Sashe 50
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna ci tana yi masa hira har suka kammala, zancen tafiyarshi ya fara yi mata anan tasake tayar masa da wani darun, kuka ta saka masa,
Janta yayi jikinsa yafara lashe fuskarta yana shanye hawayen da take yi, wata irin zazzafar soyayya yashiga nuna mata dolenta tayi shiru ta daina kukan,
Daukarta yayi yakaita cikin dakinshi ya ajiyeta akan tangamemen gadonshi yashiga nuna mata so.
Ajikinshi ya kwantar da ita yafara yi mata tausa adukkan bangarorin jikinta,iska yafara hura mata acikin kunnenta yana yimata kalamai masu dadi dan haka lokaci kankani bacci yayi awon gaba da ita.
Kwantar da ita yayi yatashi ahankali ya nufi toilet yayi wanka ya fito, cikin sauri sauri yayi shirinsa yasaka kayanshi ya debi dukkan muhimman abubuwanshi ya karasa Inda take kwance rungume da pillow ita ala dole shi ta rungume, sunkuyawa yayi ya kai bakinshi kan nata yayi mata kiss, yasake yi mata wani agoshinta sannan kumatunta sai nakarshe a tsakiyar kirjinta,
Jakarshi ya dauka yafita domin ya kusa makara saboda jirgin 4:30 zaibi zuwa Kaduna yanzu kuma gashi 4 harda yan mintuna ga baiyi salla ba.
Yana tafe yana waiwayenta har yafice daga cikin dakin, sai da ya tsaya a masallaci yayi salla sannan driver ya tafi kaishi airport, gaba daya jinsa yake yi babu dadi saboda zai tafi yabar bintinshi wacce yanzu yana jinta acikin ransa fiyeda yanda yake jin kanshi,kamar ya kirata awaya sai kuma ya rabuda ita yaga gwanda ya barta har sai ya sauka agarin Kaduna tukunna.
Bahijja kuwa tunda jabir yatafi yabarta take ta bacci kamar wacce jabir ya durawa maganin bacci, ba ita ta iya tashi ba sai wurin karfe 5:30, ahankali tafara bude idonta, ganinta tayi rungume da pillow amadadin jabir, ahankali ta tashi zaune sai kuma ta shagwabe fuska tafara kuka tana kiran
"Abbu...!" Ta kira sunanshi cikin shagwaba da kuka,
"Abbu...!" Jin shiru bai amsaba yasata tashi ta jawo towel dinshi ta daura ta leka cikin bathroom amma wayam baya ciki,
Fitowa tayi tana tafiya tana kuka tana kiransa, falo ta duba nanma baya nan, dakinshi ta sake dawowa ganin babu jakar data hada masa kayan tafiyarshi ya tabbatar mata da wayo yayi mata yai tafiyarsa,
Da kukanta ta shiga toilet tayi wanka tafito gashi ko salla bata yiba gashi jabir yau ya tara mata gajiya ba kadanba gashi baya nan, daurewa tayi ta daina kukan ta shirya tayi salla ta zauna tafara tasbihi har 6 tayi, alokacin taji kiran jabir awayarta,
Daukar wayar tayi bayan tafara kuka "abbu...!"
Jin muryarta ya tabbatar wa da jabir kuka take yi,
"Binti kukanne har yanzu baki daina ba?"
"Abbu shine ka tafi ka barni, kayi min wayo kasani bacci kafin natashi ka gudu"
Dan sansanyan murmushi jabir yayi yana mai tuno kyakkyawar fuskarta da dukkan kyakkyawar surarta wacce take tsumashi acikin kowanne irin yanayi,
"Ba gudu nayi na barki ba binti na, kiyi hakuri kinji, ba dadewa fa zanyi ba"
"Nidai bazan hakura ba sai dai idan ba zaka sake tafiya ka barni ba"
Kiss yayi mata ta cikin wayar "bazan sake ba binti wannan ma dan babu yanda zanyi ne amma bazan sakeba,i promised you my binti, ga sako nan naturo miki"
Murmushin itama tayi ta fara mayar masa da martanin kiss din da yayi mata,
"Binti kiyi hakuri ki bari haka kar kisa nakasa bacci"
Fuskarta tasoma gogewa sannan ahankali ta furta "abbu dan Allah kar ka kalli yanmata"
Dariya tasashi yi batare da ya shirya ba "binti ni ina ma zanga yanmata? Ina daki babu inda zanje daga daki sai ko dakin taron da zamu gudanar da conference din, ki kwantar da hankalinki kinji, daga ke babu kari kece yar auta awurina"
Tamkar yayi mata bishara da gidan aljanna haka taji, "abbu to yaushe zaka dawo?"
