Sashe 46
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Har azahar jabir yana asibitin sai wurin karfe biyu narana sannan yatafi da niyyar zai dawo anjima, suna fita shida driver yaje cikin gari ya bayar aka karbo abinci awani restaurant yabayar aka kai musu bayan driver ya ajiyeshi agida, shi yau kwata kwata ma baici abinci ba tunda ya tashi da safe dama zama da yunwa sabonshi ne domin a office haka yake wuni har yamma baici komai ba shiyasa yake yawan yin azumi,
Kasancewar duk suna cikin damuwa babu wanda ya samu damar cin abincin da aka kai musu, suna nan zaune sunyi jungum jungum dr yafito yace musu ta farfado zasu iya shiga su ganta,
Tashi sukayi da hanzari dukkaninsu suka fada dakin da ma take ciki suna shiga suka sameta kwance idanuwanta abude tana kallon kofa, tana ganin bahijja ta mayar da idonta ta rufe ruf tana mai jin wani irin daci acikin ranta,
Duk wanda yayi mata sannu tana daga masa kai amma koda bahijja tayi mata sai taki kulawa, nan hankalin bahijja ya tashi dama wannan ranar ta yau ta dade tana jin tsoron zuwanta saboda tasan ma zata tsaneta zata kyamaceta uwa uba zata raba hanya da ita,
Wuri suka samu suka zazzauna acikin dakin har la'asar tayi lokacin jabir ya dawo asibitin suna dakin ya shiga ya samesu, wani kololon bakin cikine ya ziyarci ma, aranta tana tunanin yanzu shikenan wannan yaron yayi nasara akanta ya musuluntar da bahijja duk da dadewar da tayi tana dorata akan addinin kiristanci, runtse idanuwanta tayi saboda bata son ganin fuskarsa ko kadan,
Kwata kwata taki amsa sannun da jabir yake yi mata, gaban papa ya karasa ya dan russuna ya zaro kudi daga cikin aljihunsa rafa daya ya bashi domin yin hidimar siyan magunguna sannan ga kaya iri iri da driver ya fara shigowa dasu irin wadanda marar lafiya zai bukata,
Godiya da addu'a jabir yashata agun papa ga albarka da yayita saka masa da addu'ar Allah ya bashi yara nagari, duk da nauyin da yakeji sai da ya amsa da amin yana kallon bahijja kasa kasa, itama dago idonta tayi ta kalleshi tana mai jin mamakin amin din da yace.
K'arfe 10:30 babansu yace tabi mijinta su tafi shida Bilkisu ne zasu zauna a asibitin inyaso gobe ta dawo da safe, bata so hakanba amma haka tafita duk ranta a hargitsi domin ta shiga damuwa sakamakon ganin fushin da ma take yi da ita,
Tun acikin mota jabir ya fara rarrashinta saboda shima ya fuskanci akwai matsala, akan cinyarshi ta kwantar da kanta tana hawaye amma bata bari ya sani ba, kanta ya soma shafawa yana cewa
"Me kike sha'awar ci muje in siya miki?"
Girgiza kai tayi alamun babu komai "to ai naga kema baki ci abincin ba kodai sai nayi miki dura idan munje gida?"
Kafada ta mak'e tana girgiza kanta.
Suna zuwa gida sashenta ta wuce taje tayi wanka tasaka kayan bacci amma har lokacin ranta babu dadi, wayarta ce tafara kara tana dubawa taga jabir ne yake kiranta,
Asanyaye ta daga wayar, "binti me kikeyi ne najiki shiru?"
"Abbu kabarni na kwana adakina yau" tafada idanuwanta cikeda kwalwa,
"To zan barki amma kafin kiyi baccin kizo ki karbi wani abu"
Kashe wayar tayi ta tashi tafita ta nufi part dinsa, acikin bedroom dinshi ta sameshi zaune shima da kayan baccin ajikinsa yana gauraya wani abu acikin Kofi, kusa dashi ta karasa ta zauna,
"Gani abbu"
"Naganki ai binti, zauna mana nagama"
Cup din ya kai saitin bakinta,"ungo sha malt ne da peak saboda naga baki ci abinci ba, jibi har kinyi kashin wuya yau kadai"
Hannunshi yakai yafara shafar wuyanta yana kallon fuskarta, bude baki tayi ta runtse ido takama cup din tafara shan maltina din, kadan ta rage aciki,
"Wannan kuma ni kika barwa?"
