Sashe 59
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Da zafine binti?"
Gudun kada ta badashi agaban nurse din ya sata daga masa kai amma batayi magana ba,
"Ayya sorry bintina" yace da ita ahankali, jin yanda yake wasa da hannunta yasata mantawa da zafin spirit din da take ji asalima bata san lokacin da nurse ta kammala ta fita ba,
Dawowar anty Bilkisu ce ta sanya jabir yi musu sallama yatafi, sai da yatafi sannan bahijja tajiyo da kanta, tunda yatafi ahanya yafara tunanin bahijja "lallai yarinyar nan ta iya fushi" yafada aranshi yana murmushi domin tunowa da yayi yanda taki ko kallonsa har yagama zamansa yatafi.
Har sukayi sati daya a asibitin bai samu kan bahijja ba domin kullum idan yaje bata rai take ta murtuke fuska sannan ta kawar da kanta tayanda bazasu ga fuskokin juna ba, yana son yaganta yayi magana da ita amma babu hali kasancewar kullum anty Bilkisu da 'ma' suna dakin,
Kwanansu 9 aka sallamesu amma fa ba karamin dawainiya jabir yasha ba lokacin da suna asibitin nan, daga office ya tura musu driver ya daukesu domin kaisu gida nan kuma bahijja tace ita ba gidan jabir za akaita ba gidansu za akaita,
Mamansu ce ta rarrasheta tace tabari dai su fara zuwa gidan nata tukunna, kwanciya tayi ajikin mamanta tana mai jin wani irin sanyi acikin ranta domin yanzu ta fahinci kwata kwata maman nata bata son bacin ranta.
Tunda suka koma gida wanka kawai tayi tasaka wata yar karamar riga iya cibiya pink colour da yar karamar mini skirt baka,
A falo ta kwanta yayinda anty bilkisu ta ke can tana yi mata yan aikace aikace, tea ta tashi tahada ta fara sha kenan jabir ya shigo kuma da alama ba lokacin ya dawo ba saboda taganshi kanshi babu hula sannan kuma takalmin kafarshi slippers ne,
Kallonta ya tsaya yi yanda tayi kyau sosai cikin kananan kayan da tasaka,
"Bintina me zaki bani nacine? Yunwa nakeji"
Bata amsa masa ba har anty bilkisu ta shigo ta riski maganarshi,juyawa anty bilkisu tayi tafita bayan tayi masa sannu da zuwa Jim kadan sai gata da food flasks guda biyu,
"Ungo kai masa abincin"
Kallon jabir tayi ta kalli anty bilkisu sai kawai ta mike tana zumbura baki ta karba tayi gaba, bin bayanta yayi yana murmushi "yan darun kwana biyu akusa suke" yafada acikin zuciyarshi,
Yanda ta zallake tana tafiya har dariya abin yaso bashi, tana shiga falonshi shima yana shiga, a kasa ta ajiye flasks din ta jiyo zata fice yayi saurin riko hannunta,
"Binti wai wannan fushin har yau baki huce bane?"
Kanta ta kawar batare da tayi magana ba,
"Kiyi min magana ko na matse bakinki yanzu"
"Kar ka matsa cewar sai nayi magana saboda maganata ba zatayi maka dadiba" tafada gamida fusge hannunta ta cire zoben da ya saka mata takama hannunshi ta dora masa atafin hannunshi,
"Ga abunka nan bana so"
Wucewa tayi ta gefenshi yana kallonta bai hanata ba, fita tayi takoma sashenta taci gaba da harkokinta.
Bayan sallar magrib tana zaune asaman gadonta sai gashi ya shigo sanye da jallabiya ruwan toka, har tsakiyar gadon yabita ya tsura mata ido,
"Binti karfa ki zama daya daga cikin mutanen nan wadanda basa yafiya idan aka yi musu laifi"
Juyowa tayi ta dubeshi tasake dauke kanta,
"Ungo zobenki domin ni bana daya daga cikin wadanda suke yin kyauta suna kwacewa domin annabi yace duk wanda yake kyauta yana kwacewa to kamar karene yayi amai sannan ya koma ya lashe amansa"
Hannunta Yakama yasake saka mata zoben yana kallon fuskarta,
"Binti kina son yau na mutsuttsuke wannan dinkin da aka yi miki? Kiyi min magana naji"
Shiru bata bashi amsa ba, maganar anty bilkisu yajiyo a falo sam bai san tana nan ba,tashi yayi yafita, haka suka ci gaba da zama har anty tagama kwana biyun da zata yi mata tayi tafiyarta dama jabir kyaleta kawai yayi yana jiran yaga tafiyar anty bilkisu.
