Sashe 32
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ceto gaskiyane za ayi ceto ranar alqiyama to amma suwaye zasu yi ceton?,da farko dai annabawa zasuyi ceto, shahidai zasu yi ceto wato wadan da sukayi mutuwar shahada sannan siddikai zasuyi ceto, siddikai sune wadanda Allah ya basu wata karin daraja bayan annabta, misali annabi Idris da annabi Ibrahim kowannensu Allah ya bashi matsayin siddiki acikin alqur'ani mai girma,
Allah yace _"Wazkur fil kitabi Idris innahu kana siddikan nabiya, acikin wata surar kuma yace wazkur fil kitabi ibrahim innahu kana siddikan nabiya"_
Bayan siddikai sai yara kanana wadanda suka rasu kafin su girma suma zasuyi ceto sannan alqur'ani mai girma shima zaiyi ceto kamar yadda annabi Muhammad (S.A.W) yafada,
_"Ku yawaita karanta alqur'ani musamman suratul bak'ara da suratul al'imran domin kowannensu ranar alqiyama zai zama giza gizai zai yiwa mai karantashi rumfa, zasu zo filin alqiyama domin ceton masu karantasu"_
Sannan wasu malaman sunce mutane na kwarai salihan bayi suma zasu yi ceto sai dai amma duk wanda za aceta sai yana da imani, mutukar bai mutu da imani acikin zuciyarsa ba to bazai samu wannan ceton da ake fada ba ina fata kin fahimceni"
Kanta ta daga duk jikinta amace,
"Yes,na fahimta"
Mikewa jabir yayi yana gyara babbar rigarsa ya fice, zama tayi cikin falon tana nazarin amsoshin da jabir ya bata.
Haka suka ci gaba da kasancewa da jabir amma kullum yana bata kissar annabawa, har yau bai daina ba yanzu ya bata ta annabi Yusuf da yan uwansa da irin rayuwar da yayi agidan kurkuku da kuma haduwarsa da yan uwansa har lokacin da ya koma ga ubangijinsa.
Duk ranar Sunday tana zuwa church acan take haduwa da ma, shikuma jabir ya fara shirye shiryen tunkarar azumin watan ramadan,
Tunda watan azumi ya kama baya zama ga zuwa office da yake yi baya tasowa sai 5 da zarar ya dawo kuma zai tafi wurin da yake yin tafsir, sai bayan sallar isha zai dawo gida kasancewar wannan azumin bai tafi wata jahar ba saboda goodness amma da lokacin da shida Ummu al'amin ne wata state din yake zuwa,
Yanzu zamansa agidan babu yawa ba kamar da bane domin kullum bashida lokacin hutu, duk goodness tabi ta damu na rashin zamansa agidan sosai, amma tana iya kokarinta na ganin ta yi masa duk wani abu wanda zai sakashi farin ciki, tsakaninta dashi kuwa sai dai kallo domin yanzu baccin ma bayinsa yake yi sosai ba kullum yana cikin ibada gashi da rana ba damar ta ganshi tunda ba agida yake wuni ba.
Goman karshe na kamawa ya tafi umarah yabarta ita kadai agidan,tafiyarsa ta sakata cikin damuwa kullum adakinshi take kwana kasancewar abude yabar mata shi, sannan akoda yaushe yana kiranta awaya suna gaisawa wani lokacin kuma yabarta da al'amin suyita faman surutunsu,
Kwanansa goma sha daya da tafiya ta tashi da wani yanayi yanayin kuwa shine ji tayi ta tsani halinda take ciki gaba daya labaran da jabir ya bata sune ke mata yawo acikin brain dinta,so take kawai taganta tana salla domin taji irin abinda jabir yake ji, sannan ta fuskanci jabir bazai taba sonta acikin wannan yanayin da take ba, tasan idan ta zama musulma jabir zai sota zai kaunaceta kuma zai nuna mata soyayya, tunanin abinyi tafara acikin ranta shin ta musulunta ko kuma ta zauna acikin addinin da take???????
