Sashe 62
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wannan babyn mai kwadayi ce irin mamanta kalli yadda take lasar lebe" yafada cikeda zolaya,kiran salla yayiwa jaririyar akunnenta na dama sannan ya koma na hagu nanma yayi mata,yayi mata huduba, zam zam da dabino ya ciro daga cikin aljihunsa ya disa mata abaki sannan ya tauna dabinon ya kai bakinshi kan nata ya fara lasa mata, dayake babyn mai kwadayi ce nan tafara shan ruwan dabinon,
Kallonsu bahijja tayi shida babyn "amma kuma komai nata irin na abbunta ne"
Kallon bakinshi tayi ta kalli bakin yarinyar "lahh abbu harfa bakinku iri daya ne"
Kafin ya bata amsa su mamanta da anty Bilkisu sun shigo harda papa, nan jabir ya basu jaririyar ya fita,a reception ya haduda mahaifinshi da sauran matan gidansu suma suna kokarin shigowa, bai bisu dakinba yawuce,
Wurin 12:30 yadawo asibitin lokacin babu kowa sai anty bilkisu jaririyar ya dauka yayi kan gadon da bahijja ke kwance da ita, kallonshi kawai bahijja take saboda yayi wanka yayi fes cikin farar shadda babu hula akanshi.
Wani irin kyau taga yayi mata sosai domin yafito kamar dan saurayi das dashi,
Agefenta ya zauna yana gyarawa babyn zama ajikinshi,
"Al'amin yayi nacin sai ya biyoni amma ban taho dashi ba saboda dare yayi, sai gobe zai zo yaga kanwarshi"
"Abbu dama ka taho min dashi"
Kallonta yayi yakai hannunshi kan kafafuwanta yafara dannawa ahankali, "binti har yanzu fa akunbure kike"
"Bp dina ne bai sauka ba abbu sai nan da wani lokaci"
"To Allah ya baki lafiya ya raya baby ya kawo kannenta kwana kusa"
Juya baya tayi tana cewa "hum um, ni yanzu sai na dade ban sake haihuwa ba abbu, nasha wahala dayawa"
Murmushi jabir yayi yana kallonta yadda ta juya baya "nima zan so ki huta din amma kuma hakan ba mai yiyuwa bane, kinga ummun al'amin har yau itama bata sake haihuwa ba mutane har cewa suke yi wai nine bana son haihuwa"
Juyowa bahijja tayi "abbu mutane dama ai ba a iya musu sai dai kawai mutum ya toshe kunnuwansa domin duk yanda yake sai sun yi korafi akanshi"
Hira suka ci gaba dayi har wurin daya saura sai da bacci ya dauketa sannan jabir ya ajiye babyn ya tafi gida, haka yan uwa da abokan arziki suketa zarya zuwa asibitin ganin baby, wasu ma bahijja ba saninsu tayi ba,wasu daliban jabir ne wasu kuma ma'aikatanshi, kai bahijja taga jama'a daga karshe ma dr din hanawa yayi arinka shiga dakin da take domin har yau jininta bai sauka ba shiyasa yace akyaleta ta huta.
Ana saura kwana biyu suna aka sallamesu zuwa gida, anan wata sabuwar hidimar ta tashi, tunda suka koma gida kuma jama'a suke kai kawo, tana daki zaune da babyn a hannunta tanata kukan huda kunnen da aka yi mata domin da a asibitin ba ayi mata ba, ita kanta bahijja ji take kamar itama tayi kukan saboda tausayin yarinyar,
Jabir ne ya shiga dakin ganin baby na kuka ya karbeta yana cewa "meya samu babyn abbu take kuka?"
"Kunne aka huda mata"
"Ina fata ba huda biyu aka yi mata ba?" Yafada yana duban kunnen jaririyar,
"Kai abbu idan biyune menene?"
"Ban so ne abarta idan ta girma in tanada ra'ayi sai tayi da kanta"
Lebenshi ya sawa babyn abaki ya fara jijjigata yana rarrashinta har tayi shiru, shidai tunda babyn nan tazo duniya yake kallonta domin komai nata irin nashine, yanzun ma anyi mata ado cikin blue din kaya riga da wando harda safa da hula tana nade cikin farin towel,
"Zo muje malam ne ya zo ganinku"
Hijab bahijja ta dauka suka fita zuwa sashen jabir inda malam yake, daukar yarinyar yayi yaita yi mata addu'a yana sakawa bahijja albarka.