Yafada kanshi akasa dagowar da zaiyi yaganta tana kokarin yin kuka,
"Wai wannan kukan na menene?" Yace da ita bayan ya dauketa cak ya dorata kan cinyarsa,
"Abbu ma tana fushi dani ko amsa sannun da nayi mata bata yi ba" kukane ya subuce mata, rasa yanda zaiyi mata yayi hakan ya sanyashi kwantar da ita agefen gadon yashiga jikinta yasa dan mitsitsin bakinshi cikin nata yafara shan bakinta.
Yajima yana yi mata wasu abubuwa na kwantar da hankali kafin ya kwantar da ita akan jikinsa ya dora kanta asaman kirjinsa yana shafar gadon bayanta ahankali,
"Kinyi wanka da ruwan dumi kuwa?" Ya tambayeta yana kissing din hannunta,
"Abbu nayi amma har yanzu dai banji daidai ba"
"Sorry kinji, zaki warware"
Hannunshi ta makale acikin nata tana matsawa,
"Abbu ma ko kallona yau batayi ba"
Gashin kanta yafara shafawa,
"Babu komai binti insha Allah wata rana zata gane gaskiya itama, ko baki da labarin kissar annabi ibrahim wanda mahaifinsa ya kasance mai bautar gumaka, alhalin shi kuma yana matsayin annabin Allah"
Sake shigewa cikin jikinsa tayi tana kara kankameshi sosai kamar wanda take tsoron yatafi ya barta,
"Haka Allah yake ikonsa abbu,shi annabi ibrahim gashi annabin Allah amma kuma mahaifinsa yana karyata abinda yazo dashi"
Dan yatsanta yafara murzawa cikin nashi,
"Kuma kinga har tallar gumaka mahaifinsa yake bashi amma bai taba bujirewa umarninsa ba, haka yake dauka yatafi tallen gashi kuma gunkin da ake sassakawa agidansu annabi ibrahim yafi na kowanne gida kyau, kullum yiwa mahaifinsa nasiha yake kan kar ya biyewa shaidan yana bautar wanin Allah,kuma daidai da rana daya bai taba sabawa umarnin mahaifinsa ba domin su iyaye ko wanne irine wajibi ne ayi musu biyaya,duk nasihar da annabi ibrahim yayiwa mahaifinsa bai saurareshi ba, kinsan mutum baya shiryar da wani, shiriya ta Allah ce"
Juyi tayi atsakiyar jikinsa takai hannunta daya ta shafo fuskarsa,
"Abbu bacci, kaci gaba da bani labarin idan kaji shiru kuma shikenan nayi bacci"
Sunbatar goshinta yayi yana murmushi, "ai kuwa ba za ayi haka ba, nima gara kawai nayi shirun tunda na fuskanci wayo kike kokarin yimin"
"A'a abbu bafa wayo bane"
Kanta yaci gaba da shafawa yana bata labarin har bacci ya dauketa, rungumeta yayi sosai acikin jikinsa yana tuno lokuta da dama wadanda suka kasance atare.
