Sashe 43
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Abbu wlh zaka makara a office gashi ana can anata jiranka"
Kallonta yayi yana sake bude manyan idanuwansa yana kallonta, fuskarta ya zubawa ido yana kallonta amma ita takasa kallonshi idonta yana kasa,
"Binti kinga, dago idonki ki kalleni"
Kasa dagowa tayi har lokacin kasa take kallo, hancinta ya lakuce "wannan yarinyar kin fiya wayo da yawa"
Ruwan da yake zuba acikin bahonne yafara zuba akasa domin bahon tuni ya dade da cika,
"Tunda kin ki yin abinda nasaki shikenan bari nayi ni daya kafin amaryata tazo munayi tare"
Juyawa yayi yaje gaban fanfon yafara kashe ruwan da yake zuba,
Ahankali bahijja ta bude kofar bathroom din tafita, agaban mirror ta tsaya tana tunani aranta, tunanin maganar da jabir ya fada mata yanzu take yi indai kuwa hakane amma da tasan sunanta gawa domin ayanda take jin zuciyarta gani take yi indai ya kara aure yanzu to babu makawa mutuwa zata yi, lallai Ummu al'amin tayi kokari gamida juriya data iya barinta ta zama kishiyarta,
Bata taba sanin kishi yanada daci ba sai yanzu da take auren jabir, kasa gyara dakin tayi tana tsaye har lokacin tana juya maganar da jabir yafada mata acikin kwanyarta, har jabir yayi wankan ya fito ya sameta tsaye agaban mirror wadda ita bata ma san yafito daga wankan ba,
Kafadunta ya dafa da duka hannuwanshi guda biyu sai alokacin ta dawo hayyacinta a sanadiyyar sanyin ruwan da taji ajikinta,
"Me kike tunani ne binti?"
Fuskarta ta shagwabe ta turo baki tana son yin kwalla,
"Abbu ba kaine ba kace...!"
Sai kuma tayi shiru,
"Nace me? Fadi inji, me nace?" Ya tambayeta yana kokarin juyo da ita,
"Kaine kace wai, wai, wai...!"
Hawayen idonta ne suka silalo kan kuncinta, hakan yasashi bude baki yana kallonta cikeda mamaki domin bai san abinda yafaru ba,
"Binti me nace? Yi shiru ki fada min kinji"
Kamar ya zugata sai tafashe da kuka tareda fadawa kirjinsa, rungumeta yayi ya fara shafa gashin kanta,
"Binti idan baki fada min ba wa zaki fadawa wanda yafini? Ni yafi cancanta da ki sanarwa da dukkan damuwarki"
"Abbu kaine kace wai idan amaryarka tazo, wai, wai, wai tare zaku nayin wanka" tana gama fadin haka ta boye fuskarta acikin kirjinsa, dariya sosai maganarta ta bawa jabir domin shi yayi tsammanin wani abune muhimmi tunda yaga harda kuka tayi,
"Yanzu binti wannan maganar kike yiwa kuka? Ohhh, nifa nayi zaton wani abune babba yasaki kuka, kishiyar kike yiwa kuka? So kike ta rainaki tun kafin tazo kenan"
"Abbu dagaske kake?"
Kanta ya shafa yana murmushi wanda har hakoransa sai da suka fito, kanta ya dago yana kallonta,
"Wasa ne binti, bada gaske nake yi ba dawasa ne amma indai bakya bani kyakkyawar kulawa to zan yimiki abinda bakya so, indai bazaki rinka bani farin cikiba to zanyi miki kishiya"
"Abbu dan Allah kayi hakuri Allah bazan sakeba" tafada idonta narai narai tana kokarin sake yin wani hawayen,
"Shikenan nahakura, karki sake yin kuka kinji, maza kije ki kawo min breakfast din kafin na shirya"
Sakinta yayi yana yi mata lallausan murmushi, fita tayi tabarshi yafara shiryawa ita kuma ta nufi sashenta, kwanuka masu tsafta ta dauko ta zubo masa doya da kwan data soya masa ga dan farfesun kayan ciki agefe sannan ga custard powder data dama sai tea wanda yasha kayan kamshi aciki,
Kinkimar kayan tayi ta kai masa falonshi ta ajiye sannan tabishi cikin dakin, lokacin data shiga har ya gama shiryawa cikin wani bakin danyen boyel mai kyau dakin gaba daya ya gauraye da kamshin turarensa mai dadi na special oud.