Masu karatu mu jira shafi nagaba domin jin abinda zai biyo baya.amma shin kuna ganin cewa jabir zai so goodness kuwa koda ace ta musulunta?? Nidai ummi A'isha bani da wannan amsar. Sannan ina mai baku hakuri da yanayin irin turancin da nayi amfani dashi aciki (broken) ni anawa ganin yawancin Christians musamman ma na kudu turancinsu ba pure bane sunfi yin broken ina fata hakan bazai zama matsala ba, burina dai kawai Ku fahimci sakon da littafin yake dauke dashi ba turancin ba.
_safiyya Ummu Abdul nagasheki gaisuwa marar adadi._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_*Masoya ina godiya agareku, wadanda sakonsu ya iskeni da wadanda sakonninsu basu samu damar zuwa gareni ba duk nagode Allah yabar zumunci da soyayya, da ace da hali da na lissafo sunayenku amma babu damar yin hakan, nagode sosai ina sonku fiyeda yadda kuke sona.*_
_81-85_
~~~Tunanin abinyi ta fara yi amma kuma acan kasan ranta tana jin tsoron mamanta domin bata mantawa tun kafin aurenta da jabir ma tace indai ta sake ta musulunta sai ta yankanta,
"Ohh my God" tafada gamida dafe goshinta, yanzu a yan kwanakin nan duk ta sauya hatta dabi'unta ma sun sauya ta daina sauraron wakokin da ada sune suka zame mata abin ji akoda yaushe sannan yanzu ta rage yawan karanta Bible dinta domin tunowa da tayi wata rana ta taba bawa jabir bible din sai yaki karba da ta matsa masa da maganar sai ya jiyo ya rike yan yatsunta yana mai fuskantarta,
"Goodness baya halatta agareni da na karanta bible bawai ina nufin ya zama haramun bane sai dai ni yanzu alqur'ani shine littafin da yafi cancanta da na rike kuma na karanta akoda yaushe saboda azamanin annabi Muhammad (S.A.W),annabi ya taba ganin sayyadina umar yana karanta wata takarda sai annabi yake tambayarsa menene wannan yake karantawa? Sai sayyadina Umar yace injila ce, wato wani dan yanki ne nacikin injila, anan sai fuskar annabi ta sauya zuwa fushi, ransa ya baci mutuka har yace da sayyadina Umar ko annabi Isah ne ya dawo awannan lokacin to wlhi dole yabishi yabi sunnarsa, atake sayyidana Umar ya nemi afuwar annabi yace bazai sake karantawa ba"
Zama tayi na dirshan tana tuno kyawawan halayen mijinta jabir, komai nashi mai nagarta he, bashida yawan hayaniya gashi ya rike addininsa da hannu bibbiyu, adan zaman da tayi dashi daga lokacin data fara hada makwanci dashi har zuwa wannan lokacin da yayi tafiya ta fahimci shi mutum ne mai mutukar tsoron Allah ga tarin ilimi akansa kamar ruwa, komai nashi Allah ga yawan bincike akan abubuwan da suka shafi addininsa, idanuwanta ta lumshe tana mai tuno da kyakkyawar surarsa wacce take mai daukar hankalin duk wata mace,
"To yanzu menene abin yi?" Ta tambayi kanta, Kodai babanta zataje ta fadawa? Ita dai tana son yanzu ta zama kamar jabir ta fuskar rayuwa,
Yayarta ta kira wato Anty Bilkisu tafada mata tana son ta karbi addinin musulunci, ba karamin murna anty Bilkisu tayiba domin dama addu'ar da ta dade tana yiwa goodness kenan na ta samu *Wani Haske* acikin rayuwarta,nan anty bilkisu ta bata shawara akan taje gida ta sanar da babansu tukunna,