Washe gari da sassafe ta tashi ta shirya abin karyawa harda wanda zata kai asibiti, tare suka tafi da jabir sai da ya shiga ya duba jikin ma sannan yayi musu sallama ya wuce office, yauma kamar jiya ma bata kulata ba har lokacin tafiyarta yayi tatafi, ahaka har sai da akayi sati daya lokacin har sauki yafara samuwa awurin ma amma sam taki kula bahijja domin ko gaisuwarta bata amsawa,
Arana ta bakwai ce ma ta tsigaleta tatas tace kuma ko mutuwa tayi bata yarda taje inda gawarta take ba sannan ba ita ba ita har duniya ta tashi,
Da kuka bahijja tafita taje ta zauna awata runfa taci gaba da kukanta, anty bilkisu ce ta biyota tazo tafara bata baki tana cewa tayi hakuri sannan ta kara da cewa
"Karki saka damuwa acikin ranki domin ba ason mace mai juna biyu ta rinka damuwa hakan zai iya shafar har abinda ke cikin cikinta"
Murmushi tayi wanda bata shirya yinsa ba saboda jin maganar anty Bilkisu,
"Tab ni tunda naje gidanma sau daya akayi wani abu" tafada acikin zuciyarta ashe afili tayi maganar batare data saniba, cikin takaici anty bilkisu ta kalleta,
"Ashe dama duk abubuwan dana dade ina sanar miki baya shiga kunnuwanki,ke kuwa me kika zauna yi? Me kika tsinana agidan? Sau daya? Amma wlh kin bani kunya, banyi zaton sakalcinki da asarancinki yakai haka ba"
Hawayen idonta ta goge ta kalli anty bilkisu "to anty ya zanyi? Shi abbu ayanda na fahinceshi bashida yawan bukatar mace"
Girgiza kai anty bilkisu tayi cikeda bacin rai, "shine ke kuma kika barshi ahaka? Bari kiji ya kamata ki tashi atsaye ki bawa mijinki gudunmawa da kulawa ta musamman, bai kamata ki zuba masa ido kice wai har sai lokacin da yaji bukatarki ya nemeki ba, yanzu wannan ba shine wayewaba, akwai dabaru da salo wanda ya kamata ki koya musamman ma yanzu da kika fuskanci mijinki ko wanne irine, dama maza masu sanyin nan ai haka suke basuda yawan bukatar mace gasu da saurin biyan bukatarsu, dan haka wlh kece ya kamata ki zauna ku fuskanci juna ki gyarashi, ta hanyar yi masa kwalliya mai daukar hankali da sauran abubuwan da zasu jawo miki ra'ayinsa gareki, sannan ina son ki riki ruwan zafi domin duk macen da take amfani da ruwan zafi to tana dauke da wata ni'ima ta musamman, asalima ruwan sanyi bashida wani amfani ajikin ya mace, ita mace anfi son koda wanne lokaci ta kasance cikin dumi shiyasa yin lalle na asali yake da amfani domin shi yafi komai dawowa da mace dumin jikinta sannan kuma yana kewayawa har cikin jinin jikinta yana wanke mata kwayoyin cuta musamman ma cutukan dake cikin mara, idan kina son ki gane haka to ki gwada yin lalle ki kwana dashi, da safe idan kinje yin fitsari ki kula sosai zaki ga fitsarin ya sauya kala yayi kalar lallen sannan kuma har warin lallen zakiji fitsarin yanayi"
Kai ta daga tana kallon anty bilkisu wacce ta dage tana koro mata bayani,
"Ni anty duk banida bukatar wadannan kawai nidai burina abbu ya sauya daga wannan sanyin nashi, wlh yanda kika ganshin nan yana tafiya ahankali to acanma hakan yakeyi"
"To kin San ya zakiyi? Gaskiya zama zakuyi kuyi magana ku fuskanci juna keda shi, wannan ba matsalar da zakiyi shiru bace domin kanki zaki cuta,kedai kawai ki tabbatar kina gyara jikinki, ki yawaita shan kanumfari domin yana gyara mace kuma yana hana fitsarinta yin zarni, duk macen datake amfani da kanumfari to zaka ji tana wani kamshi har fitsarinta kamshin kanumfarin zakaji yana yi, haka kuma shan kunun alkama da zuma da madara yana gyarawa mace jikinta sosai da sosai sannan yana saukar mata da wasu sinadirai ajikinta, shi kansa shan ruwan zafi wani abune mai mutukar amfani ajikin mace daga mace har namiji anfi son susha ruwan zafi lokacin da zasu gudanar da mu'amular auratayya"