Ana saura daya suna mai lalle tazo tayiwa bahijja hadadden kunshi baki da ja sannan aka yi mata kitso kananu three step mai 7,7,shi kam jabir lokacin yana can yana yi musu shirye shiryen walimar da za agudanar ranar sunan, al'amin kam koda wanne lokaci yana nanuke da yar jaririyar kamar zai hadiyeta.
Sai dare sannan jabir ya samu ya shigo gidan, part dinshi yaje ya kira ummu ta hada mishi ruwan wanka ta gabatar mishi da abinci yaci sannan ya kira bahijja,
Yana bakin gadonshi azaune lokacin ummu ta tafi bahijja ta shigo tana sanye da blue din t shirt da bakin skirt na jeans, hannunta dauke da jaririyar,
Kallonta jabir ya tsaya yi ganin yadda tayi kyau, gashi tasha kunshi da kitso, babyn ya karba yana shafar hannun bahijja,
"Kunshin nan yayi kyau binti"
"Nagode abbu" tafada cikin fara'a,
Jikinshi ya jata yahada ta da nashi yaci gaba da shafar kitson kanta da kunshin dake hannunta,
"Binti har yau baki tambayi sunan babynki ba"
"To ai abbu kai nake jira ka fada min"
Murmushi yayi yakama jelar kitsonta guda daya, "sunanta _Bahijja_ mai sunanki kika haifa"
Ya rada mata acikin kunnenta, dago da kanta tayi ta kalleshi "dagaske abbu?"
Sai da yayi kissing din hannunta sannan yabata amsa "dagaske binti, yanzu me zaki kirata dashi?"
"Abbu ni dama imtisal zan nace mata"
"Imtisal? Binti kin san ma'anar imtisal din?"
Girgiza kai tayi alamun a'a,
"To imtisal yana nufin kwatance kwatance ko misalce misalce, kina son arinka kwatanta abubuwa akan yarki?"
Nanma kai ta girgiza "indai hakane to ki hakura da kiranta da wannan sunan, nidama a niyyata mu kirata da *_TASLEEM_* sunan tasleem sunane mai kyau domin yana nufin wanda ya mika wuya, kinga idan kin sake haihuwa idan namiji ne sai mu kirashi da aslam ko?"
Murmushi tayi batare da tayi magana ba,yan yatsunta ya kama yafara ja yana murzasu ahankali,
"Binti kisani yanzu wani nauyi yahau kanki, wannan yarinyar da kika haifa wata amana ce Allah ya baki dan haka ki kula mutuka wurin ganin rayuwarta ta inganta, yanzu lokaci yayi wanda zaki san irin abubuwan da zaki runka yi agaban yarki domin idan ta tashi dake zata yi koyi, duk wata dabi'a taki to ita yarki zata dauka dan haka sai kinyi takatsan tsan sosai wurin sanin irin maganganun da zaki rinka furtawa idan ranki ya baci da kuma idan kina cikin halin farin ciki, sannan ki yawaita yi mata addu'a kan Allah ya shiryar da ita yasa mata imani acikin zuciyarta domin hakkin iyaye ne yiwa yayansu addu'a, yanzu gobe za ayi mata aski da safe"
Baki bahijja ta zumbura "nidai ba za ayi mata aski ba abbu"
Kanta ya shafa yana murmushi "binti yin hakan sauke wani hakkine da ya rataya awuyanmu, annabi yace hakkin yaya akan iyayensu sun hadar da yi musu addu'a tun suna ciki, idan aka haifesu kuma to hakki nafarko shine yi musu kiran salla a kunnensu sannan ayi musu huduba da suna mai kyau domin suna yana da tasiri sosai akan mutum amma ku matan yanzu kowanne suna kiran yaranku kuke dashi indai yayi muku dadi,
to tsaya kiji wani mutum yazo ya samu manzon Allah duk kayan mutumin a yayyage da alamun wahala da tsanani atare dashi, sai annabi ya tambayeshi sunanshi sai ya fada sai annabi yace dole ne kasha wahala arayuwa domin fassarar sunanka tana nufin matalauci, marar arzuki mai shan wahala, dan haka yanzu zaka canja suna ka koma wani domin suna yana da mutukar tasiri ga mutum, to kinga indai hakane to dole ku rinka sanin ma'anar suna kafin ku sakawa yaro, sai abu nagaba shine bawa yaro zam zam da dabino ko zuma lokacin da aka haifeshi wannan ma sunna ce,
