Sashe 45
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hijabinta ta dauka tayi salla tana idarwa tayi musu addu'o'i musamman ma kan samun zuri'a tagari duk da cewar jiya taji jabir ya dade yana yi musu wannan addu'ar lokacin da abubuwa zasu faru,
Cire hijabin tayi ta tashi bayan ta kammala addu'ar,gashin kanta taje gaban mirror ta fara tajewa amma kuma sai kamshin man datayi amfani dashi wurin wankewa yake, domin ita ba zata iya kwarawa kanta ruwa kawai tabarshi ahaka ba har sai tasaka man wanke gashi ta wankeshi domin idan aka zubawa gashi ruwa kawai aka kyaleshi to zakaji yana wani irin tashi marar dadi har maigida yaji babu dadi,
Cure gashin tayi ta daureshi ta nufi hanyar fita, akofa sukayi kicibus da jabir yana kokarin shigowa yasha wando iya gwiwa da yar shirt dinshi bashida banbanci da samari irin yan makarantar nan,
Da sauri ta juya masa baya tayi niyyar komawa cikin dakin, a tsakiyar dakin ta tsaya tana karewa royal bed dinsa kallo wanda yake a hargutse,
Jinsa tayi ta bayanta ya rungumeta ya zagayeta da hannayenshi gamida ziro kansa ta kan kafadarta,
"Binti kin tashi?" Yafada acikin rada,
"Abbu good morning"
"Morning bintin abbu, how was your night?"
Shiru tayi tana yamutsa fuskarta,acikin ranta ta tace "too harsh"
"Binti ba zaki amsa ba?"
Jiyo da ita yayi sai ta rufe idonta sai ga hawaye sharrr sun fara zuba akan idonta,
Baki bude ya kalleta dama a banza ma tana yin kuka inaga yanzu da dalili ya samu,
"Kiyi hakuri binti kinji, nine ko? Yi hakuri"
Hadata yayi da jikinsa yafara rarrashinta har ya samu ta daina hawayen, hanmunta ya kama ya zaunar da ita akan wani dan karamin stool yaje yafara gyara mata gadon, kallonshi kawai take yanda yake da sanyin nan to komai ma nashi a sanyaye yake gudanarwa dan haka ya zame mata dole ta nemo mafita duk da tasan ba ita kadai bace mai irin wannan matsalar ba mata da dama suna fuskantarta,
Hannun nata ya sake kamawa ya rakata kan gadon ta kwanta, agefenta ya zauna ya fara jan yan yatsun kafarta, da haka ya ware ya fara yi mata tausa ajikinta, kamar wacce take jira sai bacci, zama yayi yana kallonta acikin ranshi yana tunanin irin banbancin dake tsakaninta da ummu domin yagane akwai banbance banbance masu tarin yawa bawai kasancewarta budurwa kawai ba ko a ta fannin ni'ima ni'imarta tasha banban data ummu, kodan ita bahijjan tana shan kayan marmari ne da sauran abubuwan datake hadawa da kanta,
Haka yayita yan tunane tunanensa yana zaune yana kallonta, drewar din gefen gadonshi ya bude yafara bincike har ya binciko abinda yake nema, wani dan kyakkyawan zobe ne na gold mai kyau, dan yatsanta na hagu ya kamata ya saka mata zoben, ya kwanta agefenta yana makale da hannunta,
Sun jima suna baccin kafin jabir ya tashi yana kallon bahijja wacce keta faman baccinta tana fitar da numfashi ahankali, ahankali yafara kokarin zare hannunsa daga cikin nata, yana gama zarewa ta tashi firgigit,sai kuma tafara kallonsu shida ita, sunkuyar da kanta tayi tana kallon kayan jikinta,
"Abbu kagani kayanka sunyi min yawa ko"
Murmushi jabir yayi ya matsa kusa da ita "amma ai sunyi miki kyau binti"