"Nagode Anty, insha Allahu zan kiyaye, amma ni kunshin zan gwada yi nagani"
"Hakan yanada kyau sister ki gwada kiga"
Suna nan zaune suna tattaunawa har la'asar tayi lis, 5 jabir yazo asibitin, shima dakyar ma ta iya amsa gaisuwarsa amma daga nan bata kara yi masa magana,
Kasancewar duk suna cikin damuwa babu wanda ya samu damar cin abincin da aka kai musu, suna nan zaune sunyi jungum jungum dr yafito yace musu ta farfado zasu iya shiga su ganta,
Tashi sukayi da hanzari dukkaninsu suka fada dakin da ma take ciki suna shiga suka sameta kwance idanuwanta abude tana kallon kofa, tana ganin bahijja ta mayar da idonta ta rufe ruf tana mai jin wani irin daci acikin ranta,
Duk wanda yayi mata sannu tana daga masa kai amma koda bahijja tayi mata sai taki kulawa, nan hankalin bahijja ya tashi dama wannan ranar ta yau ta dade tana jin tsoron zuwanta saboda tasan ma zata tsaneta zata kyamaceta uwa uba zata raba hanya da ita,
Wuri suka samu suka zazzauna acikin dakin har la'asar tayi lokacin jabir ya dawo asibitin suna dakin ya shiga ya samesu, wani kololon bakin cikine ya ziyarci ma, aranta tana tunanin yanzu shikenan wannan yaron yayi nasara akanta ya musuluntar da bahijja duk da dadewar da tayi tana dorata akan addinin kiristanci, runtse idanuwanta tayi saboda bata son ganin fuskarsa ko kadan,
Kwata kwata taki amsa sannun da jabir yake yi mata, gaban papa ya karasa ya dan russuna ya zaro kudi daga cikin aljihunsa rafa daya ya bashi domin yin hidimar siyan magunguna sannan ga kaya iri iri da driver ya fara shigowa dasu irin wadanda marar lafiya zai bukata,
Godiya da addu'a jabir yashata agun papa ga albarka da yayita saka masa da addu'ar Allah ya bashi yara nagari, duk da nauyin da yakeji sai da ya amsa da amin yana kallon bahijja kasa kasa, itama dago idonta tayi ta kalleshi tana mai jin mamakin amin din da yace.
K'arfe 10:30 babansu yace tabi mijinta su tafi shida Bilkisu ne zasu zauna a asibitin inyaso gobe ta dawo da safe, bata so hakanba amma haka tafita duk ranta a hargitsi domin ta shiga damuwa sakamakon ganin fushin da ma take yi da ita,
Tun acikin mota jabir ya fara rarrashinta saboda shima ya fuskanci akwai matsala, akan cinyarshi ta kwantar da kanta tana hawaye amma bata bari ya sani ba, kanta ya soma shafawa yana cewa
"Me kike sha'awar ci muje in siya miki?"
Girgiza kai tayi alamun babu komai "to ai naga kema baki ci abincin ba kodai sai nayi miki dura idan munje gida?"
Kafada ta mak'e tana girgiza kanta.
Suna zuwa gida sashenta ta wuce taje tayi wanka tasaka kayan bacci amma har lokacin ranta babu dadi, wayarta ce tafara kara tana dubawa taga jabir ne yake kiranta,
Asanyaye ta daga wayar, "binti me kikeyi ne najiki shiru?"
"Abbu kabarni na kwana adakina yau" tafada idanuwanta cikeda kwalwa,
"To zan barki amma kafin kiyi baccin kizo ki karbi wani abu"
Kashe wayar tayi ta tashi tafita ta nufi part dinsa, acikin bedroom dinshi ta sameshi zaune shima da kayan baccin ajikinsa yana gauraya wani abu acikin Kofi, kusa dashi ta karasa ta zauna,
"Gani abbu"
"Naganki ai binti, zauna mana nagama"
Cup din ya kai saitin bakinta,"ungo sha malt ne da peak saboda naga baki ci abinci ba, jibi har kinyi kashin wuya yau kadai"
Hannunshi yakai yafara shafar wuyanta yana kallon fuskarta, bude baki tayi ta runtse ido takama cup din tafara shan maltina din, kadan ta rage aciki,
"Wannan kuma ni kika barwa?"