Acan wurin da ya kebe domin gudanar da ibadarsa ta hangoshi yana sallar walaha, tsayawa tayi ta zuba masa ido tana kallon shi hakika yayi mata kyau domin gayunshi ya burgeta mutuka, tun daga hular kansa har agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa duk kalar kayansa ne, tana nan tsaye tasaka zaren gabar rigarta abakinta tana wasa dashi har ya idar yayi addu'a yatashi ya nufo inda take tsaye tana jiransa, gabanta ya karaso ya tsaya, hannunsa yasa yana kokarin zare zaren dake bakinta tana wasa dashi da hakorinta,
"Binti abin riga kike ci? Kalleki kamar wata baby"
Kallonsa tayi tana murmushi "abbu kayi kyau sosai"
"Nagode binti, yau yarintar ce ta motsa?" Yafada yana lakuce hancinta,
Murmushi tayi taja hannunsa tana kallonsa, "abbu muje kayi breakfast, bana son ka makara azuwa office"
Bin bayanta yayi har suka isa wurin da takalmansa ke jere reras, wani bakin takalmi ta dauko masa na fata half cover mai kyau, ajiye mishi tayi agabansa,
Falo suka nufa bayan yasaka takalmin, akan kujera ya zauna ta jawo masa dan karamin stool ta ajiye masa abincin akai tana kallonsa,
"Binti wannan girkin naki ai sai yasa kunnena ya cire" yafada daidai lokacin da yafara cin doyar data soya masa,
"Abbu banda tsokana fa" tafada tana murmushi,
"Babu wani tsokana binti, abincin yayi dadi gashi naga harda wani koko koko, kunu kunu kika hada min"
Murmushi tayi tana tafa hannunta "lah jama'a kunji abbu bai san custard powder ba, amma abbu idan akaji dariya za ayi maka"
"To ai gashinan kin fara yimin dariyar"
Hannunsa ta riko na hagu, "abbu bari na gyara maka agogonka"
Agogon ta kunce ta sake daura masa tana murmushi koda ta gama daura masa bata saki hannun nasa ba yan yatsunta tafara ja tana lankwasa masa su suna kara kas kas,
"Binti kema kin iya mugunta ko?"
"Abbu me nayi maka? Daga gyara?"
Mikewa yayi yana murmushi aranshi yana burin wani lokaci da yake hasashen zuwansa a daren yau,
"Bari naje binti"
"Abbu, Allah ya kiyaye hanya, Allah ya bada sa'a" tafada tana kallonsa
"Amin binti" yafada tareda jan hancinta saboda ganin idonta ya fara kokarin kawo kwalla,
"Meyasa bakya gajiya da kuka ne? Ki rage saurin kuka idan ba haka ba zaki haifi yaro ruwa ruwa"
Dariya ce ta subuce mata bata shirya ba "abbu nida ko cikin banyi ba har zaka fara yimin maganar yaro" tafada tana yi masa murmushi,
"Saurin me kikeyi binti? Zakiyi ai soon"
Murmushi tayi har lokacin tana rikeda hannunsa "abbu ka taho min da chocolate"
"Muga bakin kwadayin shan chocolate?"
Bakin ta bude tana turo masa dan yagani, kiss ya manna mata akan lips dinta duka yana murmushi,
Sakinsa tayi ta juya tana murmushin itama, fita yayi yana mai jin babu dadi acikin ranshi dalilin nisantar ta da zaiyi,
Tana labe tana lekenshi har yabar gidan, kan kujera ta fada ta kwanta tana tunanin hali irin na jabir.
