma launin fuskarta ya sauya idonta yayi ja wata harda kwantsa, sannan ita kanta yanayin fuskar wani iri yake zama har sai anyi wanka,
Fitowa tayi daga cikin bayin tayi maza tafara bincikar kayan sawarsa, wata farar t shirt ta zaro mai layi layi ajiki mai dogon hannu da maballaye ajiki, cikin sauri ta saka rigar sannan ta zaro jeans blue shima tasaka sai dai kayan tsayinsu yayi mata yawa kasancewar jabir dogone ajin farko,