← Book details Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 64

Sashe 30

Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Goodness ya kalla ya dan janye wayar daga jikin kunnenshi,

"Come here"

Ahankali ta tashi ta matsa inda yake, bai jirata ba ya daga rigarta, ya fara duba cibiyar ta,dan yatsanshi ya saka akan cibiyar cikin sauri ta rike yatsan nashi "ohh wash abbu da zafi",

Wayar ya mayar jikin kunnenshi yana yiwa dr bayani, ido ta zuba masa aranta tana tunanin to me kenan? Meye dalilinshi na kin barinta taje taga dr Kodai kishi yake?? Hhhh masu karatu nikaina ummi A'isha tambayar da nake son inyi muku kenan kodai kodai??? Anya kuwa mal jabir ba a kamu ba?? Hmmm muje zuwa zamu gane ai.

Sai da ya gama wayar sannan ta saki dan yatsan nashi tana kallonshi shikuma fuskarshi na kallon wayarsa,

"Bari zai turo da sunayen magungunan da za asai miki kisha yanzu, idan ya turo sai nabayar a siyo miki",

"Thank you abbu"

Tashi tayi ta koma part dinta tayi wanka tayi shirin bacci ta fito ta shiga kitchen ta dafawa jabir shayin na'a na'a ta dauka ta nufi part dinsa.

Yana falo azaune jikinsa sanye da kayan bacci _lemon green_ yana dudduba magungunata wanda ya bayar aka siyo mata,

"Zo ga maganinki"

Karasawa tayi ta zauna tana kallon maganin itama harda wani mai kamar hydrogen amma ba shi bane sai nasha kala daban daban,

"Ki dauka kisha yanzu, shi kuma wannan goge wurin zaki rinka yi dashi"

"Toh" ta karba tana kallonshi, dakyar ta iya daurewa ta goge cibiyarta da spirid domin yanada zafi dan dai kawai tana tsoron jabir ne kar yayi mata irin na rannan.

Kallonta yayi lokacin da take shan maganin tasha kayan baccinta riga fara mai digon pink ajiki sai wando pink colour, mikewa yayi ya shiga _bedroom_ dinshi nan ta tashi tabi bayanshi, agefen gado ta sameshi zaune yana waya da ummu al'amin, bata iya jiyo abinda yake fada hakan ya sata kwanciya acan karshen gadon ta juya masa baya tayi ruf da ciki.

Sun jima suna yin waya da matarshi tana jinsu har ya gama wayar, jin shiru yasata juyawa tana kallonshi,

"Abbu labarin da kace zaka bani jiya"

Juyowa yayi gareta "labarin wa nace zan baki"

"Jesus" tafada tana kokarin gyara kwanciyarta,

"Kamar yadda nafada miki yesu ba Allah bane kuma ba dan Allah bane, asalima idan aka ambaci wannan kalmar sama da kasa sai sunyi kamar zasu hade domin Allah bai cancanci wannan siffar ba, annabi Isah annabin Allah ne wanda mahaifiyarshi ta haifeshi ba tare da uba ba kuma itama Qur'ani ya sanar damu cewar mutuniyar kirki ce tagari mai yawan ibada, amma da Allah ya tashi nuna hikimarsa da ikonsa sai ya nufeta da haihuwar annabinsa ba tareda ta taba saduwa da wani d'a namiji ba, kawai mala'ika ne ya hura mata iska take ta dauki cikin annabi Isah, lokacin data dawo cikin gari wurin mutane suka ganta da d'a sai abin ya basu mamaki har suna son jin abinda ya faru da kuma inda ta samu d'a, alokacin annabi Isah yayi magana cewar shi bawan Allah ne kuma sannan Allah zai bashi wani littafi zuwa ga mutane, hikimar yin haka shine domin akore Kalmar can ta farko ta cewar shi annabi Isah Allah ne shiyasa ya fada da bakinsa cewa shi bawan Allah ne sannan Allah ya sanar damu cewa misalin annabi Isah kamar misalin mutum ne wanda aka halicceshi da tabo sannan aka ce dashi ya kasance take sai ya kasance, gashi Allah ya bashi mu'ujiza domin yana tayar da matacce yana warkar da makaho, kuturu amma duk da izinin Allah, yakan zana tsuntsu da tabo ya hura shi sai ya tashi sama da izinin Allah yabi iska yayita gudu,har yanzu yana nan a sama araye kuma bai taba aure ba saurayine,a karshen duniya annabi Isah zai dawo kuma zai saukone ranar laraba bayan an idar da sallar la'asar, zai sauka a masallacin k'udus (Jerusalem) sannan zaiyi aiki da shari'a da sunnar annabi Muhammad (s.a.w),shiyasa alokacin malamai sunce za awayi gari mutum yana da dunbin dukiya amma babu wanda zai bawa zakka saboda kowa alokacin mai arziki ne, arziki zai wadaci kowa domin zamanine wanda babu zalunci acikinsa, alokacin kuma dujal tuni ya bayyana yanata batar da mutane daga kan hanyar gaskiya to annabi Isah zai nemoshi kuma zai kasheshi idan ya kasheshi shima Allah zai karbi rayuwarsa zai koma ga Allah"