Shiryawa tayi tabi shawarar Anty Bilkisu ta tafi gidan iyayenta, kamar kullum gidan babu kowa sai mahaifinta kadai wanda yake zaune a tsakar gidan ya shimfida tabarma yana kishingide yana sauraren radio,
Shigarta shigace ta mutumci domin bakar rigace ajikinta ta yafa bakin dan kwalin rigar, ko ba afada mata ba tasan ma tatafi church,
Agefen tabarmar ta zauna bayan sun gaisa tafara yiwa babanta bayani,
"Papa munyi magana da anty bilkisu ne nafada mata ina son zan musulunta shine tace inzo in sanar dakai"
Zaune baban nata ya tashi daga kishingidar da yayi, jin maganar yake kamar a mafarki wai goodness zata musulunta,
"Alhamdulillah, lallai Allah shine mai iko akan dukkanin komai, sannan kuma dama rahamar ubangiji haka take, wani baya musulunta sai har yaga wani mutum yana salla alhalin kuma ba aranar yafara ganin ana salla ba, wani kuma karatun alqur'ani zai ji sai kawai yayi sha'awar musulunci bayan ba ranar ya fara jin karatun qur'anin ba, kai koma dai menene to wannan wata babbar rahama ce daga Allah,
Goodness hakika ubangiji yasoki da rahama kuma yasoki da samun babban rabo acikin rayuwarki, yanzu abinda nake so dake shine kar ki yarda ki sanar da mahaifiyarki sannan kije gidan mahaifin jabir mijinki ki karbi musulunci agurin mahaifinsa, bana son mamanku tazo ta tarar dake agidan nan,ubangiji Allah yayi miki albarka yasake baki *Wani haske* acikin rayuwarki"
Mahaifinta yafada yana kwallar farin ciki, ita kanta goodness itama hawayen take yi, tashi tayi tafita ta koma gidanta, katoton dogon hijabin da Ummu al'amin ta bata ta dauko ta dorashi asaman doguwar rigarta ta tafi gidansu jabir,
A soro ta tarar da Malam mahaifin jabir, Malam yayi mamakin ganinta amma lokacin da yaji kudirinta sai mamakinsa ya sake karuwa gamida farin ciki, wanda har sai da hakoransa suka bayyana,
"Dafarko dai ina fata ba wani ra'ayine yasaki sha'awar karbar musulunci ba? Ina fatan zaki yi hakanne domin Allah saboda dukkan aiki sai da niyya shiyasa acikin hadisin da aka karbo daga Umar Allah ya kara masa yarda yace annabi Muhammad yace dukkan aiki sai da niyya sannan kowanne mutum akwai abinda yayi niyya, duk wanda yayi hijira domin Allah da manzonsa to sakamakon hijirarsa tana ga Allah da son manzonsa,wanda yayi hijira kuwa domin duniya ko wata k'awa, ko dan wata mace da zai aura to sakamakon hijirarsa tana ga abinda yayi hijira dominsa, shugaban masu rawaito hadisai ne ya rawaito wannan hadisin _(imamul muhaddasina)_"
Kanta ta daga "ba wani ne ya tilastani ba, kuma ba dan wani nayi hakan ba face dan Allah"
"To alhamdulillah, da farko dai ina son kisani shi musulunci yana nufin mika wuya ga Allah, da jawuwa agareshi da biyayya,da kuma tsarkakewa daga shirka,
Sannan shi musulunci yana da ginshikai guda biyar kamar yadda annabi Muhammad yafada acikin ingantaccen hadisi cewar angina musulunci akan abubuwa guda biyar, nafarko shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah sannan annabi Muhammad manzon Allahne, sai tsayar da salla, salla itace aiki nafarko da zafara bincikawa ranar tashin alqiyama, idan ta gyaru dukkan ayyuka sun gyaru idan kuma an samu sabanin haka to abin sai dai ace Allah ya kyauta,abu na uku shine azumin watan ramadan,