Karfe 4 yau yadawo daga office, ta kofar baya yabi ya shiga part dinta daga shi sai vest da dogon wandon farin yadin dake jikinsa,
Adakinta ya sameta tana kwance ruf da ciki,amma ba bacci take yiba idonta biyu,
Juyata yayi yana cewa "binti babu kyau irin wannan kwanciyar dan Allah ki daina"
Jin bata amsaba yasashi niyyar daukarta sai kuma yafasa yana cewa "ashe fa bamu taba barin tarihi adakin nan ba ko? Bari yau mu bari"
Tana jinshi amma bata yi tsammanin dagaske yake yiba, jikinta ya shiga yafara aika mata da wasu zafafan sakonni, da dai taga dagaske yake sai tafara kuka,
"Abbu kar wurin dinkina ya farke kayan cikina su fito"
Dariya yayi ya rungumeta yana shafar kanta,
"Bazai farke ba binti kinji".
Bayan komai ya wakana ne bahijja,
Cikin sigar shagwaba tafara magana, "abbu yanzu ka kyauta min kenan?"
"Ai nabaki hakuri binti, shiyasa ma yanzu nasake baki wani hakurin saboda naga kamar akan kin rasa cikinki ne kike fushi dani"
Girgiza kai tayi "abbu baka sona, baka taba cewa kana sona ba" takarasa maganar tana hawaye,
"Au wannan shine kadai? Wlhi ina sonki binti ina yimiki irin son da bana yiwa kaina"
Koba komai taji sanyi acikin ranta saboda jin maganarshi, daukarta yayi zuwa toilet yayi mata wanka ya fito da ita ya zauna ya shiryata yasaka mata wasu kananan kaya riga da wando, ko masallaci bai iya fitaba agida ya zauna yajasu salla, lokacin bacci yanayi ya shiryata cikin kayan baccinta yar yaloluwar rigar bacci yeluwa iya gwiwa, daukarta yayi zuwa sashensa ya kwantar da ita agefen gado, kusa da ita yaje ya kwanta bayan shima ya shirya, kalamai masu dadi ya shiga yi mata, Kalmar i love you kuwa tajita babu adadi har tayi bacci bata san lokacin da yadaina fadi ba.
Mata da miji dama sai Allah domin sun shirya sun dinke sunci gaba da zamansu lafiya fiyeda da, zaman da bahijjan ta danyi agida lokacin da suka samu sabani da jabir yabawa mamanta damar fuskantarta sosai wanda har taji itama yanzu tana burin kasancewa cikin addinin islama, hakan ba karamin dadi yayiwa kowa ba, awurin jabir ta karbi Kalmar shahada sannan ta amshi sabon suna wato A'isha, wannan abuda yafaru ya kara sakawa bahijja imani domin yanzu tagane sau da dama abubuwan da suke faruwa arayuwarmu marassa dadi to hanyace kuma ta samun wani babban rabon acikin rayuwarmu domin lokacin da suka samu sabani da jabir ta shiga cikin tashin hankali sosai ashe mabudin alherine agareta bata saniba.
Yau takama ranar laraba tana kitchen tana aikin kayan kwadayinta jabir ya dawo daga office ya shigo ya isketa tana soya yar gullisuwa,
Abayanta ya tsaya "binti yau kuma me akeyi haka"
"Abbu Yar gullisuwa nakeyi"
Murmushi yayi ya leka cikin kaskon man, "dadina dake duk hanyar kwadayi kin santa binti, da alama nasake baki wani sabon babyn ko?"