"Haba binti anyita nanata magana dayane? 3 days zanyi babu yawa"
Rufe idonta tayi tana tunanin yau ko a ina zata kwana,
"To abbu Allah ya kaimu"
"Amin binti, anjima zan kiraki kinji"
Kashe wayar tayi tana tunaninshi acikin zuciyarta.
Daren ranar bata iya bacci ba dakinta taje ta kwanta amma tunanin abbunta ya dameta, zaune ta tashi ta zubawa kan gadon ido tana nazari,
tattarawa tayi takoma dakin jabir ta kwanta amma kuma sam ta kasa baccin da zarar ta rufe idonta babu abinda take gani sai yanayin da suke kasancewa tare ako wanne lokacin bacci,idan kuma ta bude idonta sai ta rinka ganin kamar zata ganshi ne,
Daukar wayarta tayi tasoma laluben wayar jabir amma fuskarta sharkaf take da hawaye ohh bahijja irin wannan kuka haka sai kace pherty,
Jabir na daukar wayar yaji shasshekar kukanta "abbu nakasa bacci"
"Yi hakuri binti, kiyi alwala kiyi sallar nafila kinji, ko kin fara hutu?"
"Kai abbu yaushe nafara hutun naga dazuma kafin katafi kasan ina salla"
Murmushi yayi "ai tambayace binti, nasani ko nadace kwallona ya shiga raga"
"Kai abbu" tafada cikeda kunya,
"Ke binti" ya kwaikwayi maganarta, hakan da yayi ne yabata dariya,
Dariya take yi tana kyakyatawa kamar ba itace take kuka yanzu ba,
"Abbu ai al'amin ya ishemu"
"A'a binti al'amin dan ummu ne kema ki daure ki dage ki samu ki haifi naki,ko bakya son ki haifi mai kama da ni? Nafi son kema ki haihu ki zama mama"
Hannunta tasa ta toshe bakinta tana murmushi, cikin dabara ya samu ya rabata da damuwar da ta shiga, sun dade suna hira har tafara gyangyadi, addu'ar bacci yayi mata ta shafa ta kwanta taci gaba dayin wayar dashi yana bata labari mai dadi, shirun da yajine ya tabbatar masa da cewar tayi bacci, wayar ya kashe yana murmushi.
Kullum suna makale awaya dashi har yayi kwana ukun, aranar da zai dawo taje gidan kitso aka yarfo mata kananan kitso masu kyau harda wanda aka zubo mata shi gaban goshinta aka tufke mata shi,
Rasa inda zata saka kanta tayi dan tsananin murna, alla alla takeyi kawai ya dawo ta ganshi saboda tayi missing dinshi ba kadan ba.
Karfe 2:30 ya sauka amma baije gida ba office yawuce tunda ya sanar da ita saukarsa taji kamar tayi tsuntsuwa taje ta daukoshi, jin yatafi office yasata kasa hakuri har saida ta aika masa da lafiyayyen girkin da tayi masa. Sai da yasha aiki a office har 5 tayi sannan ya tashi ya nufi gida,
Yana zuwa gidan sashen bahijja yafara shiga amma ko ina ya duba bata nan dan haka ya fita ya nufi nasa sashen, tunda ya shiga falon yake shakar kamshi mai dadi yana tashi afalon,
Jakarshi ya ajiye ya tasamma cikin bedroom dinshi, abin mamaki nanma bata ciki juyawa yayi zai fita amma aranshi yana tunanin to ina bahijja ta tafi, jinta yayi dalaf ta daleshi tana murna,
"Oyoyo abbuna"
Makaleta yayi ya nufi gaban mirror ya tsaya yana hangota ta cikin mudubin, wata kwalliya tasha tayi kyau sosai tayi kwalliya sosai cikin yar bingilar pink din rigarta da bakin wando matsattse,
Birkitota yayi yafara kallon kitson kanta yana shafashi,
"Waye yayi miki wannan kitson? Yayi kyau"
"Nagode abbu, agidan kitsone can baya"
"To zan bada tukwici yanzun nan"
Bata ankaraba taji yayi sama da ita bai direta ako inaba sai akan makeken gadonshi.
