Sashe 22
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ahankali ya bude kofa ya shiga hangota yayi zaune tanata tand'ar baki da loly pop a hannunta kan cinyarta kuma al'amin ne kwance yana bacci ta dage ta zubawa tv ido, ahankali yaje kusa da ita ya mika hannu zai dauki al'amin nan tayi wata zabura har tana tuttuje bandejin dake kan yatsanta wanda aka nad'e mata ciwon kafarta,
"Oh Sir ka tsorata ni banji shigowarka ba" tafada tana mai sauke ajiyar zuciya,
"Kawo na rage miki aiki na kaishi daki" mika hannu yayi ya daukeshi nan jikinshi da nata ya hadu wanda yayi sanadiyyar haifar musu da wani yanayi na musamman, daukarshi yayi ya nufi dakinta dashi yaje ya kwantar dashi tare da yi masa addu'o'in kwanciya bacci, bargo yaja ya rufa masa ya fito daga cikin dakin, agogo ya kalla 11 daidai,
"Ba zakije ki kwanta ba sai dare ya sake yi?"
"Sir sai anjima ina son na karasa kallo ne"
Jijjiga kai yayi, ya juya ya fita acan kasan ransa yana tunanin anya kuwa yarinyar nan bata da aljanu? Saboda kullum bata da aiki sai sauraron kida da kallon TV, Komawa sashensa yayi yaje ya kwanta.
Washe gari da safe bayan ta kammala yiwa al'amin wanka ta shiryashi cikin wata jar riga wacce ajiki aka rubuta Good boy da bakin wando,
"Oya take this, ka kaiwa watchman kace yaje ya siyo min ya baka ka kawo min kaji? Yawwa my boy" kudi ta bashi da yar karamar takarda wacce tayi rubutu ajiki,
Da gudu ya fice ita kuma ta shiga wanka, bakin gate yaje amma mai gadin baya nan sannan kofar gidan akulle take, da gudu ya juya ya shiga part din abbunshi,acikin dakinsa ya sameshi yana kwance akan gado,
"Sabahul khair abbuna, gashi inji anty na tace asiyo mata"
Karb'ar takardar jabir yayi ya bude ya tashi zaune, always ta rubuta ajikin takardar,
Drawer din gadonshi ya jawo anan yaga akwai saura guda biyu kasancewar yana siyowa ummu al'amin kuma anan yake ajiye mata sannan itama goodness din yakan siyo mata duk lokacin da yayi mata provision na kayan amfanin gida wannan watanne kawai ya manta,
Dauka yayi da kansa ya tafi kai mata shikuma al'amin ya haye gadonshi yana wasa, lokacin da ya shiga ta fito daga wanka tana daure da towel ta kwanta rub da ciki akan gado tana jiran al'amin ya kawo mata Aiken da tayi masa,
"Gashi" ya fada lokacin da yake mika mata ledar, zumbur ta tashi tana kallonsa,
"Thank you Sir"
"Kar ki sake aiken watchman siyo miki wannan abin, ai ina siyo miki wannan month dinma mantawa nayi"
"Sorry sir, bazan sake ba"
Kudinta ya mika mata da yar takardar ya juya ya fita
Cikin sauri ta shiga shiryawa tana wani dan kasaitaccen murmushi ita kadai, tana kammalawa ta shiga kitchen ta fara harhada abincin karyawa da abincin rana domin church zata tafi kuma ba zata dawo ba sai yamma,
Sai da ta gama kammala komai sannan ta debi kwanukan abincin ta nufi sashen jabir, lokacin da ta shiga yana tsaye a tsakiyar falonsa yana latsa wayarshi, kan dining ta wuce taje ta shirya komai ta nufi wurinshi da niyyar sanar dashi cewar zata tafi church, tana tsayawa al'amin na shigowa aguje, da gudu yazo ya banketa ta tafi ta fada jikin jabir, ko tsayawa al'amin baiyi ba yayi cikin dakin abbunshi da gudu,
Tana rungume ajikinsa ta dago kanta tana kallonshi shi dinma ita din yake kallo zuciyarsa dauke da tambayoyi kala kala na dalilin da yasa duk lokacin da ya tabata sai yaji wani sabon yanayi yana ziyartar shi koda kuwa dan yatsanta ya tab'a.