"Nidai abbu kabari gaskiya" tafada ashagwabance, juyawa yayi yafita yana yi mata dariya.
Tun daga ranar ya zamana kullum ita kenan cikin hade haden kayan makulashe,yau kam salak ta yanka ta yanka masa tumatur da albasa da dafaffen kwai tasaka maggi da man gyada tafara ci,
Shigowar jabir ne ya katse mata laumar da ta dage tanayi,
"Abbu ga salad"
Akan kujera ya zauna yana kallonta, tacika sosai domin kirjinta yasake cika gashi hips dinta shima yasake budewa sosai,
"A'a binti nagode ci kayanki" yace da ita yana murmushi,
"To abbu ka samo min lalo, anjima tuwon amala zanyi miyar lalo sai in saka masa man shanu da garin yaji"
"Binti ina zan samo miki wani lalo yanzu?"
"Agidan malam za asamu"
"To naji ya isa, zan samo mikin"
Cin salak dinta taci gaba dayi yayinda shi kuma yana zaune yana kallonta, kullum kwadayinta sake karuwa yake domin bata da aiki sai shan tsami gaye, alawar madara, goba mai tsami da makamantansu amma tunda take neman kayan kwadayinta jabir bai taba kin samo mata ba duk abinda take so samomata yake domin har tambayarta yake idan zai fita yau kuma me ake kwadayi ita kam sai dai tayi murmushi tafada masa.
Lokaci yaci gaba da tafiya har cikin nata yafito domin yanzu watanshi 7 duk tabi ta dan kunkumbura, alokacin su ummu al'amin suka fara shirin zuwa gida,
Ana saura kwana biyu su dawo bahijja tafara kwasar kayayyakinta dake cikin dakin jabir domin dama rabi tana dakinta ne rabi tana dakinsa,cike da damuwa tashiga toilet dinsa ta kwaso inner wears dinta dake shanye wanda jabir ya wanke mata,
Kayan kwalliyarta dake kan mirror dinshi tafara tattarewa ranta acinkushe,shima kansa jabir din yana cikin damuwa domin yanzune ya kamata ya bata kulawa ta musamman domin cikin dake jikinta gashi yanzu bata yin minti 30 sai taci abinci shiyasa kullum da daddare sai ya tashi ya hada mata abinci taci koda kuwa cornflakes ne da madara. Ganin ta shiga damuwa yasashi kwantar mata da hankali har ta dan ji sassauci aranta.
Ana igobe ranar da su Ummu al'amin zasu dawo yan uwan ummun suka zo domin gyara mata sashenta, wannan shine karo nafarko da bahijja taga wani wanda ya danganci ummu al'amin.
Duk da tsohon cikin dake jikinta hakan bai hanata shiga kitchen ta dora musu girki ba, tuwon shinkafa tayi musu miyar agushi,
Dauka tayi ta kai musu tasamesu sunata faman aikace aikace domin babu laifi wurin yahada uban datti,
Zama tayi bayan ta ajiye musu abincin, tana nan wurinsu tana dan tattaya su aikin wata daga cikinsu ta zame tafadi "washhh ni jikar mutun hudu" wacce ta zame din tafada tana rike kunkuminta,
"Kijita maimakon kiyi salati zaki wani ce haka sai kace wata sabuwar tuba" wata daga cikinsu tafada, take bahijja taji ranta ya sosu, tun kafin abin yayi yawa ta mike dakyar tafita daga part din ta nufi nata, sam bata ma san cewar jabir ya dawo gidanba,dakinta ta Shiga tana hawaye "wai shin meyasa wasu mutanen suke yiwa wadanda suka karbi musulunci isgili?" Ta tambayi kanta,
Gaban mudubinta takarasa tana kuka domin abin ya bata mata rai, jabir yana daya dakin nata ya jiyo motsinta, binta yayi yaje ya tsaya abayanta tareda jiyo da ita ganin tana kuka yasanya kwakwalwarshi gano abinda yafaru,
"Binti keda yan uwan ummu al'amin ne ko?"