Tunda ya tafi yabarta taketa kirkirar ayyuka domin bata son zama kurum saboda idan ta zauna tasan kadaicine zai dameta gashi kuma tunda jabir yafita take tunaninshi acikin zuciyarta,
Babu irin aikin da bata yi ba domin ganin ta ragewa kanta lokaci, kananan kayan jabir duk ta tattare da jallabiyoyinshi da kayan baccinshi duk ta wanke, bayan ta gama taje ta dora girki, tuwon shinkafa miyar agushi tayi tahada lemonta na kwakwa da madara kamar yadda ta saba,
Wayar jabir tafara kira lokacin misalin karfe 1:30 narana, yana tsaka da aiki a office sai rubuce rubuce yake gashi files tuli guda akan teburinsa kasancewar ya dade baya office din shiyasa ayyuka suka tarar masa,
Agajiye ya daga wayar yana murmushi aranshi kuma yana tunanin ko yanzu da wacce rigimar ta bullo kuma,
"Binti ya akayi?"
Fuska ta shagwabe kamar yana kallonta, "abbu sai yaushe zaka dawo?"
"Binti aiki yayi min yawa, sai 5 zan tashi may be ma yau sai nayi over time saboda inada ayyuka dayawa"
"Abbu kar kayi over time dan Allah, kadawo 5 din"
"Kina son ganina ne binti?"
"Ehh abbu"
"Me zaki bani?"
"Abbu sai kadawo dai, yanzu dai ka turo min mal idi driver"
"Ina zaki aikeshi?"
"Wurinka abbu, dan Allah karka manta"
"Bazan manta ba"
"Yawwa abbu nagode, ayi aiki lafiya"
Wayar ta tsinke tana jin wani irin dadi acikin ranta,
Shima jabir wayar ya ajiye yana murmushi ko me zata aiko masa kuma oho,
Lokacin da mal idi driver yazo dama tuni ta gama harhada masa kayan acikin kwando babba, komai da zai bukata ta zuba kama tun daga filet da cokula da cups da tissue domin goge hannu, dan haka yana zuwa bashi kawai tayi takoma sashenta,
Lokacin da sakon ya riski jabir ba karamin mamaki yayi ba, domin abincine wanda akalla mutane biyar zasu ci ya ishesu gashi harda hadadden lemon kwakwa,dadine yake ratsashi tako ina dama meeting zasuyi shida directors dinsa Wanda duk lokacin da sukayi meeting din abincin sayarwa ake siyo musu amma shi baya ci saboda gaskiya yanada tsananin kyankyami,
Wannan abincin da bahijja ta aika musu shi sukaci sukayi kat Suna santi kowa sai yabawa yake yi, shikuwa jin bahijja yake har acikin zuciyarsa saboda yasan ta damu dashi sannan tana kiyaye duk wani abu wanda zai sakashi cikin damuwa, ranar har 6yakai a office sai 6:30 ya nufi gida, duk ya gama kosawa burinsa kawai yaje gida yayi ido hudu da ita.
Tana falonta tana kallon wani American film ya shiga yana gyara babbar rigarsa,
Tashi tayi tana murnar ganinsa yayinda shikuma yayi mutuwar tsaye yana kallon kyakkyawar shigar da tayi domin wata rigace orange colour mai wasu fararen duwatsu ajiki, iya cinya rigar take sannan bata da babban hannu, hannunta dan karamine, ga wani wando baki fela tasaka, kanta ta daura bakin dan kwali,
Gabansa taje ta tsaya tana kallonsa,
"Abbu sannu da zuwa"
Hannu ya mika ya kamo nata hannun yajata ya hadata da barin jikinshi ya nufi sashensa da ita,
"Yawwa binti ya gida? Natafi nabarki ke daya ko?"