Kallonshi tayi tana tuna wani abu acikin ranta wanda ita kadai tasan ko me take tunawa,
"Abbu yunwa nakeji" tafada tana turo baki,
"Zakici abinci yanzun nan binti, ai nasan bakya wasa da abinci shiyasa kike da karfi sosai kusan ma kinfini karfin"
"Haba abbu wanne karfi nafika? Tayaya kasan haka alhalin nida ba dambe muka yi dakai ba"
Sakin hannunta yayi yana murmushi tare da kokarin sauka daga kan gadon yana cewa "dambe na nawa kuma binti"
Falo ya fita ya shigo mata da kayan Karin kumallon da ya shirya mata shida kansa, akasa ya ajiye mata ya kamota ya sauko da ita,
Kazar jiya taga ya dumama mata sannan ya soya mata kwai ya dan soya mata dankali da plantain, sai ruwan tea, "yau zanci girkin maza kenan" tafada aranta,
Dankalin taci da plantain din tasha tea ta tashi tana mik'a, "abbu natafi dakina sai ka taho"
Kafin ya dago yayi mata magana har takai bakin kofa hakan ya sashi yin shiru, fita tayi ta koma dakinta tana zuwa tafada gado ta janyo katuwar teddy dinta ta rungume sai alokacin duk abubuwan da suka wakana tsakaninta da jabir suka fara dawo mata, idanuwanta ta lumshe tana jin wani irin farin ciki har cikin ranta, tana nan kwance har jabir ya shigo kunnensa makale da waya yana magana amma daga yanda ta fuskanta da al'amin yake wayar domin ta jiyoshi yana cewa
"Al'amin antyn naka ai sai kayi mata sannu saboda bata dan jin dadi"
Wayar ya mika mata yana shirin zama akusa da ita gamida zare teddy din dake makale ajikinta,
"Ni ni nidai lafiya ta kalau" tafada tana turo baki, dan yatsan da ya saka mata zobe ya kamo yafara ja yana cewa "yanzu ni zaki rinka rungumewa ba teddy ba binti, wayar ta kara a kunnenta tafara magana,
"Al'amin, yakake?"
"Anty fine" yanda yayi maganar sai taji tamkar mahaifinsa, sama sama ta biyeshi suka danyi shirmensu da suka saba amma yau bata bari sunyi nisa ba saboda wani iri takeji ajikinta sannan gashi gabanta sai faman faduwa yake yi,
"Abbu bazaka fita bane office?" Ta tambayeshi bayan ta ajiye wayar,
"Yau ina gidan nan tare dake binti, ko bakya son in zauna natafi?"
Kanta ta kwantar ajikin kafadarsa, "inaso mana abbu amma tunda natashi nake jin gabana yana faduwa"
"Kina yin wasa da addu'a binti, bakya son yin addu'a"
"Abbu wlh inayi"
Kafin ya sake yin magana wayarta tafara kara, cikin hanzari ta daukota tana duba sunan wanda yake kiran.
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[10/19, 5:49 PM] +234 903 993 4050: [10/11, 11:33 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_106-110_
~~~Sunan yayarta anty Bilkisu ta gani, cikin hanzari ta kara wayar akunnenta jikinta har rawa yake yi, suna gaisawa yayar tata take sanar da ita cewar suna asibiti an kwantar da ma,
Cikin rawar baki ta tambayeta wanne asibiti ne, tana fada mata ta ajiye wayar tana hawaye, janta jikinshi jabir yayi yafara shafar bayanta yana tambayarta,
"Binti waye bashida lafiya?"
Cikin kuka tace "ma ce"
Hawayen dake sauka akan fuskarta ya soma share mata amma yana jin tausayinta ga wata irin zazzafar soyayyarta har acikin jinin jikinsa zuwa bargonsa, yasan yanzu dole ta shiga damuwa saboda fushin mahaifiyarta da zata fuskanta,
" kukan ya isa haka binti, kiyi shiru kinji, ko bakya son nabarki kije?"