Amma babu tilas akan marar lafiya, ko kuma tsoho wanda shekarunsa suka ja ko kuma karamin yaro, ko matafiyi duk an samu rangwame akan wadannan mutanen,
Allah yace _"Wazkur fil kitabi Idris innahu kana siddikan nabiya, acikin wata surar kuma yace wazkur fil kitabi ibrahim innahu kana siddikan nabiya"_
Bayan siddikai sai yara kanana wadanda suka rasu kafin su girma suma zasuyi ceto sannan alqur'ani mai girma shima zaiyi ceto kamar yadda annabi Muhammad (S.A.W) yafada,
_"Ku yawaita karanta alqur'ani musamman suratul bak'ara da suratul al'imran domin kowannensu ranar alqiyama zai zama giza gizai zai yiwa mai karantashi rumfa, zasu zo filin alqiyama domin ceton masu karantasu"_
Sannan wasu malaman sunce mutane na kwarai salihan bayi suma zasu yi ceto sai dai amma duk wanda za aceta sai yana da imani, mutukar bai mutu da imani acikin zuciyarsa ba to bazai samu wannan ceton da ake fada ba ina fata kin fahimceni"
Kanta ta daga duk jikinta amace,
"Yes,na fahimta"
Mikewa jabir yayi yana gyara babbar rigarsa ya fice, zama tayi cikin falon tana nazarin amsoshin da jabir ya bata.
Haka suka ci gaba da kasancewa da jabir amma kullum yana bata kissar annabawa, har yau bai daina ba yanzu ya bata ta annabi Yusuf da yan uwansa da irin rayuwar da yayi agidan kurkuku da kuma haduwarsa da yan uwansa har lokacin da ya koma ga ubangijinsa.
Duk ranar Sunday tana zuwa church acan take haduwa da ma, shikuma jabir ya fara shirye shiryen tunkarar azumin watan ramadan,
Tunda watan azumi ya kama baya zama ga zuwa office da yake yi baya tasowa sai 5 da zarar ya dawo kuma zai tafi wurin da yake yin tafsir, sai bayan sallar isha zai dawo gida kasancewar wannan azumin bai tafi wata jahar ba saboda goodness amma da lokacin da shida Ummu al'amin ne wata state din yake zuwa,
Yanzu zamansa agidan babu yawa ba kamar da bane domin kullum bashida lokacin hutu, duk goodness tabi ta damu na rashin zamansa agidan sosai, amma tana iya kokarinta na ganin ta yi masa duk wani abu wanda zai sakashi farin ciki, tsakaninta dashi kuwa sai dai kallo domin yanzu baccin ma bayinsa yake yi sosai ba kullum yana cikin ibada gashi da rana ba damar ta ganshi tunda ba agida yake wuni ba.
Goman karshe na kamawa ya tafi umarah yabarta ita kadai agidan,tafiyarsa ta sakata cikin damuwa kullum adakinshi take kwana kasancewar abude yabar mata shi, sannan akoda yaushe yana kiranta awaya suna gaisawa wani lokacin kuma yabarta da al'amin suyita faman surutunsu,
Kwanansa goma sha daya da tafiya ta tashi da wani yanayi yanayin kuwa shine ji tayi ta tsani halinda take ciki gaba daya labaran da jabir ya bata sune ke mata yawo acikin brain dinta,so take kawai taganta tana salla domin taji irin abinda jabir yake ji, sannan ta fuskanci jabir bazai taba sonta acikin wannan yanayin da take ba, tasan idan ta zama musulma jabir zai sota zai kaunaceta kuma zai nuna mata soyayya, tunanin abinyi tafara acikin ranta shin ta musulunta ko kuma ta zauna acikin addinin da take???????