Daga kai tayi "abbu ai gobe sai nabika"
Murmushi yayi yana mai tuno al'amin dinshi domin shima kusan kullum haka yake cewa sai ya bishi office lokuta da dama sai yayi masa dabara sannan zai samu ya zare jikinsa ya fita,
Har cikin falonshi ta rakashi tana shakar kamshin jikinsa, cikin bedroom dinsa ya shiga yayi wanka ya fito yayi shirin masallaci, gaba daya kamshine ke tashi daga jikinsa,
Har inda take yaje ya kamo hannunta ya yatasheta daga zaunen da take ya rike yan yatsunta yana kallon kwayar idonta, sunkuyar da kanta tayi ta kasa kallonsa,dago habarta yayi yakai bakinsa kan goshinta yayi mata kiss,yana murmushi,
"Binti zanje masallaci kinji? Sai nadawo"
Kallonta yayi yana sake bude manyan idanuwansa yana kallonta, fuskarta ya zubawa ido yana kallonta amma ita takasa kallonshi idonta yana kasa,
"Binti kinga, dago idonki ki kalleni"
Kasa dagowa tayi har lokacin kasa take kallo, hancinta ya lakuce "wannan yarinyar kin fiya wayo da yawa"
Ruwan da yake zuba acikin bahonne yafara zuba akasa domin bahon tuni ya dade da cika,
"Tunda kin ki yin abinda nasaki shikenan bari nayi ni daya kafin amaryata tazo munayi tare"
Juyawa yayi yaje gaban fanfon yafara kashe ruwan da yake zuba,
Ahankali bahijja ta bude kofar bathroom din tafita, agaban mirror ta tsaya tana tunani aranta, tunanin maganar da jabir ya fada mata yanzu take yi indai kuwa hakane amma da tasan sunanta gawa domin ayanda take jin zuciyarta gani take yi indai ya kara aure yanzu to babu makawa mutuwa zata yi, lallai Ummu al'amin tayi kokari gamida juriya data iya barinta ta zama kishiyarta,
Bata taba sanin kishi yanada daci ba sai yanzu da take auren jabir, kasa gyara dakin tayi tana tsaye har lokacin tana juya maganar da jabir yafada mata acikin kwanyarta, har jabir yayi wankan ya fito ya sameta tsaye agaban mirror wadda ita bata ma san yafito daga wankan ba,
Kafadunta ya dafa da duka hannuwanshi guda biyu sai alokacin ta dawo hayyacinta a sanadiyyar sanyin ruwan da taji ajikinta,
"Me kike tunani ne binti?"
Fuskarta ta shagwabe ta turo baki tana son yin kwalla,
"Abbu ba kaine ba kace...!"
Sai kuma tayi shiru,
"Nace me? Fadi inji, me nace?" Ya tambayeta yana kokarin juyo da ita,
"Kaine kace wai, wai, wai...!"
Hawayen idonta ne suka silalo kan kuncinta, hakan yasashi bude baki yana kallonta cikeda mamaki domin bai san abinda yafaru ba,
"Binti me nace? Yi shiru ki fada min kinji"
Kamar ya zugata sai tafashe da kuka tareda fadawa kirjinsa, rungumeta yayi ya fara shafa gashin kanta,
"Binti idan baki fada min ba wa zaki fadawa wanda yafini? Ni yafi cancanta da ki sanarwa da dukkan damuwarki"
"Abbu kaine kace wai idan amaryarka tazo, wai, wai, wai tare zaku nayin wanka" tana gama fadin haka ta boye fuskarta acikin kirjinsa, dariya sosai maganarta ta bawa jabir domin shi yayi tsammanin wani abune muhimmi tunda yaga harda kuka tayi,
"Yanzu binti wannan maganar kike yiwa kuka? Ohhh, nifa nayi zaton wani abune babba yasaki kuka, kishiyar kike yiwa kuka? So kike ta rainaki tun kafin tazo kenan"
"Abbu dagaske kake?"
Kanta ya shafa yana murmushi wanda har hakoransa sai da suka fito, kanta ya dago yana kallonta,
"Wasa ne binti, bada gaske nake yi ba dawasa ne amma indai bakya bani kyakkyawar kulawa to zan yimiki abinda bakya so, indai bazaki rinka bani farin cikiba to zanyi miki kishiya"
"Abbu dan Allah kayi hakuri Allah bazan sakeba" tafada idonta narai narai tana kokarin sake yin wani hawayen,
"Shikenan nahakura, karki sake yin kuka kinji, maza kije ki kawo min breakfast din kafin na shirya"
Sakinta yayi yana yi mata lallausan murmushi, fita tayi tabarshi yafara shiryawa ita kuma ta nufi sashenta, kwanuka masu tsafta ta dauko ta zubo masa doya da kwan data soya masa ga dan farfesun kayan ciki agefe sannan ga custard powder data dama sai tea wanda yasha kayan kamshi aciki,
Kinkimar kayan tayi ta kai masa falonshi ta ajiye sannan tabishi cikin dakin, lokacin data shiga har ya gama shiryawa cikin wani bakin danyen boyel mai kyau dakin gaba daya ya gauraye da kamshin turarensa mai dadi na special oud.