Kai ta girgiza cikin kuka tayi magana "ina so"
"To kiyi shiru ki shirya muje"
Idonta har lokacin taf da kwalla take kallonsa "abbu jikina ciwo yake yimin gashi duk yayi tsami"
"Am sorry binti, ki daure kinji"
Ahankali ta janye jikinta daga nashi ta tashi taje gaban drewar din kayanta ta bude, wata blue din doguwar riga ta zaro ta jiyo tana kallonsa ya gane abinda take nufi, ganin yana zaune yana kallonta yasata fita taje dayan bedroom din ta sako rigar ta dawo, binta yayi da murmushi agaskiya bahijja akwai shirme in banda haka to maganar boye boye kuma ai takare a tsakaninsu,
K'aton hijabi ta saka kalar ruwan madara duk wadannan abubuwan tana yinsune kamar kazar da kwai ya fashewa aciki domin sam yau bata da kuzari dakyar take motsa jikinta,
Mikewa yayi yaja hannunta suka fita zuwa sashensa, afalo ta zauna taki binshi cikin dakin, tana nan zaune ya fito cikin farin boyel da hula ga wani mayen kamshi da yake tashi daga jikinsa wanda yake barazanar tarwatsa numfashinta,
"Tashi muje" shine kawai abinda ya fada, tashi tayi tabi bayansa suka fita har suka karasa tsakar gidan bata yi magana ba tana biye dashi yana kiran driver,
Abaya dukkaninsu suka zauna driver yaja motar suka bar harabar gidan suka nufi Nakowa clinic, jikinta jabir ya matsa ya kamo yan yatsunta ya fara murza zoben da ya sanya mata,
"Binti bakiga kyautar da na bakiba shine babu ko godiya?" Yayi hakane domin ya dan sanyaya mata zuciyarta, aikuwa murmushin yak'e tayi tana kallon kyakkyawar fuskarsa,
"Ni kyautar da nabaka godiyar kayi min?" Tafada cikeda kunya,
"Wacce kyauta kika bani binti?" Ya tambayeta yana ware idanuwansa akan fuskarta,
"Nima namanta tunda kaima ka manta" tace dashi tana tutturo bakinta,
"Idan baki daina turo min bakin nan ba idan na kamashi sai kin fadawa yan garinku"
"Abbu okene kenan, kasan mu canne garinmu" tafada tana murmushi,
Jin alamun tsayawar motar ya dawo dasu cikin hayyacinsu sai alokacin suka san sun karaso asibitin, hakika haka ya kamata kowanne miji ya kasance ya rinka mantar da matarsa duk wani bacin rai ta hanyar maye gurbin bakin cikinta da farin ciki amma wani maimakon haka saima kara mata bacin ran zaiyi.
Hannunta ya kama suka fita suka tasamma cikin asibitin, tun daga nesa ta hango papa da yayarta suna tsattsaye duk hankulansu atashe,
Jin jikinta tayi ya sake yin sanyi, koda suka karasa wurinsu kasa magana tayi sai jabir ne yafara tambayar halin da ma din take ciki da kuma abinda ya faru,
"Tun jiya da mangariba muke nan amma har yanzu bata farfado ba, yanke jiki tayi ta fadi sakamakon jin muna maganar musuluntar da bahijja tayi nida Bilkisu, ashe lokacin ta dawo gidan daga church tana ji ta kwalla kara ta zube awurin, yanzu doctor yace zuciyarta bugawa tayi watakila ma sai sunyi mata aiki"
Babansu ya fada cikeda alhini, fuskarsa dauke da damuwa,
"Allah yabata lafiya, Allah ya tashi kafadunta" jabir yafada yana mai jin tausayinsu, ita kam bahijja tana daga tsaye tana faman hawaye,
Anty Bilkisu ce ta taso tazo inda take ta kama hannunta taje ta zaunar da ita akan dogon bencin da aka tanada awurin domin masu zaman jinya, baki suka fara bata dukkaninsu har ta samu ta daina kukan da take yi,
Suna nan zaune suna jiran tsammani domin kosu bilkisun da suka kwana awurinta basu samu ganinta ba balle bahijja da tazo yanzu, amma ga doctor nan da sauran nurses sunata kai kawo zuwa dakin da ma din take kwance aciki.