Masu karatu mu jira shafi nagaba domin jin abinda zai biyo baya.amma shin kuna ganin cewa jabir zai so goodness kuwa koda ace ta musulunta?? Nidai ummi A'isha bani da wannan amsar. Sannan ina mai baku hakuri da yanayin irin turancin da nayi amfani dashi aciki (broken) ni anawa ganin yawancin Christians musamman ma na kudu turancinsu ba pure bane sunfi yin broken ina fata hakan bazai zama matsala ba, burina dai kawai Ku fahimci sakon da littafin yake dauke dashi ba turancin ba.
_safiyya Ummu Abdul nagasheki gaisuwa marar adadi._
*_Ummi Shatu_*👌🏻
[
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_*Masoya ina godiya agareku, wadanda sakonsu ya iskeni da wadanda sakonninsu basu samu damar zuwa gareni ba duk nagode Allah yabar zumunci da soyayya, da ace da hali da na lissafo sunayenku amma babu damar yin hakan, nagode sosai ina sonku fiyeda yadda kuke sona.*_
_81-85_
~~~Tunanin abinyi ta fara yi amma kuma acan kasan ranta tana jin tsoron mamanta domin bata mantawa tun kafin aurenta da jabir ma tace indai ta sake ta musulunta sai ta yankanta,
"Ohh my God" tafada gamida dafe goshinta, yanzu a yan kwanakin nan duk ta sauya hatta dabi'unta ma sun sauya ta daina sauraron wakokin da ada sune suka zame mata abin ji akoda yaushe sannan yanzu ta rage yawan karanta Bible dinta domin tunowa da tayi wata rana ta taba bawa jabir bible din sai yaki karba da ta matsa masa da maganar sai ya jiyo ya rike yan yatsunta yana mai fuskantarta,
"Goodness baya halatta agareni da na karanta bible bawai ina nufin ya zama haramun bane sai dai ni yanzu alqur'ani shine littafin da yafi cancanta da na rike kuma na karanta akoda yaushe saboda azamanin annabi Muhammad (S.A.W),annabi ya taba ganin sayyadina umar yana karanta wata takarda sai annabi yake tambayarsa menene wannan yake karantawa? Sai sayyadina Umar yace injila ce, wato wani dan yanki ne nacikin injila, anan sai fuskar annabi ta sauya zuwa fushi, ransa ya baci mutuka har yace da sayyadina Umar ko annabi Isah ne ya dawo awannan lokacin to wlhi dole yabishi yabi sunnarsa, atake sayyidana Umar ya nemi afuwar annabi yace bazai sake karantawa ba"
Zama tayi na dirshan tana tuno kyawawan halayen mijinta jabir, komai nashi mai nagarta he, bashida yawan hayaniya gashi ya rike addininsa da hannu bibbiyu, adan zaman da tayi dashi daga lokacin data fara hada makwanci dashi har zuwa wannan lokacin da yayi tafiya ta fahimci shi mutum ne mai mutukar tsoron Allah ga tarin ilimi akansa kamar ruwa, komai nashi Allah ga yawan bincike akan abubuwan da suka shafi addininsa, idanuwanta ta lumshe tana mai tuno da kyakkyawar surarsa wacce take mai daukar hankalin duk wata mace,
"To yanzu menene abin yi?" Ta tambayi kanta, Kodai babanta zataje ta fadawa? Ita dai tana son yanzu ta zama kamar jabir ta fuskar rayuwa,
Yayarta ta kira wato Anty Bilkisu tafada mata tana son ta karbi addinin musulunci, ba karamin murna anty Bilkisu tayiba domin dama addu'ar da ta dade tana yiwa goodness kenan na ta samu *Wani Haske* acikin rayuwarta,nan anty bilkisu ta bata shawara akan taje gida ta sanar da babansu tukunna,
Shiryawa tayi tabi shawarar Anty Bilkisu ta tafi gidan iyayenta, kamar kullum gidan babu kowa sai mahaifinta kadai wanda yake zaune a tsakar gidan ya shimfida tabarma yana kishingide yana sauraren radio,