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[9/11, 10:50 AM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_59-60_
~~~Kasa sakinta daga jikinsa yayi yana rike da ita yabi jikinta da kallo kanta ta daura bakin dan kwali wanda yana iya hango tarin tulin gashin kitson attach din dake kanta wanda ya sauko har kan kafadunta, blue din body hug ce ajikinta tareda bakar skirt ta jeans wacce tayi mata dadas ajikinta,
"Anty, abbuna kuyi hakuri fitsari ne ya matse ni shiyasa na shigo da gudu"
Suka jiyo muryar al'amin yana fada daidai lokacin da yake fitowa daga cikin bedroom din jabir,
Cikin sanyinshi ya saketa ta matsa daga jikinsa kanta yana kasa,
"Sir zanje church" ta fada ahankali,
"Ok sai kin dawo" yafada tareda juyawa zuwa kan kujera ya zauna,
Kan al'amin ta shafa "my boy sai na dawo ko?"
"Sai kin dawo anty kinga nima gurin abbuna zanje muyi wasa tunda ke tafiya zakiyi ungunwa ki barni"
"Yawwa al'amin maza kayi wasan kafin na dawo kaji good boy"
Kumatunsa ta shafa ta juya ta fita ta koma sashenta agurguje tayi breakfast ta dauki katon Bible dinta da yar karamar jakarta ta fita daga gidan.
Lokacin da goodness ta fita daga falon jabir, ido ya zubawa al'amin yana tunanin irin shakuwar dake tsakanin al'amin din da goodness gashi Ummu ta fara yi masa maganar cewar ta samowa al'amin din sch akusa da inda take dan haka nan da d'an wani lokaci kankani zai kai mata shi,
"Abbu kaga anty idan zata yi addu'a sai ta rufe idonta kuma ko abinci zata ci wani lokacin sai ta rufe idonta sannan bata yin bisimilla"
Muryar al'amin ce ta dawo dashi hayyacinsa, hannun al'amin din ya kama yana fuskantarsa,
"Al'amin addininmu da addinin antynka ba iri daya bane, dan haka duk abinda kaga tayi irin na addininsu to kar kayi koyi da ita"
"Abbu to itama ka koya mata karatu ka sanar da ita ilimin addininmu saboda ka samu lada da yawa tunda annabi yace idan mutum ya mutu dukkan ayyukansa suna yankewa in banda abubuwa guda uku, sadaka mai gudana, ko ilimin da ake anfanuwa dashi ko kuma d'a na kwarai wanda zai rinka yi masa addu'a"
"Nasani al'amin, insha Allahu zan fahintar da antynka addininmu"
"Yawwa abbu jazakallahu khairan"
Hannunsa yaja suka koma dining table domin karyawa,Amma acikin zuciyarshi ya dauki niyyar koyar da goodness dukkanin kyawawan dabi'u wanda addinin musulunci yazo dasu kuma zai fahimtar da ita menene musulunci cikin salo da dabaru irin na d'a namiji.
Goodness bata samu damar dawowa gida ba sai wurin 6,tana shiga dakinta ta ajiye kayanta ta nufi sashen jabir a falo ta samesu sun baje al'amin yanata rubutu acikin exercise book shi kuma jabir yana rikeda littafin _fiqhul aulawiyyat_ yana nazarinsa,
Ahankali ta shiga idonta kan jabir tana kallonsa,
"Sannu sir" tace dashi tareda zama akusa da al'amin,
"Yawwa" yace da ita a takaice,
"Anty kin dawo? Nima kinga abbuna ne yasani rubutu"
"Dakyau my boy"
Dunkufar da kansa yayi yaci gaba da rubutun yayinda ita kuma ta fara kallon jabir kasa kasa tana nazarinsa acikin ranta, dan mitsitsin bakinsa dake burgeta akoda yaushe ta kalla ta lashi lebenta.