Yafada kanshi akasa dagowar da zaiyi yaganta tana kokarin yin kuka,
"Wai wannan kukan na menene?" Yace da ita bayan ya dauketa cak ya dorata kan cinyarsa,
"Abbu ma tana fushi dani ko amsa sannun da nayi mata bata yi ba" kukane ya subuce mata, rasa yanda zaiyi mata yayi hakan ya sanyashi kwantar da ita agefen gadon yashiga jikinta yasa dan mitsitsin bakinshi cikin nata yafara shan bakinta.
Yajima yana yi mata wasu abubuwa na kwantar da hankali kafin ya kwantar da ita akan jikinsa ya dora kanta asaman kirjinsa yana shafar gadon bayanta ahankali,
"Kinyi wanka da ruwan dumi kuwa?" Ya tambayeta yana kissing din hannunta,
"Abbu nayi amma har yanzu dai banji daidai ba"
"Sorry kinji, zaki warware"
Hannunshi ta makale acikin nata tana matsawa,
"Abbu ma ko kallona yau batayi ba"
Gashin kanta yafara shafawa,
"Babu komai binti insha Allah wata rana zata gane gaskiya itama, ko baki da labarin kissar annabi ibrahim wanda mahaifinsa ya kasance mai bautar gumaka, alhalin shi kuma yana matsayin annabin Allah"
Sake shigewa cikin jikinsa tayi tana kara kankameshi sosai kamar wanda take tsoron yatafi ya barta,
"Haka Allah yake ikonsa abbu,shi annabi ibrahim gashi annabin Allah amma kuma mahaifinsa yana karyata abinda yazo dashi"
Dan yatsanta yafara murzawa cikin nashi,
"Kuma kinga har tallar gumaka mahaifinsa yake bashi amma bai taba bujirewa umarninsa ba, haka yake dauka yatafi tallen gashi kuma gunkin da ake sassakawa agidansu annabi ibrahim yafi na kowanne gida kyau, kullum yiwa mahaifinsa nasiha yake kan kar ya biyewa shaidan yana bautar wanin Allah,kuma daidai da rana daya bai taba sabawa umarnin mahaifinsa ba domin su iyaye ko wanne irine wajibi ne ayi musu biyaya,duk nasihar da annabi ibrahim yayiwa mahaifinsa bai saurareshi ba, kinsan mutum baya shiryar da wani, shiriya ta Allah ce"
Juyi tayi atsakiyar jikinsa takai hannunta daya ta shafo fuskarsa,
"Abbu bacci, kaci gaba da bani labarin idan kaji shiru kuma shikenan nayi bacci"
Sunbatar goshinta yayi yana murmushi, "ai kuwa ba za ayi haka ba, nima gara kawai nayi shirun tunda na fuskanci wayo kike kokarin yimin"
"A'a abbu bafa wayo bane"
Kanta yaci gaba da shafawa yana bata labarin har bacci ya dauketa, rungumeta yayi sosai acikin jikinsa yana tuno lokuta da dama wadanda suka kasance atare.