Kwalla taga jabir yana gogewa daga idanuwanshi hakan ya sanyata tashi zaune ta karasa gabanshi ta kamo hannuwanshi ta rike acikin nata,

"Abbu abin da abin tausayi amma kar kayi kuka pls"

"Bayan nan kin san abinda zai biyo baya?? Aranar tashin alqiyama Allah zai tambayi annabi Isah cewar yakai Isah dan maryam shin Kaine ka cewa mutane ku rikeni nida uwata abubuwan bautawa biyu bayan Allah?, sai annabi Isah yace tsarkinka ya tabbata! Baya kasancewa agare ni in fadi abinda babu wani hakki agareni. Idan na kasance na fadeshi to lallai ka sanshi, kana sanin abinda ke cikin raina, kuma bani sanin abinda ke cikin ranka. Lallai ne kai masanin abubuwan boye ne, ban fada musu ba face abinda ka umarceni dashi wato Ku bautawa Allah ubangijina kuma ubangijinku,kuma na kasance mai shaida mutukar na dawwama acikinsu sa'annan alokacin daka karbi raina ka kasance kaine mai tsaro akansu, kuma kai halartacce ne akan dukkan komai. Idan ka azabtar dasu to lalle ne su bayinka ne, idan kuma ka gafarta musu to lallai ne kaine mabuwayi mai hikima, Allah yace wannan ce ranar da masu gaskiya gaskiyarsu take amfanar dasu suna da gidaje a aljannah koramu suna gudana daga karkashinsu suna madawwama acikinsu har abada, Allah ya yarda dasu kuma sun yarda dashi, wannan ne babban rabo mai girma"

Hawaye ne suka ciko idonsa, hannu goodness ta saka ta goge masa su tana kallon kyakkyawar fuskarshi.

Har lokacin hawaye ne na tsantsan imani ke kwaranya akan lausasan kumatusa, ganin haka yasa goodness itama fashewa da kuka duk da cewar bata san abinda jabir yake yiwa hawaye ba shi kukan tunawa da ranar alqiyama yake yi yayinda ita kuma kawai take tayashi ganin abin sonta na zubar da kwalla akaron farko na tarihin rayuwarta,

Hannuwanshi ta damke tana cigaba da kukan, sauke idonsa yayi akan fuskarta ahankali ya rungumeta tsam tsam ajikinsa yana hawaye, kankameshi itama tayi tana mai cigaba da kukan da take yi, sun jima ahaka kafin jabir ya iya dagota daga jikinsa yazuba manyan idanuwansa akan fuskarta,hannunsa yasa yafara share hawayen fuskarta yana murmushi, nata hannun itama ta sanya tafara share masa nasa hawayen tana kallon fuskarshi amma har lokacin bata daina kukan ba.