Suna nan zaune kowa yana abinda ke gabansa har lokacin salla ya gabato, hankalinta ta mayar kan tv din dake kunne tana faman aiki,
"Al'amin tashi maza kaje kayi alwala kazo muje masallaci". Ta jiyo muryar jabir yana yiwa al'amin magana cikin muryarsa sai dan karen sanyi,
"Na'am abbu" al'amin ya bashi amsa tareda rufe exercise book din da yake rubutu aciki,
Tana zaune tana kallo suka fita masallaci ganin zaman baya yi mata dadi ya sanyata mikewa ta koma sashenta ta shiga wanka ta fito ta shirya ta saka wani wando tied da rigarsa mai gajeren hannu purple colour, tana tsaka da fesa turare al'amin ya fado dakin,
"Anty kizo inji abbuna"
"Yana ina?"
"Yana falonshi yana kallo"
Tare suka fito ta kunna masa cartoon ita kuma ta wuce sashen jabir.
A falo ta tarar dashi yana jan cazbaha ga tv kuma ya kunna yana kallon din huda tv ya mayar da hankalinsa sosai wurin sauraron program din dasuke gabatarwa a lokacin mai taken _missing ingredient_ wanda sheikh Muhammad salah yake gabatarwa,
"Excuse me sir" ta fada ahankali, manyan idanuwansa ya dago ya kalleta kanta babu ko dan kwali ko yar hular ma da take sawa yau bata saka ba,
"Dauki wannan grass din ki dafa min da Lipton"
"Ok Sir"
Na'a na'ar ta dauka wacce ke ajiye akan center table ta juya ta fita, bin bayanta yayi da kallo tabbas dan sura tana da cikakkiyar surar da duk wani da namiji yake bukata a wurin mace,domin yar duma duma ce ita sam bata da rama, singalalinta kuwa cikarsa za tayi cinyar wata siririyar, idanuwansa ya dauke daga kallon kofa ya mayar dasu kan tv yana sauraron dawowarta.
Part dinta ta koma ta iske al'amin ya nutsu yana kallon cartoon dinsa, wuceshi tayi ta shiga cikin kitchen ta dafawa jabir na'a na'a ta juyo acikin dan karamin tea flask ta fito,
"Anty nima zan sha shayin" al'amin ya fada yana tashi zaune,
"Oya zo muje abbunka ya san maka"
Tashi yayi yabi bayanta, a yanda ta tafi ta barshi dazu yanzun ma haka ta dawo ta sameshi, hannun al'amin ta kama suka koma sashenta bayan jabir ya tsiyaya masa shayin a kofi,
"Wash anty na kona bakina"
"Ka ringa fifitawa da bakinka kafin kasha"
"Lah anty annabi ya hana hura abinsha da baki"
Kallonsa tayi ta jinjima kai "al'amin kenan kai kam komai kasani, ko wanne abu yana ajiye acikin brain dinka, maza kasha kazo muje muyi bacci yau bazan yi kallo ba".
***
Watan Ummu al'amin uku da tafiya ta kira jabir ta sanar dashi ya kai mata al'amin tun lokacin yaji babu dadi domin zai rabu da al'amin gashi uwa uba yasan goodness zata shiga wani hali na rashin abokin wasanta amma dole ne shi yanzu ya zame mata abokin wasan domin karta shiga halin zaman kunci acikin gidansa.