Cire hijabin tayi ta tashi bayan ta kammala addu'ar,gashin kanta taje gaban mirror ta fara tajewa amma kuma sai kamshin man datayi amfani dashi wurin wankewa yake, domin ita ba zata iya kwarawa kanta ruwa kawai tabarshi ahaka ba har sai tasaka man wanke gashi ta wankeshi domin idan aka zubawa gashi ruwa kawai aka kyaleshi to zakaji yana wani irin tashi marar dadi har maigida yaji babu dadi,
Cure gashin tayi ta daureshi ta nufi hanyar fita, akofa sukayi kicibus da jabir yana kokarin shigowa yasha wando iya gwiwa da yar shirt dinshi bashida banbanci da samari irin yan makarantar nan,
Da sauri ta juya masa baya tayi niyyar komawa cikin dakin, a tsakiyar dakin ta tsaya tana karewa royal bed dinsa kallo wanda yake a hargutse,
Jinsa tayi ta bayanta ya rungumeta ya zagayeta da hannayenshi gamida ziro kansa ta kan kafadarta,
"Binti kin tashi?" Yafada acikin rada,
"Abbu good morning"
"Morning bintin abbu, how was your night?"
Shiru tayi tana yamutsa fuskarta,acikin ranta ta tace "too harsh"
"Binti ba zaki amsa ba?"
Jiyo da ita yayi sai ta rufe idonta sai ga hawaye sharrr sun fara zuba akan idonta,
Baki bude ya kalleta dama a banza ma tana yin kuka inaga yanzu da dalili ya samu,
"Kiyi hakuri binti kinji, nine ko? Yi hakuri"
Hadata yayi da jikinsa yafara rarrashinta har ya samu ta daina hawayen, hanmunta ya kama ya zaunar da ita akan wani dan karamin stool yaje yafara gyara mata gadon, kallonshi kawai take yanda yake da sanyin nan to komai ma nashi a sanyaye yake gudanarwa dan haka ya zame mata dole ta nemo mafita duk da tasan ba ita kadai bace mai irin wannan matsalar ba mata da dama suna fuskantarta,
Hannun nata ya sake kamawa ya rakata kan gadon ta kwanta, agefenta ya zauna ya fara jan yan yatsun kafarta, da haka ya ware ya fara yi mata tausa ajikinta, kamar wacce take jira sai bacci, zama yayi yana kallonta acikin ranshi yana tunanin irin banbancin dake tsakaninta da ummu domin yagane akwai banbance banbance masu tarin yawa bawai kasancewarta budurwa kawai ba ko a ta fannin ni'ima ni'imarta tasha banban data ummu, kodan ita bahijjan tana shan kayan marmari ne da sauran abubuwan datake hadawa da kanta,
Haka yayita yan tunane tunanensa yana zaune yana kallonta, drewar din gefen gadonshi ya bude yafara bincike har ya binciko abinda yake nema, wani dan kyakkyawan zobe ne na gold mai kyau, dan yatsanta na hagu ya kamata ya saka mata zoben, ya kwanta agefenta yana makale da hannunta,
Sun jima suna baccin kafin jabir ya tashi yana kallon bahijja wacce keta faman baccinta tana fitar da numfashi ahankali, ahankali yafara kokarin zare hannunsa daga cikin nata, yana gama zarewa ta tashi firgigit,sai kuma tafara kallonsu shida ita, sunkuyar da kanta tayi tana kallon kayan jikinta,
"Abbu kagani kayanka sunyi min yawa ko"
Murmushi jabir yayi ya matsa kusa da ita "amma ai sunyi miki kyau binti"
Kallonshi tayi tana tuna wani abu acikin ranta wanda ita kadai tasan ko me take tunawa,
"Abbu yunwa nakeji" tafada tana turo baki,