Acan wurin da ya kebe domin gudanar da ibadarsa ta hangoshi yana sallar walaha, tsayawa tayi ta zuba masa ido tana kallon shi hakika yayi mata kyau domin gayunshi ya burgeta mutuka, tun daga hular kansa har agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa duk kalar kayansa ne, tana nan tsaye tasaka zaren gabar rigarta abakinta tana wasa dashi har ya idar yayi addu'a yatashi ya nufo inda take tsaye tana jiransa, gabanta ya karaso ya tsaya, hannunsa yasa yana kokarin zare zaren dake bakinta tana wasa dashi da hakorinta,
"Binti abin riga kike ci? Kalleki kamar wata baby"
Kallonsa tayi tana murmushi "abbu kayi kyau sosai"
"Nagode binti, yau yarintar ce ta motsa?" Yafada yana lakuce hancinta,
Murmushi tayi taja hannunsa tana kallonsa, "abbu muje kayi breakfast, bana son ka makara azuwa office"
Bin bayanta yayi har suka isa wurin da takalmansa ke jere reras, wani bakin takalmi ta dauko masa na fata half cover mai kyau, ajiye mishi tayi agabansa,
Falo suka nufa bayan yasaka takalmin, akan kujera ya zauna ta jawo masa dan karamin stool ta ajiye masa abincin akai tana kallonsa,
"Binti wannan girkin naki ai sai yasa kunnena ya cire" yafada daidai lokacin da yafara cin doyar data soya masa,
"Abbu banda tsokana fa" tafada tana murmushi,
"Babu wani tsokana binti, abincin yayi dadi gashi naga harda wani koko koko, kunu kunu kika hada min"
Murmushi tayi tana tafa hannunta "lah jama'a kunji abbu bai san custard powder ba, amma abbu idan akaji dariya za ayi maka"
"To ai gashinan kin fara yimin dariyar"
Hannunsa ta riko na hagu, "abbu bari na gyara maka agogonka"
Agogon ta kunce ta sake daura masa tana murmushi koda ta gama daura masa bata saki hannun nasa ba yan yatsunta tafara ja tana lankwasa masa su suna kara kas kas,
"Binti kema kin iya mugunta ko?"
"Abbu me nayi maka? Daga gyara?"
Mikewa yayi yana murmushi aranshi yana burin wani lokaci da yake hasashen zuwansa a daren yau,
"Bari naje binti"
"Abbu, Allah ya kiyaye hanya, Allah ya bada sa'a" tafada tana kallonsa
"Amin binti" yafada tareda jan hancinta saboda ganin idonta ya fara kokarin kawo kwalla,
"Meyasa bakya gajiya da kuka ne? Ki rage saurin kuka idan ba haka ba zaki haifi yaro ruwa ruwa"
Dariya ce ta subuce mata bata shirya ba "abbu nida ko cikin banyi ba har zaka fara yimin maganar yaro" tafada tana yi masa murmushi,
"Saurin me kikeyi binti? Zakiyi ai soon"
Murmushi tayi har lokacin tana rikeda hannunsa "abbu ka taho min da chocolate"
"Muga bakin kwadayin shan chocolate?"
Bakin ta bude tana turo masa dan yagani, kiss ya manna mata akan lips dinta duka yana murmushi,
Sakinsa tayi ta juya tana murmushin itama, fita yayi yana mai jin babu dadi acikin ranshi dalilin nisantar ta da zaiyi,
Tana labe tana lekenshi har yabar gidan, kan kujera ta fada ta kwanta tana tunanin hali irin na jabir.