Basu iya barin junansu ba sai daf da sallar magrib, daukarta yayi zuwa bathroom yayi mata wanka yayi mata alwala ya dawo da ita cikin dakin, ita dai duk kunya ta gama rufeta,
"Daga dawowa ko gaisawa ba muyi ba kika rikitani da soyayyarki" yafada cikin tsokana yana kokarin daura mata towel,
"Ayya abbu ai laifinka ne ba nawa ba" rufe fuskarta tayi bayan tagama maganar,
"Nagode miki sosai kuma naji dadi Allah ya yi miki albarka binti"
"Amin abbu, nagode"
Shiryawa yayi agurguje ya saka jallabiya kalar ruwan toka ya tafi masallaci bayan ya shiryata itama.
Haka rayuwa taci gaba da kasance musu cikin farin ciki da annashuwa gashi kullum cikin kyautatawa junansu suke, ita dai bahijja bata da damuwar komai sai ta mahaifiyarta domin kullum abin sake tabarbarewa yake babu sauki saima gaba da yakeyi, duk lokacin da taje gidan bata samun sakin fuska awurin ma sai ko wurin mahaifinta.
Cikin wannan yanayine jabir yayi musu shirin zuwa madina domin suyi umarah sannan su ziyarci su ummu al'amin saboda rabonsa dasu yanzu ankusa shekara saura yan watanni,
Lokacin da bahijja taji wannan albishir din ba karamin murna tayi ba anan suka shiga yin shirin tafiya bayan duk abinda zasu bukata natafiya ya kammalu, sai da suka je suka yiwa dukkan wand yacancanta sallama sannan suka daga kowannensu zuciyarsa dauke da murna musamman ma bahijja.
Acikin jirgi ajikin jabir ta lafe ta makaleshi gam tana muzurai sai aikin hararar wata mata take yi wacce ke gefen jabir azaune tana satar kallonshi,
"Abbu jiyo da fuskarka nan" tafada gamida saka hannunta ta jiyo da fuskarshi zuwa kusa da tata,
"Menene binti?" Ya tambayeta yana dora idanuwansa kan nata,
"Gani nayine sai kallonka ake tayi kai kadai sai kace babu wani namiji anan sai kai daya" tafadi hakan cikeda kishi,
"Binti dadina dake kishi, kinada kishi sosai tun kafin kisan abinda ake yiwa kishin,bare yanzu da kika sani"
Idonta ta sauke ta kwantar da kanta akan kafadarshi tana murmushi, hirarsu suka ci gaba dayi har Allah ya saukesu acikin madina,
Lokacin da suka fito suka hango al'amin da ummunshi tsaye suna jiran isowarsu, kallon kallo aka fara yi tun daga nesa tsakanin ummu da bahijja,
Hannunta rike cikin na jabir tasha bakar doguwar Arabian gown sannan ta yane kanta da bakin mayafin rigar, ba karamin kyau ta sake yi ba,
Ita dinma bahijjan shigar da ummun tayi take kallo domin bakar doguwar riga irinta larabawa tasaka da dan karamin hijab, hannunta rikeda na al'amin, ko ba a fadawa Ummu ba tasan bahijja ta musulunta domin ta tabbatar da ace bata musulunta ba to da babu abinda zai saka jabir yazo da ita,
Ahankali suke tafiya har suka karasa inda su ummu ke tsaye, da gudu al'amin ya fusge yaje ya rungume bahijja yana murna, ita dinma rungumeshi tayi ta dagashi ta saba akafadarta duk kuwa da cewar yanzu ya dan kara girma,
Dukkaninsu daga ummun har jabir tsayawa suka yi suna kallon al'amin da bahijja saboda yadda suka manta dasu sai dariya suke yi suna kara rungume juna,
"Anty ashe dama kema zaki zo? Anty kema kina salla yanzu ko?"