"Zakici abinci yanzun nan binti, ai nasan bakya wasa da abinci shiyasa kike da karfi sosai kusan ma kinfini karfin"
"Haba abbu wanne karfi nafika? Tayaya kasan haka alhalin nida ba dambe muka yi dakai ba"
Sakin hannunta yayi yana murmushi tare da kokarin sauka daga kan gadon yana cewa "dambe na nawa kuma binti"
Falo ya fita ya shigo mata da kayan Karin kumallon da ya shirya mata shida kansa, akasa ya ajiye mata ya kamota ya sauko da ita,
Kazar jiya taga ya dumama mata sannan ya soya mata kwai ya dan soya mata dankali da plantain, sai ruwan tea, "yau zanci girkin maza kenan" tafada aranta,
Dankalin taci da plantain din tasha tea ta tashi tana mik'a, "abbu natafi dakina sai ka taho"
Kafin ya dago yayi mata magana har takai bakin kofa hakan ya sashi yin shiru, fita tayi ta koma dakinta tana zuwa tafada gado ta janyo katuwar teddy dinta ta rungume sai alokacin duk abubuwan da suka wakana tsakaninta da jabir suka fara dawo mata, idanuwanta ta lumshe tana jin wani irin farin ciki har cikin ranta, tana nan kwance har jabir ya shigo kunnensa makale da waya yana magana amma daga yanda ta fuskanta da al'amin yake wayar domin ta jiyoshi yana cewa
"Al'amin antyn naka ai sai kayi mata sannu saboda bata dan jin dadi"
Wayar ya mika mata yana shirin zama akusa da ita gamida zare teddy din dake makale ajikinta,
"Ni ni nidai lafiya ta kalau" tafada tana turo baki, dan yatsan da ya saka mata zobe ya kamo yafara ja yana cewa "yanzu ni zaki rinka rungumewa ba teddy ba binti, wayar ta kara a kunnenta tafara magana,
"Al'amin, yakake?"
"Anty fine" yanda yayi maganar sai taji tamkar mahaifinsa, sama sama ta biyeshi suka danyi shirmensu da suka saba amma yau bata bari sunyi nisa ba saboda wani iri takeji ajikinta sannan gashi gabanta sai faman faduwa yake yi,
"Abbu bazaka fita bane office?" Ta tambayeshi bayan ta ajiye wayar,
"Yau ina gidan nan tare dake binti, ko bakya son in zauna natafi?"
Kanta ta kwantar ajikin kafadarsa, "inaso mana abbu amma tunda natashi nake jin gabana yana faduwa"
"Kina yin wasa da addu'a binti, bakya son yin addu'a"
"Abbu wlh inayi"
Kafin ya sake yin magana wayarta tafara kara, cikin hanzari ta daukota tana duba sunan wanda yake kiran.
_*Ummi Shatu*_👌🏻
[10/19, 5:49 PM] +234 903 993 4050: [10/11, 11:33 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_106-110_
~~~Sunan yayarta anty Bilkisu ta gani, cikin hanzari ta kara wayar akunnenta jikinta har rawa yake yi, suna gaisawa yayar tata take sanar da ita cewar suna asibiti an kwantar da ma,
Cikin rawar baki ta tambayeta wanne asibiti ne, tana fada mata ta ajiye wayar tana hawaye, janta jikinshi jabir yayi yafara shafar bayanta yana tambayarta,
"Binti waye bashida lafiya?"
Cikin kuka tace "ma ce"
Hawayen dake sauka akan fuskarta ya soma share mata amma yana jin tausayinta ga wata irin zazzafar soyayyarta har acikin jinin jikinsa zuwa bargonsa, yasan yanzu dole ta shiga damuwa saboda fushin mahaifiyarta da zata fuskanta,
" kukan ya isa haka binti, kiyi shiru kinji, ko bakya son nabarki kije?"