Shigarta shigace ta mutumci domin bakar rigace ajikinta ta yafa bakin dan kwalin rigar, ko ba afada mata ba tasan ma tatafi church,
Agefen tabarmar ta zauna bayan sun gaisa tafara yiwa babanta bayani,
"Papa munyi magana da anty bilkisu ne nafada mata ina son zan musulunta shine tace inzo in sanar dakai"
Zaune baban nata ya tashi daga kishingidar da yayi, jin maganar yake kamar a mafarki wai goodness zata musulunta,
"Alhamdulillah, lallai Allah shine mai iko akan dukkanin komai, sannan kuma dama rahamar ubangiji haka take, wani baya musulunta sai har yaga wani mutum yana salla alhalin kuma ba aranar yafara ganin ana salla ba, wani kuma karatun alqur'ani zai ji sai kawai yayi sha'awar musulunci bayan ba ranar ya fara jin karatun qur'anin ba, kai koma dai menene to wannan wata babbar rahama ce daga Allah,
Goodness hakika ubangiji yasoki da rahama kuma yasoki da samun babban rabo acikin rayuwarki, yanzu abinda nake so dake shine kar ki yarda ki sanar da mahaifiyarki sannan kije gidan mahaifin jabir mijinki ki karbi musulunci agurin mahaifinsa, bana son mamanku tazo ta tarar dake agidan nan,ubangiji Allah yayi miki albarka yasake baki *Wani haske* acikin rayuwarki"
Mahaifinta yafada yana kwallar farin ciki, ita kanta goodness itama hawayen take yi, tashi tayi tafita ta koma gidanta, katoton dogon hijabin da Ummu al'amin ta bata ta dauko ta dorashi asaman doguwar rigarta ta tafi gidansu jabir,
A soro ta tarar da Malam mahaifin jabir, Malam yayi mamakin ganinta amma lokacin da yaji kudirinta sai mamakinsa ya sake karuwa gamida farin ciki, wanda har sai da hakoransa suka bayyana,
"Dafarko dai ina fata ba wani ra'ayine yasaki sha'awar karbar musulunci ba? Ina fatan zaki yi hakanne domin Allah saboda dukkan aiki sai da niyya shiyasa acikin hadisin da aka karbo daga Umar Allah ya kara masa yarda yace annabi Muhammad yace dukkan aiki sai da niyya sannan kowanne mutum akwai abinda yayi niyya, duk wanda yayi hijira domin Allah da manzonsa to sakamakon hijirarsa tana ga Allah da son manzonsa,wanda yayi hijira kuwa domin duniya ko wata k'awa, ko dan wata mace da zai aura to sakamakon hijirarsa tana ga abinda yayi hijira dominsa, shugaban masu rawaito hadisai ne ya rawaito wannan hadisin _(imamul muhaddasina)_"
Kanta ta daga "ba wani ne ya tilastani ba, kuma ba dan wani nayi hakan ba face dan Allah"
"To alhamdulillah, da farko dai ina son kisani shi musulunci yana nufin mika wuya ga Allah, da jawuwa agareshi da biyayya,da kuma tsarkakewa daga shirka,
Sannan shi musulunci yana da ginshikai guda biyar kamar yadda annabi Muhammad yafada acikin ingantaccen hadisi cewar angina musulunci akan abubuwa guda biyar, nafarko shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah sannan annabi Muhammad manzon Allahne, sai tsayar da salla, salla itace aiki nafarko da zafara bincikawa ranar tashin alqiyama, idan ta gyaru dukkan ayyuka sun gyaru idan kuma an samu sabanin haka to abin sai dai ace Allah ya kyauta,abu na uku shine azumin watan ramadan,
Amma babu tilas akan marar lafiya, ko kuma tsoho wanda shekarunsa suka ja ko kuma karamin yaro, ko matafiyi duk an samu rangwame akan wadannan mutanen,