Girgiza kai tayi alamar a'a,
"Kar kiyi min karya binti nasan sune suka saka ki kuka kila cemiki sukayi ke ba asalin musulma bace"
Gudun kada ta badashi agaban nurse din ya sata daga masa kai amma batayi magana ba,
"Ayya sorry bintina" yace da ita ahankali, jin yanda yake wasa da hannunta yasata mantawa da zafin spirit din da take ji asalima bata san lokacin da nurse ta kammala ta fita ba,
Dawowar anty Bilkisu ce ta sanya jabir yi musu sallama yatafi, sai da yatafi sannan bahijja tajiyo da kanta, tunda yatafi ahanya yafara tunanin bahijja "lallai yarinyar nan ta iya fushi" yafada aranshi yana murmushi domin tunowa da yayi yanda taki ko kallonsa har yagama zamansa yatafi.
Har sukayi sati daya a asibitin bai samu kan bahijja ba domin kullum idan yaje bata rai take ta murtuke fuska sannan ta kawar da kanta tayanda bazasu ga fuskokin juna ba, yana son yaganta yayi magana da ita amma babu hali kasancewar kullum anty Bilkisu da 'ma' suna dakin,
Kwanansu 9 aka sallamesu amma fa ba karamin dawainiya jabir yasha ba lokacin da suna asibitin nan, daga office ya tura musu driver ya daukesu domin kaisu gida nan kuma bahijja tace ita ba gidan jabir za akaita ba gidansu za akaita,
Mamansu ce ta rarrasheta tace tabari dai su fara zuwa gidan nata tukunna, kwanciya tayi ajikin mamanta tana mai jin wani irin sanyi acikin ranta domin yanzu ta fahinci kwata kwata maman nata bata son bacin ranta.
Tunda suka koma gida wanka kawai tayi tasaka wata yar karamar riga iya cibiya pink colour da yar karamar mini skirt baka,
A falo ta kwanta yayinda anty bilkisu ta ke can tana yi mata yan aikace aikace, tea ta tashi tahada ta fara sha kenan jabir ya shigo kuma da alama ba lokacin ya dawo ba saboda taganshi kanshi babu hula sannan kuma takalmin kafarshi slippers ne,
Kallonta ya tsaya yi yanda tayi kyau sosai cikin kananan kayan da tasaka,
"Bintina me zaki bani nacine? Yunwa nakeji"
Bata amsa masa ba har anty bilkisu ta shigo ta riski maganarshi,juyawa anty bilkisu tayi tafita bayan tayi masa sannu da zuwa Jim kadan sai gata da food flasks guda biyu,
"Ungo kai masa abincin"
Kallon jabir tayi ta kalli anty bilkisu sai kawai ta mike tana zumbura baki ta karba tayi gaba, bin bayanta yayi yana murmushi "yan darun kwana biyu akusa suke" yafada acikin zuciyarshi,
Yanda ta zallake tana tafiya har dariya abin yaso bashi, tana shiga falonshi shima yana shiga, a kasa ta ajiye flasks din ta jiyo zata fice yayi saurin riko hannunta,
"Binti wai wannan fushin har yau baki huce bane?"
Kanta ta kawar batare da tayi magana ba,
"Kiyi min magana ko na matse bakinki yanzu"
"Kar ka matsa cewar sai nayi magana saboda maganata ba zatayi maka dadiba" tafada gamida fusge hannunta ta cire zoben da ya saka mata takama hannunshi ta dora masa atafin hannunshi,
"Ga abunka nan bana so"
Wucewa tayi ta gefenshi yana kallonta bai hanata ba, fita tayi takoma sashenta taci gaba da harkokinta.
Bayan sallar magrib tana zaune asaman gadonta sai gashi ya shigo sanye da jallabiya ruwan toka, har tsakiyar gadon yabita ya tsura mata ido,
"Binti karfa ki zama daya daga cikin mutanen nan wadanda basa yafiya idan aka yi musu laifi"
Juyowa tayi ta dubeshi tasake dauke kanta,
"Ungo zobenki domin ni bana daya daga cikin wadanda suke yin kyauta suna kwacewa domin annabi yace duk wanda yake kyauta yana kwacewa to kamar karene yayi amai sannan ya koma ya lashe amansa"
Hannunta Yakama yasake saka mata zoben yana kallon fuskarta,
"Binti kina son yau na mutsuttsuke wannan dinkin da aka yi miki? Kiyi min magana naji"
Shiru bata bashi amsa ba, maganar anty bilkisu yajiyo a falo sam bai san tana nan ba,tashi yayi yafita, haka suka ci gaba da zama har anty tagama kwana biyun da zata yi mata tayi tafiyarta dama jabir kyaleta kawai yayi yana jiran yaga tafiyar anty bilkisu.