Kai ta girgiza cikin kuka tayi magana "ina so"
"To kiyi shiru ki shirya muje"
Idonta har lokacin taf da kwalla take kallonsa "abbu jikina ciwo yake yimin gashi duk yayi tsami"
"Am sorry binti, ki daure kinji"
Ahankali ta janye jikinta daga nashi ta tashi taje gaban drewar din kayanta ta bude, wata blue din doguwar riga ta zaro ta jiyo tana kallonsa ya gane abinda take nufi, ganin yana zaune yana kallonta yasata fita taje dayan bedroom din ta sako rigar ta dawo, binta yayi da murmushi agaskiya bahijja akwai shirme in banda haka to maganar boye boye kuma ai takare a tsakaninsu,
K'aton hijabi ta saka kalar ruwan madara duk wadannan abubuwan tana yinsune kamar kazar da kwai ya fashewa aciki domin sam yau bata da kuzari dakyar take motsa jikinta,
Mikewa yayi yaja hannunta suka fita zuwa sashensa, afalo ta zauna taki binshi cikin dakin, tana nan zaune ya fito cikin farin boyel da hula ga wani mayen kamshi da yake tashi daga jikinsa wanda yake barazanar tarwatsa numfashinta,
"Tashi muje" shine kawai abinda ya fada, tashi tayi tabi bayansa suka fita har suka karasa tsakar gidan bata yi magana ba tana biye dashi yana kiran driver,
Abaya dukkaninsu suka zauna driver yaja motar suka bar harabar gidan suka nufi Nakowa clinic, jikinta jabir ya matsa ya kamo yan yatsunta ya fara murza zoben da ya sanya mata,
"Binti bakiga kyautar da na bakiba shine babu ko godiya?" Yayi hakane domin ya dan sanyaya mata zuciyarta, aikuwa murmushin yak'e tayi tana kallon kyakkyawar fuskarsa,
"Ni kyautar da nabaka godiyar kayi min?" Tafada cikeda kunya,
"Wacce kyauta kika bani binti?" Ya tambayeta yana ware idanuwansa akan fuskarta,
"Nima namanta tunda kaima ka manta" tace dashi tana tutturo bakinta,
"Idan baki daina turo min bakin nan ba idan na kamashi sai kin fadawa yan garinku"
"Abbu okene kenan, kasan mu canne garinmu" tafada tana murmushi,
Jin alamun tsayawar motar ya dawo dasu cikin hayyacinsu sai alokacin suka san sun karaso asibitin, hakika haka ya kamata kowanne miji ya kasance ya rinka mantar da matarsa duk wani bacin rai ta hanyar maye gurbin bakin cikinta da farin ciki amma wani maimakon haka saima kara mata bacin ran zaiyi.
Hannunta ya kama suka fita suka tasamma cikin asibitin, tun daga nesa ta hango papa da yayarta suna tsattsaye duk hankulansu atashe,
Jin jikinta tayi ya sake yin sanyi, koda suka karasa wurinsu kasa magana tayi sai jabir ne yafara tambayar halin da ma din take ciki da kuma abinda ya faru,
"Tun jiya da mangariba muke nan amma har yanzu bata farfado ba, yanke jiki tayi ta fadi sakamakon jin muna maganar musuluntar da bahijja tayi nida Bilkisu, ashe lokacin ta dawo gidan daga church tana ji ta kwalla kara ta zube awurin, yanzu doctor yace zuciyarta bugawa tayi watakila ma sai sunyi mata aiki"
Babansu ya fada cikeda alhini, fuskarsa dauke da damuwa,
"Allah yabata lafiya, Allah ya tashi kafadunta" jabir yafada yana mai jin tausayinsu, ita kam bahijja tana daga tsaye tana faman hawaye,
Anty Bilkisu ce ta taso tazo inda take ta kama hannunta taje ta zaunar da ita akan dogon bencin da aka tanada awurin domin masu zaman jinya, baki suka fara bata dukkaninsu har ta samu ta daina kukan da take yi,
Suna nan zaune suna jiran tsammani domin kosu bilkisun da suka kwana awurinta basu samu ganinta ba balle bahijja da tazo yanzu, amma ga doctor nan da sauran nurses sunata kai kawo zuwa dakin da ma din take kwance aciki.