Washe gari da sassafe ta tashi ta shirya abin karyawa harda wanda zata kai asibiti, tare suka tafi da jabir sai da ya shiga ya duba jikin ma sannan yayi musu sallama ya wuce office, yauma kamar jiya ma bata kulata ba har lokacin tafiyarta yayi tatafi, ahaka har sai da akayi sati daya lokacin har sauki yafara samuwa awurin ma amma sam taki kula bahijja domin ko gaisuwarta bata amsawa,
Arana ta bakwai ce ma ta tsigaleta tatas tace kuma ko mutuwa tayi bata yarda taje inda gawarta take ba sannan ba ita ba ita har duniya ta tashi,
Da kuka bahijja tafita taje ta zauna awata runfa taci gaba da kukanta, anty bilkisu ce ta biyota tazo tafara bata baki tana cewa tayi hakuri sannan ta kara da cewa
"Karki saka damuwa acikin ranki domin ba ason mace mai juna biyu ta rinka damuwa hakan zai iya shafar har abinda ke cikin cikinta"
Murmushi tayi wanda bata shirya yinsa ba saboda jin maganar anty Bilkisu,
"Tab ni tunda naje gidanma sau daya akayi wani abu" tafada acikin zuciyarta ashe afili tayi maganar batare data saniba, cikin takaici anty bilkisu ta kalleta,
"Ashe dama duk abubuwan dana dade ina sanar miki baya shiga kunnuwanki,ke kuwa me kika zauna yi? Me kika tsinana agidan? Sau daya? Amma wlh kin bani kunya, banyi zaton sakalcinki da asarancinki yakai haka ba"
Hawayen idonta ta goge ta kalli anty bilkisu "to anty ya zanyi? Shi abbu ayanda na fahinceshi bashida yawan bukatar mace"
Girgiza kai anty bilkisu tayi cikeda bacin rai, "shine ke kuma kika barshi ahaka? Bari kiji ya kamata ki tashi atsaye ki bawa mijinki gudunmawa da kulawa ta musamman, bai kamata ki zuba masa ido kice wai har sai lokacin da yaji bukatarki ya nemeki ba, yanzu wannan ba shine wayewaba, akwai dabaru da salo wanda ya kamata ki koya musamman ma yanzu da kika fuskanci mijinki ko wanne irine, dama maza masu sanyin nan ai haka suke basuda yawan bukatar mace gasu da saurin biyan bukatarsu, dan haka wlh kece ya kamata ki zauna ku fuskanci juna ki gyarashi, ta hanyar yi masa kwalliya mai daukar hankali da sauran abubuwan da zasu jawo miki ra'ayinsa gareki, sannan ina son ki riki ruwan zafi domin duk macen da take amfani da ruwan zafi to tana dauke da wata ni'ima ta musamman, asalima ruwan sanyi bashida wani amfani ajikin ya mace, ita mace anfi son koda wanne lokaci ta kasance cikin dumi shiyasa yin lalle na asali yake da amfani domin shi yafi komai dawowa da mace dumin jikinta sannan kuma yana kewayawa har cikin jinin jikinta yana wanke mata kwayoyin cuta musamman ma cutukan dake cikin mara, idan kina son ki gane haka to ki gwada yin lalle ki kwana dashi, da safe idan kinje yin fitsari ki kula sosai zaki ga fitsarin ya sauya kala yayi kalar lallen sannan kuma har warin lallen zakiji fitsarin yanayi"
Kai ta daga tana kallon anty bilkisu wacce ta dage tana koro mata bayani,
"Ni anty duk banida bukatar wadannan kawai nidai burina abbu ya sauya daga wannan sanyin nashi, wlh yanda kika ganshin nan yana tafiya ahankali to acanma hakan yakeyi"
"To kin San ya zakiyi? Gaskiya zama zakuyi kuyi magana ku fuskanci juna keda shi, wannan ba matsalar da zakiyi shiru bace domin kanki zaki cuta,kedai kawai ki tabbatar kina gyara jikinki, ki yawaita shan kanumfari domin yana gyara mace kuma yana hana fitsarinta yin zarni, duk macen datake amfani da kanumfari to zaka ji tana wani kamshi har fitsarinta kamshin kanumfarin zakaji yana yi, haka kuma shan kunun alkama da zuma da madara yana gyarawa mace jikinta sosai da sosai sannan yana saukar mata da wasu sinadirai ajikinta, shi kansa shan ruwan zafi wani abune mai mutukar amfani ajikin mace daga mace har namiji anfi son susha ruwan zafi lokacin da zasu gudanar da mu'amular auratayya"
"Nagode Anty, insha Allahu zan kiyaye, amma ni kunshin zan gwada yi nagani"
"Hakan yanada kyau sister ki gwada kiga"
Suna nan zaune suna tattaunawa har la'asar tayi lis, 5 jabir yazo asibitin, shima dakyar ma ta iya amsa gaisuwarsa amma daga nan bata kara yi masa magana,