Janta yayi jikinsa yafara lashe fuskarta yana shanye hawayen da take yi, wata irin zazzafar soyayya yashiga nuna mata dolenta tayi shiru ta daina kukan,
Daukarta yayi yakaita cikin dakinshi ya ajiyeta akan tangamemen gadonshi yashiga nuna mata so.
Ajikinshi ya kwantar da ita yafara yi mata tausa adukkan bangarorin jikinta,iska yafara hura mata acikin kunnenta yana yimata kalamai masu dadi dan haka lokaci kankani bacci yayi awon gaba da ita.
Kwantar da ita yayi yatashi ahankali ya nufi toilet yayi wanka ya fito, cikin sauri sauri yayi shirinsa yasaka kayanshi ya debi dukkan muhimman abubuwanshi ya karasa Inda take kwance rungume da pillow ita ala dole shi ta rungume, sunkuyawa yayi ya kai bakinshi kan nata yayi mata kiss, yasake yi mata wani agoshinta sannan kumatunta sai nakarshe a tsakiyar kirjinta,
Jakarshi ya dauka yafita domin ya kusa makara saboda jirgin 4:30 zaibi zuwa Kaduna yanzu kuma gashi 4 harda yan mintuna ga baiyi salla ba.
Yana tafe yana waiwayenta har yafice daga cikin dakin, sai da ya tsaya a masallaci yayi salla sannan driver ya tafi kaishi airport, gaba daya jinsa yake yi babu dadi saboda zai tafi yabar bintinshi wacce yanzu yana jinta acikin ransa fiyeda yanda yake jin kanshi,kamar ya kirata awaya sai kuma ya rabuda ita yaga gwanda ya barta har sai ya sauka agarin Kaduna tukunna.
Bahijja kuwa tunda jabir yatafi yabarta take ta bacci kamar wacce jabir ya durawa maganin bacci, ba ita ta iya tashi ba sai wurin karfe 5:30, ahankali tafara bude idonta, ganinta tayi rungume da pillow amadadin jabir, ahankali ta tashi zaune sai kuma ta shagwabe fuska tafara kuka tana kiran
"Abbu...!" Ta kira sunanshi cikin shagwaba da kuka,
"Abbu...!" Jin shiru bai amsaba yasata tashi ta jawo towel dinshi ta daura ta leka cikin bathroom amma wayam baya ciki,
Fitowa tayi tana tafiya tana kuka tana kiransa, falo ta duba nanma baya nan, dakinshi ta sake dawowa ganin babu jakar data hada masa kayan tafiyarshi ya tabbatar mata da wayo yayi mata yai tafiyarsa,
Da kukanta ta shiga toilet tayi wanka tafito gashi ko salla bata yiba gashi jabir yau ya tara mata gajiya ba kadanba gashi baya nan, daurewa tayi ta daina kukan ta shirya tayi salla ta zauna tafara tasbihi har 6 tayi, alokacin taji kiran jabir awayarta,
Daukar wayar tayi bayan tafara kuka "abbu...!"
Jin muryarta ya tabbatar wa da jabir kuka take yi,
"Binti kukanne har yanzu baki daina ba?"
"Abbu shine ka tafi ka barni, kayi min wayo kasani bacci kafin natashi ka gudu"
Dan sansanyan murmushi jabir yayi yana mai tuno kyakkyawar fuskarta da dukkan kyakkyawar surarta wacce take tsumashi acikin kowanne irin yanayi,
"Ba gudu nayi na barki ba binti na, kiyi hakuri kinji, ba dadewa fa zanyi ba"
"Nidai bazan hakura ba sai dai idan ba zaka sake tafiya ka barni ba"
Kiss yayi mata ta cikin wayar "bazan sake ba binti wannan ma dan babu yanda zanyi ne amma bazan sakeba,i promised you my binti, ga sako nan naturo miki"
Murmushin itama tayi ta fara mayar masa da martanin kiss din da yayi mata,
"Binti kiyi hakuri ki bari haka kar kisa nakasa bacci"
Fuskarta tasoma gogewa sannan ahankali ta furta "abbu dan Allah kar ka kalli yanmata"
Dariya tasashi yi batare da ya shirya ba "binti ni ina ma zanga yanmata? Ina daki babu inda zanje daga daki sai ko dakin taron da zamu gudanar da conference din, ki kwantar da hankalinki kinji, daga ke babu kari kece yar auta awurina"
Tamkar yayi mata bishara da gidan aljanna haka taji, "abbu to yaushe zaka dawo?"