Karfe 4 yau yadawo daga office, ta kofar baya yabi ya shiga part dinta daga shi sai vest da dogon wandon farin yadin dake jikinsa,
Adakinta ya sameta tana kwance ruf da ciki,amma ba bacci take yiba idonta biyu,
Juyata yayi yana cewa "binti babu kyau irin wannan kwanciyar dan Allah ki daina"
Jin bata amsaba yasashi niyyar daukarta sai kuma yafasa yana cewa "ashe fa bamu taba barin tarihi adakin nan ba ko? Bari yau mu bari"
Tana jinshi amma bata yi tsammanin dagaske yake yiba, jikinta ya shiga yafara aika mata da wasu zafafan sakonni, da dai taga dagaske yake sai tafara kuka,
"Abbu kar wurin dinkina ya farke kayan cikina su fito"
Dariya yayi ya rungumeta yana shafar kanta,
"Bazai farke ba binti kinji".
Bayan komai ya wakana ne bahijja,
Cikin sigar shagwaba tafara magana, "abbu yanzu ka kyauta min kenan?"
"Ai nabaki hakuri binti, shiyasa ma yanzu nasake baki wani hakurin saboda naga kamar akan kin rasa cikinki ne kike fushi dani"
Girgiza kai tayi "abbu baka sona, baka taba cewa kana sona ba" takarasa maganar tana hawaye,
"Au wannan shine kadai? Wlhi ina sonki binti ina yimiki irin son da bana yiwa kaina"
Koba komai taji sanyi acikin ranta saboda jin maganarshi, daukarta yayi zuwa toilet yayi mata wanka ya fito da ita ya zauna ya shiryata yasaka mata wasu kananan kaya riga da wando, ko masallaci bai iya fitaba agida ya zauna yajasu salla, lokacin bacci yanayi ya shiryata cikin kayan baccinta yar yaloluwar rigar bacci yeluwa iya gwiwa, daukarta yayi zuwa sashensa ya kwantar da ita agefen gado, kusa da ita yaje ya kwanta bayan shima ya shirya, kalamai masu dadi ya shiga yi mata, Kalmar i love you kuwa tajita babu adadi har tayi bacci bata san lokacin da yadaina fadi ba.
Mata da miji dama sai Allah domin sun shirya sun dinke sunci gaba da zamansu lafiya fiyeda da, zaman da bahijjan ta danyi agida lokacin da suka samu sabani da jabir yabawa mamanta damar fuskantarta sosai wanda har taji itama yanzu tana burin kasancewa cikin addinin islama, hakan ba karamin dadi yayiwa kowa ba, awurin jabir ta karbi Kalmar shahada sannan ta amshi sabon suna wato A'isha, wannan abuda yafaru ya kara sakawa bahijja imani domin yanzu tagane sau da dama abubuwan da suke faruwa arayuwarmu marassa dadi to hanyace kuma ta samun wani babban rabon acikin rayuwarmu domin lokacin da suka samu sabani da jabir ta shiga cikin tashin hankali sosai ashe mabudin alherine agareta bata saniba.
Yau takama ranar laraba tana kitchen tana aikin kayan kwadayinta jabir ya dawo daga office ya shigo ya isketa tana soya yar gullisuwa,
Abayanta ya tsaya "binti yau kuma me akeyi haka"
"Abbu Yar gullisuwa nakeyi"
Murmushi yayi ya leka cikin kaskon man, "dadina dake duk hanyar kwadayi kin santa binti, da alama nasake baki wani sabon babyn ko?"
"Nidai abbu kabari gaskiya" tafada ashagwabance, juyawa yayi yafita yana yi mata dariya.