Tunda ya tafi yabarta taketa kirkirar ayyuka domin bata son zama kurum saboda idan ta zauna tasan kadaicine zai dameta gashi kuma tunda jabir yafita take tunaninshi acikin zuciyarta,
Babu irin aikin da bata yi ba domin ganin ta ragewa kanta lokaci, kananan kayan jabir duk ta tattare da jallabiyoyinshi da kayan baccinshi duk ta wanke, bayan ta gama taje ta dora girki, tuwon shinkafa miyar agushi tayi tahada lemonta na kwakwa da madara kamar yadda ta saba,
Wayar jabir tafara kira lokacin misalin karfe 1:30 narana, yana tsaka da aiki a office sai rubuce rubuce yake gashi files tuli guda akan teburinsa kasancewar ya dade baya office din shiyasa ayyuka suka tarar masa,
Agajiye ya daga wayar yana murmushi aranshi kuma yana tunanin ko yanzu da wacce rigimar ta bullo kuma,
"Binti ya akayi?"
Fuska ta shagwabe kamar yana kallonta, "abbu sai yaushe zaka dawo?"
"Binti aiki yayi min yawa, sai 5 zan tashi may be ma yau sai nayi over time saboda inada ayyuka dayawa"
"Abbu kar kayi over time dan Allah, kadawo 5 din"
"Kina son ganina ne binti?"
"Ehh abbu"
"Me zaki bani?"
"Abbu sai kadawo dai, yanzu dai ka turo min mal idi driver"
"Ina zaki aikeshi?"
"Wurinka abbu, dan Allah karka manta"
"Bazan manta ba"
"Yawwa abbu nagode, ayi aiki lafiya"
Wayar ta tsinke tana jin wani irin dadi acikin ranta,
Shima jabir wayar ya ajiye yana murmushi ko me zata aiko masa kuma oho,
Lokacin da mal idi driver yazo dama tuni ta gama harhada masa kayan acikin kwando babba, komai da zai bukata ta zuba kama tun daga filet da cokula da cups da tissue domin goge hannu, dan haka yana zuwa bashi kawai tayi takoma sashenta,
Lokacin da sakon ya riski jabir ba karamin mamaki yayi ba, domin abincine wanda akalla mutane biyar zasu ci ya ishesu gashi harda hadadden lemon kwakwa,dadine yake ratsashi tako ina dama meeting zasuyi shida directors dinsa Wanda duk lokacin da sukayi meeting din abincin sayarwa ake siyo musu amma shi baya ci saboda gaskiya yanada tsananin kyankyami,
Wannan abincin da bahijja ta aika musu shi sukaci sukayi kat Suna santi kowa sai yabawa yake yi, shikuwa jin bahijja yake har acikin zuciyarsa saboda yasan ta damu dashi sannan tana kiyaye duk wani abu wanda zai sakashi cikin damuwa, ranar har 6yakai a office sai 6:30 ya nufi gida, duk ya gama kosawa burinsa kawai yaje gida yayi ido hudu da ita.
Tana falonta tana kallon wani American film ya shiga yana gyara babbar rigarsa,
Tashi tayi tana murnar ganinsa yayinda shikuma yayi mutuwar tsaye yana kallon kyakkyawar shigar da tayi domin wata rigace orange colour mai wasu fararen duwatsu ajiki, iya cinya rigar take sannan bata da babban hannu, hannunta dan karamine, ga wani wando baki fela tasaka, kanta ta daura bakin dan kwali,
Gabansa taje ta tsaya tana kallonsa,
"Abbu sannu da zuwa"
Hannu ya mika ya kamo nata hannun yajata ya hadata da barin jikinshi ya nufi sashensa da ita,
"Yawwa binti ya gida? Natafi nabarki ke daya ko?"
Daga kai tayi "abbu ai gobe sai nabika"
Murmushi yayi yana mai tuno al'amin dinshi domin shima kusan kullum haka yake cewa sai ya bishi office lokuta da dama sai yayi masa dabara sannan zai samu ya zare jikinsa ya fita,
Har cikin falonshi ta rakashi tana shakar kamshin jikinsa, cikin bedroom dinsa ya shiga yayi wanka ya fito yayi shirin masallaci, gaba daya kamshine ke tashi daga jikinsa,
Har inda take yaje ya kamo hannunta ya yatasheta daga zaunen da take ya rike yan yatsunta yana kallon kwayar idonta, sunkuyar da kanta tayi ta kasa kallonsa,dago habarta yayi yakai bakinsa kan goshinta yayi mata kiss,yana murmushi,
"Binti zanje masallaci kinji? Sai nadawo"