"Haba binti anyita nanata magana dayane? 3 days zanyi babu yawa"
Rufe idonta tayi tana tunanin yau ko a ina zata kwana,
"To abbu Allah ya kaimu"
"Amin binti, anjima zan kiraki kinji"
Kashe wayar tayi tana tunaninshi acikin zuciyarta.
Daren ranar bata iya bacci ba dakinta taje ta kwanta amma tunanin abbunta ya dameta, zaune ta tashi ta zubawa kan gadon ido tana nazari,
tattarawa tayi takoma dakin jabir ta kwanta amma kuma sam ta kasa baccin da zarar ta rufe idonta babu abinda take gani sai yanayin da suke kasancewa tare ako wanne lokacin bacci,idan kuma ta bude idonta sai ta rinka ganin kamar zata ganshi ne,
Daukar wayarta tayi tasoma laluben wayar jabir amma fuskarta sharkaf take da hawaye ohh bahijja irin wannan kuka haka sai kace pherty,
Jabir na daukar wayar yaji shasshekar kukanta "abbu nakasa bacci"
"Yi hakuri binti, kiyi alwala kiyi sallar nafila kinji, ko kin fara hutu?"
"Kai abbu yaushe nafara hutun naga dazuma kafin katafi kasan ina salla"
Murmushi yayi "ai tambayace binti, nasani ko nadace kwallona ya shiga raga"
"Kai abbu" tafada cikeda kunya,
"Ke binti" ya kwaikwayi maganarta, hakan da yayi ne yabata dariya,
Dariya take yi tana kyakyatawa kamar ba itace take kuka yanzu ba,
"Abbu ai al'amin ya ishemu"
"A'a binti al'amin dan ummu ne kema ki daure ki dage ki samu ki haifi naki,ko bakya son ki haifi mai kama da ni? Nafi son kema ki haihu ki zama mama"
Hannunta tasa ta toshe bakinta tana murmushi, cikin dabara ya samu ya rabata da damuwar da ta shiga, sun dade suna hira har tafara gyangyadi, addu'ar bacci yayi mata ta shafa ta kwanta taci gaba dayin wayar dashi yana bata labari mai dadi, shirun da yajine ya tabbatar masa da cewar tayi bacci, wayar ya kashe yana murmushi.
Kullum suna makale awaya dashi har yayi kwana ukun, aranar da zai dawo taje gidan kitso aka yarfo mata kananan kitso masu kyau harda wanda aka zubo mata shi gaban goshinta aka tufke mata shi,
Rasa inda zata saka kanta tayi dan tsananin murna, alla alla takeyi kawai ya dawo ta ganshi saboda tayi missing dinshi ba kadan ba.
Karfe 2:30 ya sauka amma baije gida ba office yawuce tunda ya sanar da ita saukarsa taji kamar tayi tsuntsuwa taje ta daukoshi, jin yatafi office yasata kasa hakuri har saida ta aika masa da lafiyayyen girkin da tayi masa. Sai da yasha aiki a office har 5 tayi sannan ya tashi ya nufi gida,
Yana zuwa gidan sashen bahijja yafara shiga amma ko ina ya duba bata nan dan haka ya fita ya nufi nasa sashen, tunda ya shiga falon yake shakar kamshi mai dadi yana tashi afalon,
Jakarshi ya ajiye ya tasamma cikin bedroom dinshi, abin mamaki nanma bata ciki juyawa yayi zai fita amma aranshi yana tunanin to ina bahijja ta tafi, jinta yayi dalaf ta daleshi tana murna,
"Oyoyo abbuna"
Makaleta yayi ya nufi gaban mirror ya tsaya yana hangota ta cikin mudubin, wata kwalliya tasha tayi kyau sosai tayi kwalliya sosai cikin yar bingilar pink din rigarta da bakin wando matsattse,
Birkitota yayi yafara kallon kitson kanta yana shafashi,
"Waye yayi miki wannan kitson? Yayi kyau"
"Nagode abbu, agidan kitsone can baya"
"To zan bada tukwici yanzun nan"
Bata ankaraba taji yayi sama da ita bai direta ako inaba sai akan makeken gadonshi.