Tun daga ranar ya zamana kullum ita kenan cikin hade haden kayan makulashe,yau kam salak ta yanka ta yanka masa tumatur da albasa da dafaffen kwai tasaka maggi da man gyada tafara ci,
Shigowar jabir ne ya katse mata laumar da ta dage tanayi,
"Abbu ga salad"
Akan kujera ya zauna yana kallonta, tacika sosai domin kirjinta yasake cika gashi hips dinta shima yasake budewa sosai,
"A'a binti nagode ci kayanki" yace da ita yana murmushi,
"To abbu ka samo min lalo, anjima tuwon amala zanyi miyar lalo sai in saka masa man shanu da garin yaji"
"Binti ina zan samo miki wani lalo yanzu?"
"Agidan malam za asamu"
"To naji ya isa, zan samo mikin"
Cin salak dinta taci gaba dayi yayinda shi kuma yana zaune yana kallonta, kullum kwadayinta sake karuwa yake domin bata da aiki sai shan tsami gaye, alawar madara, goba mai tsami da makamantansu amma tunda take neman kayan kwadayinta jabir bai taba kin samo mata ba duk abinda take so samomata yake domin har tambayarta yake idan zai fita yau kuma me ake kwadayi ita kam sai dai tayi murmushi tafada masa.
Lokaci yaci gaba da tafiya har cikin nata yafito domin yanzu watanshi 7 duk tabi ta dan kunkumbura, alokacin su ummu al'amin suka fara shirin zuwa gida,
Ana saura kwana biyu su dawo bahijja tafara kwasar kayayyakinta dake cikin dakin jabir domin dama rabi tana dakinta ne rabi tana dakinsa,cike da damuwa tashiga toilet dinsa ta kwaso inner wears dinta dake shanye wanda jabir ya wanke mata,
Kayan kwalliyarta dake kan mirror dinshi tafara tattarewa ranta acinkushe,shima kansa jabir din yana cikin damuwa domin yanzune ya kamata ya bata kulawa ta musamman domin cikin dake jikinta gashi yanzu bata yin minti 30 sai taci abinci shiyasa kullum da daddare sai ya tashi ya hada mata abinci taci koda kuwa cornflakes ne da madara. Ganin ta shiga damuwa yasashi kwantar mata da hankali har ta dan ji sassauci aranta.
Ana igobe ranar da su Ummu al'amin zasu dawo yan uwan ummun suka zo domin gyara mata sashenta, wannan shine karo nafarko da bahijja taga wani wanda ya danganci ummu al'amin.
Duk da tsohon cikin dake jikinta hakan bai hanata shiga kitchen ta dora musu girki ba, tuwon shinkafa tayi musu miyar agushi,
Dauka tayi ta kai musu tasamesu sunata faman aikace aikace domin babu laifi wurin yahada uban datti,
Zama tayi bayan ta ajiye musu abincin, tana nan wurinsu tana dan tattaya su aikin wata daga cikinsu ta zame tafadi "washhh ni jikar mutun hudu" wacce ta zame din tafada tana rike kunkuminta,
"Kijita maimakon kiyi salati zaki wani ce haka sai kace wata sabuwar tuba" wata daga cikinsu tafada, take bahijja taji ranta ya sosu, tun kafin abin yayi yawa ta mike dakyar tafita daga part din ta nufi nata, sam bata ma san cewar jabir ya dawo gidanba,dakinta ta Shiga tana hawaye "wai shin meyasa wasu mutanen suke yiwa wadanda suka karbi musulunci isgili?" Ta tambayi kanta,
Gaban mudubinta takarasa tana kuka domin abin ya bata mata rai, jabir yana daya dakin nata ya jiyo motsinta, binta yayi yaje ya tsaya abayanta tareda jiyo da ita ganin tana kuka yasanya kwakwalwarshi gano abinda yafaru,
"Binti keda yan uwan ummu al'amin ne ko?"
Girgiza kai tayi alamar a'a,
"Kar kiyi min karya binti nasan sune suka saka ki kuka kila cemiki sukayi ke ba asalin musulma bace"