Sashenta ya shiga dawowarsa kenan daga office misalin karfe _5:30_ na yamma, part din nata tsit da alama babu kowa aciki hakan ya sashi komawa nasa, a falo ya jiyo hayaniyarsu sunata kokawa ita da al'amin yana kokarin sai ya saka mata kadangaren roba ajikinta ita kuma tsoronshi take, tana ganin jabir ta nufi wurinshi da gudu,
"Yawwa Sir kaga al'amin wai sai ya saka min lizard" ta fada tana haki,
"Abbu wlh na wasane fa bana gaske bane, anty tsoron kadangare take yau ko throughout bata zauna a falonta ba saboda da safe kadangare yabi ta corridor ya shiga falonta"
"Oh Sir ka tsorata ni banji shigowarka ba" tafada tana mai sauke ajiyar zuciya,
"Kawo na rage miki aiki na kaishi daki" mika hannu yayi ya daukeshi nan jikinshi da nata ya hadu wanda yayi sanadiyyar haifar musu da wani yanayi na musamman, daukarshi yayi ya nufi dakinta dashi yaje ya kwantar dashi tare da yi masa addu'o'in kwanciya bacci, bargo yaja ya rufa masa ya fito daga cikin dakin, agogo ya kalla 11 daidai,
"Ba zakije ki kwanta ba sai dare ya sake yi?"
"Sir sai anjima ina son na karasa kallo ne"
Jijjiga kai yayi, ya juya ya fita acan kasan ransa yana tunanin anya kuwa yarinyar nan bata da aljanu? Saboda kullum bata da aiki sai sauraron kida da kallon TV, Komawa sashensa yayi yaje ya kwanta.
Washe gari da safe bayan ta kammala yiwa al'amin wanka ta shiryashi cikin wata jar riga wacce ajiki aka rubuta Good boy da bakin wando,
"Oya take this, ka kaiwa watchman kace yaje ya siyo min ya baka ka kawo min kaji? Yawwa my boy" kudi ta bashi da yar karamar takarda wacce tayi rubutu ajiki,
Da gudu ya fice ita kuma ta shiga wanka, bakin gate yaje amma mai gadin baya nan sannan kofar gidan akulle take, da gudu ya juya ya shiga part din abbunshi,acikin dakinsa ya sameshi yana kwance akan gado,
"Sabahul khair abbuna, gashi inji anty na tace asiyo mata"
Karb'ar takardar jabir yayi ya bude ya tashi zaune, always ta rubuta ajikin takardar,
Drawer din gadonshi ya jawo anan yaga akwai saura guda biyu kasancewar yana siyowa ummu al'amin kuma anan yake ajiye mata sannan itama goodness din yakan siyo mata duk lokacin da yayi mata provision na kayan amfanin gida wannan watanne kawai ya manta,
Dauka yayi da kansa ya tafi kai mata shikuma al'amin ya haye gadonshi yana wasa, lokacin da ya shiga ta fito daga wanka tana daure da towel ta kwanta rub da ciki akan gado tana jiran al'amin ya kawo mata Aiken da tayi masa,
"Gashi" ya fada lokacin da yake mika mata ledar, zumbur ta tashi tana kallonsa,
"Thank you Sir"
"Kar ki sake aiken watchman siyo miki wannan abin, ai ina siyo miki wannan month dinma mantawa nayi"
"Sorry sir, bazan sake ba"
Kudinta ya mika mata da yar takardar ya juya ya fita
Cikin sauri ta shiga shiryawa tana wani dan kasaitaccen murmushi ita kadai, tana kammalawa ta shiga kitchen ta fara harhada abincin karyawa da abincin rana domin church zata tafi kuma ba zata dawo ba sai yamma,
Sai da ta gama kammala komai sannan ta debi kwanukan abincin ta nufi sashen jabir, lokacin da ta shiga yana tsaye a tsakiyar falonsa yana latsa wayarshi, kan dining ta wuce taje ta shirya komai ta nufi wurinshi da niyyar sanar dashi cewar zata tafi church, tana tsayawa al'amin na shigowa aguje, da gudu yazo ya banketa ta tafi ta fada jikin jabir, ko tsayawa al'amin baiyi ba yayi cikin dakin abbunshi da gudu,
Tana rungume ajikinsa ta dago kanta tana kallonshi shi dinma ita din yake kallo zuciyarsa dauke da tambayoyi kala kala na dalilin da yasa duk lokacin da ya tabata sai yaji wani sabon yanayi yana ziyartar shi koda kuwa dan yatsanta ya tab'a.