Basu iya barin junansu ba sai daf da sallar magrib, daukarta yayi zuwa bathroom yayi mata wanka yayi mata alwala ya dawo da ita cikin dakin, ita dai duk kunya ta gama rufeta,
"Daga dawowa ko gaisawa ba muyi ba kika rikitani da soyayyarki" yafada cikin tsokana yana kokarin daura mata towel,
"Ayya abbu ai laifinka ne ba nawa ba" rufe fuskarta tayi bayan tagama maganar,
"Nagode miki sosai kuma naji dadi Allah ya yi miki albarka binti"
"Amin abbu, nagode"
Shiryawa yayi agurguje ya saka jallabiya kalar ruwan toka ya tafi masallaci bayan ya shiryata itama.
Haka rayuwa taci gaba da kasance musu cikin farin ciki da annashuwa gashi kullum cikin kyautatawa junansu suke, ita dai bahijja bata da damuwar komai sai ta mahaifiyarta domin kullum abin sake tabarbarewa yake babu sauki saima gaba da yakeyi, duk lokacin da taje gidan bata samun sakin fuska awurin ma sai ko wurin mahaifinta.
Cikin wannan yanayine jabir yayi musu shirin zuwa madina domin suyi umarah sannan su ziyarci su ummu al'amin saboda rabonsa dasu yanzu ankusa shekara saura yan watanni,
Lokacin da bahijja taji wannan albishir din ba karamin murna tayi ba anan suka shiga yin shirin tafiya bayan duk abinda zasu bukata natafiya ya kammalu, sai da suka je suka yiwa dukkan wand yacancanta sallama sannan suka daga kowannensu zuciyarsa dauke da murna musamman ma bahijja.
Acikin jirgi ajikin jabir ta lafe ta makaleshi gam tana muzurai sai aikin hararar wata mata take yi wacce ke gefen jabir azaune tana satar kallonshi,
"Abbu jiyo da fuskarka nan" tafada gamida saka hannunta ta jiyo da fuskarshi zuwa kusa da tata,
"Menene binti?" Ya tambayeta yana dora idanuwansa kan nata,
"Gani nayine sai kallonka ake tayi kai kadai sai kace babu wani namiji anan sai kai daya" tafadi hakan cikeda kishi,
"Binti dadina dake kishi, kinada kishi sosai tun kafin kisan abinda ake yiwa kishin,bare yanzu da kika sani"
Idonta ta sauke ta kwantar da kanta akan kafadarshi tana murmushi, hirarsu suka ci gaba dayi har Allah ya saukesu acikin madina,
Lokacin da suka fito suka hango al'amin da ummunshi tsaye suna jiran isowarsu, kallon kallo aka fara yi tun daga nesa tsakanin ummu da bahijja,
Hannunta rike cikin na jabir tasha bakar doguwar Arabian gown sannan ta yane kanta da bakin mayafin rigar, ba karamin kyau ta sake yi ba,
Ita dinma bahijjan shigar da ummun tayi take kallo domin bakar doguwar riga irinta larabawa tasaka da dan karamin hijab, hannunta rikeda na al'amin, ko ba a fadawa Ummu ba tasan bahijja ta musulunta domin ta tabbatar da ace bata musulunta ba to da babu abinda zai saka jabir yazo da ita,
Ahankali suke tafiya har suka karasa inda su ummu ke tsaye, da gudu al'amin ya fusge yaje ya rungume bahijja yana murna, ita dinma rungumeshi tayi ta dagashi ta saba akafadarta duk kuwa da cewar yanzu ya dan kara girma,
Dukkaninsu daga ummun har jabir tsayawa suka yi suna kallon al'amin da bahijja saboda yadda suka manta dasu sai dariya suke yi suna kara rungume juna,
"Anty ashe dama kema zaki zo? Anty kema kina salla yanzu ko?"