_*Ummi A'isha*_👌🏻

[10/24, 5:26 PM] Manshat: [9/24, 7:40 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*

*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_

_76-80_

*_Wannan Shafin nakune masu yiwa wani haske dariya, ina fata dariyar yau zatafi ta kullum, sannan dariyar da kuke yiwa wani haske nima takan sani dariya domin ku kun san abinda kuke yiwa dariya haka kuma nima nasan abinda nake yiwa dariyar, wannan fa shi ake kira da kallon kallo, asha karatu lafiya_*

~~~Ido ta tsura masa tana kallonsa acikin zuciyarta tana jinjina labarin da yasanar da ita tun daga kan na annabi Adam har zuwa na annabi Isah (AS) hakika ita dai tasan tun lokacin da tana karamar yarinya ake basu tarihin annabawan nan kamar yadda sunayensu yazo acikin wasu wurare nacikin Bible, yawancin annabawan tanada labarinsu dan tun daga kan Adam,Moses, Jacob,abraham,Jesus, har zuwa kan annabi Muhammad (S.A.W) babu wanda ba asanar dasu ba sai dai its different da wanda jabir yake bata domin shi nasa labarin jinsa take da banbanci da wanda ita tasani,

Har alokacin shima jabir kallonta yake bayan yagama share mata hawayen kan fuskarta, hannunta bisa kuncinsa tana share masa hawayen ya kalleta yace,

"Pls kidaina kukan nan haka"

Girgiza masa kai tayi tana matso wasu hawayen "how can i stop it bayan kai kuma kana yi? Kadaina kaima pls"

Hannunta dake kan kuncinsa ya rike da nashi hannun,

"Ai ni ba kuka nayi ba hawaye ne kawai"

Murmushi tayi tana mai tsayar da ragowar kukan da yake taho mata,

"Abbu wadannan labaran duk da kabani nasan dan kadan game dasu but nawa wanda nasani yasha banban da naka wanda kake fada min"

Har lokacin yana rike da hannunta guda daya akan kuncinsa,

"Goodness shi alqur'ani ba a canjashi,tun lokacin da aka saukar dashi har kawo yanzu babu ko harafi daya da aka canja sannan labaran dake ciki sahihai ne kuma tacaccu, sabanin bible wanda duk an sassauya abubuwan dake ciki, asali ma ba shine littafi nagaskiya ba domin wani bayahude ne ya rubuta shi bayan ya hada kai da wani bamaguje, shiyasa zaki ga Bible din da kuke using yanzu dashi an rubuta _Red letter edition_ ma'ana duk wurin da aka rubuta shi da jan tawada to shine wurin da ake da yakinin maganar Allah ce amma duk inda akayi rubutu da bakar tawada to ba fadin Allah bane sannan kuma kinga ai inda akayi rubutu da jan biron basu da yawa sai acan karshe karshe ma sannan ake samunsu"

Hannunsa ta sake makalewa cikin nata ta gyara zamanta daga durkushen da take ada,

"Abbu naji kace wani bayahude ne ya rubuta wannan _Bible_ din bayan kuma ni nasan bulus ne ya rubuta shi"

"Tabbas bulus ne ya rubutashi kuma asalinsa shi bayahude ne, akwai banbanci tsakanin Christians da kuma masihiyyuna, masihiyyuna sune wadanda suke bin almasihu nagaskiya wato annabi Isah sune wadanda basu sauya ba sannan ba suyi bidi'a ba,

Basu kirkiro ba dangane da abinda aka aiko annabi Isah dashi wadannan su ake kira da nasara (masihiyyuna), _Christians_ kuma sune wadanda suke bin jabun addini wanda aka dangantawa annabi Isah ta hanyar manzo bulus, wanda yake bayahude yayi barna da yawa akan mutanen annabi Isah ta hanyar kashesu da azabtar dasu da kuma haifar musu da yakoki na kare dangi,

Duk da yagama wannan kisan da cewa bai taba ganin annabi Isah ba kuma shi ba sahabinsa bane, daga baya sai yazo ya bayyana tubanshi ga mabiya annabi Isah,majority dinsu basu yarda dashi ba domin sun gane cewa wani makirci ne ya kullo domin ya lalata addinin,
Chapter 30 · 0% Book details