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[9/11, 10:50 AM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
_*NA*_
_*UMMI A'ISHA*_
_59-60_
~~~Kasa sakinta daga jikinsa yayi yana rike da ita yabi jikinta da kallo kanta ta daura bakin dan kwali wanda yana iya hango tarin tulin gashin kitson attach din dake kanta wanda ya sauko har kan kafadunta, blue din body hug ce ajikinta tareda bakar skirt ta jeans wacce tayi mata dadas ajikinta,
"Anty, abbuna kuyi hakuri fitsari ne ya matse ni shiyasa na shigo da gudu"
Suka jiyo muryar al'amin yana fada daidai lokacin da yake fitowa daga cikin bedroom din jabir,
Cikin sanyinshi ya saketa ta matsa daga jikinsa kanta yana kasa,
"Sir zanje church" ta fada ahankali,
"Ok sai kin dawo" yafada tareda juyawa zuwa kan kujera ya zauna,
Kan al'amin ta shafa "my boy sai na dawo ko?"
"Sai kin dawo anty kinga nima gurin abbuna zanje muyi wasa tunda ke tafiya zakiyi ungunwa ki barni"
"Yawwa al'amin maza kayi wasan kafin na dawo kaji good boy"
Kumatunsa ta shafa ta juya ta fita ta koma sashenta agurguje tayi breakfast ta dauki katon Bible dinta da yar karamar jakarta ta fita daga gidan.
Lokacin da goodness ta fita daga falon jabir, ido ya zubawa al'amin yana tunanin irin shakuwar dake tsakanin al'amin din da goodness gashi Ummu ta fara yi masa maganar cewar ta samowa al'amin din sch akusa da inda take dan haka nan da d'an wani lokaci kankani zai kai mata shi,
"Abbu kaga anty idan zata yi addu'a sai ta rufe idonta kuma ko abinci zata ci wani lokacin sai ta rufe idonta sannan bata yin bisimilla"
Muryar al'amin ce ta dawo dashi hayyacinsa, hannun al'amin din ya kama yana fuskantarsa,
"Al'amin addininmu da addinin antynka ba iri daya bane, dan haka duk abinda kaga tayi irin na addininsu to kar kayi koyi da ita"
"Abbu to itama ka koya mata karatu ka sanar da ita ilimin addininmu saboda ka samu lada da yawa tunda annabi yace idan mutum ya mutu dukkan ayyukansa suna yankewa in banda abubuwa guda uku, sadaka mai gudana, ko ilimin da ake anfanuwa dashi ko kuma d'a na kwarai wanda zai rinka yi masa addu'a"
"Nasani al'amin, insha Allahu zan fahintar da antynka addininmu"
"Yawwa abbu jazakallahu khairan"
Hannunsa yaja suka koma dining table domin karyawa,Amma acikin zuciyarshi ya dauki niyyar koyar da goodness dukkanin kyawawan dabi'u wanda addinin musulunci yazo dasu kuma zai fahimtar da ita menene musulunci cikin salo da dabaru irin na d'a namiji.
Goodness bata samu damar dawowa gida ba sai wurin 6,tana shiga dakinta ta ajiye kayanta ta nufi sashen jabir a falo ta samesu sun baje al'amin yanata rubutu acikin exercise book shi kuma jabir yana rikeda littafin _fiqhul aulawiyyat_ yana nazarinsa,
Ahankali ta shiga idonta kan jabir tana kallonsa,
"Sannu sir" tace dashi tareda zama akusa da al'amin,
"Yawwa" yace da ita a takaice,
"Anty kin dawo? Nima kinga abbuna ne yasani rubutu"
"Dakyau my boy"
Dunkufar da kansa yayi yaci gaba da rubutun yayinda ita kuma ta fara kallon jabir kasa kasa tana nazarinsa acikin ranta, dan mitsitsin bakinsa dake burgeta akoda yaushe ta kalla ta lashi lebenta.
Suna nan zaune kowa yana abinda ke gabansa har lokacin salla ya gabato, hankalinta ta mayar kan tv din dake kunne tana faman aiki,
"Al'amin tashi maza kaje kayi alwala kazo muje masallaci". Ta jiyo muryar jabir yana yiwa al'amin magana cikin muryarsa sai dan karen sanyi,
"Na'am abbu" al'amin ya bashi amsa tareda rufe exercise book din da yake rubutu aciki,
Tana zaune tana kallo suka fita masallaci ganin zaman baya yi mata dadi ya sanyata mikewa ta koma sashenta ta shiga wanka ta fito ta shirya ta saka wani wando tied da rigarsa mai gajeren hannu purple colour, tana tsaka da fesa turare al'amin ya fado dakin,
"Anty kizo inji abbuna"
"Yana ina?"
"Yana falonshi yana kallo"
Tare suka fito ta kunna masa cartoon ita kuma ta wuce sashen jabir.
A falo ta tarar dashi yana jan cazbaha ga tv kuma ya kunna yana kallon din huda tv ya mayar da hankalinsa sosai wurin sauraron program din dasuke gabatarwa a lokacin mai taken _missing ingredient_ wanda sheikh Muhammad salah yake gabatarwa,
"Excuse me sir" ta fada ahankali, manyan idanuwansa ya dago ya kalleta kanta babu ko dan kwali ko yar hular ma da take sawa yau bata saka ba,
"Dauki wannan grass din ki dafa min da Lipton"
"Ok Sir"
Na'a na'ar ta dauka wacce ke ajiye akan center table ta juya ta fita, bin bayanta yayi da kallo tabbas dan sura tana da cikakkiyar surar da duk wani da namiji yake bukata a wurin mace,domin yar duma duma ce ita sam bata da rama, singalalinta kuwa cikarsa za tayi cinyar wata siririyar, idanuwansa ya dauke daga kallon kofa ya mayar dasu kan tv yana sauraron dawowarta.
Part dinta ta koma ta iske al'amin ya nutsu yana kallon cartoon dinsa, wuceshi tayi ta shiga cikin kitchen ta dafawa jabir na'a na'a ta juyo acikin dan karamin tea flask ta fito,
"Anty nima zan sha shayin" al'amin ya fada yana tashi zaune,
"Oya zo muje abbunka ya san maka"
Tashi yayi yabi bayanta, a yanda ta tafi ta barshi dazu yanzun ma haka ta dawo ta sameshi, hannun al'amin ta kama suka koma sashenta bayan jabir ya tsiyaya masa shayin a kofi,
"Wash anty na kona bakina"
"Ka ringa fifitawa da bakinka kafin kasha"
"Lah anty annabi ya hana hura abinsha da baki"
Kallonsa tayi ta jinjima kai "al'amin kenan kai kam komai kasani, ko wanne abu yana ajiye acikin brain dinka, maza kasha kazo muje muyi bacci yau bazan yi kallo ba".
***
Watan Ummu al'amin uku da tafiya ta kira jabir ta sanar dashi ya kai mata al'amin tun lokacin yaji babu dadi domin zai rabu da al'amin gashi uwa uba yasan goodness zata shiga wani hali na rashin abokin wasanta amma dole ne shi yanzu ya zame mata abokin wasan domin karta shiga halin zaman kunci acikin gidansa.
Sashenta ya shiga dawowarsa kenan daga office misalin karfe _5:30_ na yamma, part din nata tsit da alama babu kowa aciki hakan ya sashi komawa nasa, a falo ya jiyo hayaniyarsu sunata kokawa ita da al'amin yana kokarin sai ya saka mata kadangaren roba ajikinta ita kuma tsoronshi take, tana ganin jabir ta nufi wurinshi da gudu,
"Yawwa Sir kaga al'amin wai sai ya saka min lizard" ta fada tana haki,
"Abbu wlh na wasane fa bana gaske bane, anty tsoron kadangare take yau ko throughout bata zauna a falonta ba saboda da safe kadangare yabi ta corridor ya shiga falonta"