sannan ranar suna ana son ayiwa jariri ko jaririya aski idan angama za abayar da sadaka kwatankwacin nauyin gashin da aka aske, hakika yin aski itama wata sunnarce amma mata dayawa bakwa son ayi wa yaranku wannan askin indai matane to wannan gashin datti ne, daudar mahaifa ce asketa shine mafi a'ala,
sai hakki nagaba shine yankawa jariri rago idan namiji ne rago biyu idan kuma macece rago daya wannan shine yazo abisa koyarwar manzon Allah amma babu laifi ga wadanda suke da wadata su yanka fiyeda haka, abu nagaba acikin hakkin yara akan iyayensu shine basu tarbiya da kula da tarbiyarsu tun suna cikin tsumma har kawo lokacin da zasu girma su mallaki hankalin kansu, ya kamata iyaye su rinka koyar da yaransu saukakan kalmomi tun suna kanana irinsu alhamdulillah, bisimillahir rahamanur rahim, masha Allah, astagfurullah,
sannan ki sani duk abinda kike yi to yaronki yana lura dake kuma dake zaiyi koyi a dukkan al'amuransa idan ya tashi zai tashine da dabi'unki yanda kike reacting idan ranki ya baci, yanda kike reacting idan abin farin ciki ya sameki da dukkan abubuwan da kikeyi agaban idonshi shiyasa idan ranki ya baci to anfi son kiyi addu'a idan abin farin cikine ya samu nanma kiyi addu'a sai yaronki yataso cikin tarbiya mai kyau.
Sannan alokacin da yaro ya fara tasowa to yana dakyau iyaye su jashi ajiki su bashi kulawa su sakar masa fuska su rinka zama tare dashi suna tattaunawa suna sanar dashi hakkin Allah akanshi da kuma tsoratar dashi da azabar Allah to irin hakane zakiga ko yaro yataso to zai tasone da shakuwa mai karfi tsakaninsa da iyayensa sannan baya iya sanar da kowa damuwarsa sai iyayensa amma indai bamu ja yayanmu ajiki ba to maimakon su sanar damu sai dai suje su sanar da wasu awaje ko su sanar da kawayensu saboda mu suna jin kunyar fada mana bayan kuma iyaye su suka fi cancanta da zama aminan yayansu na kut da kut domin babu mai rufawa da asirinsa sama da iyaye, ke kanki shaidace akaina nida al'amin nadaukeshi tamkar wani abokina shiyasa ya taso bashida wasu abokai sai ni tun yana yaro nakan zaunar dashi nayi wasa dashi muci abinci tare muje salla tare shiyasa ya taso da dukkanin irin halayena da dabi'una sannan baya iya boyemin damuwarsa ko sirrinsa, ko mafarki al'amin yayi sai ya fada min har takai akwai lokacin da nasanar dashi cewa zaiyi mafarki, mafarkin balaga nafada masa cewar duk lokacin da yayi wannan mafarkin to ya girma ya zama cikakken namiji wanda zai iya yiwa mace abinda zata haihu kuma yanzu anbude masa littafin rubuta ayyukansa na alkairi da sharri nayi masa nasihohi masu ratsa jiki, to haka ake son iyaye su zama domin su kansu yayan suna samun sassaukar rayuwa"
Kallonsu bahijja tayi shida babyn "amma kuma komai nata irin na abbunta ne"
Kallon bakinshi tayi ta kalli bakin yarinyar "lahh abbu harfa bakinku iri daya ne"
Kafin ya bata amsa su mamanta da anty Bilkisu sun shigo harda papa, nan jabir ya basu jaririyar ya fita,a reception ya haduda mahaifinshi da sauran matan gidansu suma suna kokarin shigowa, bai bisu dakinba yawuce,
Wurin 12:30 yadawo asibitin lokacin babu kowa sai anty bilkisu jaririyar ya dauka yayi kan gadon da bahijja ke kwance da ita, kallonshi kawai bahijja take saboda yayi wanka yayi fes cikin farar shadda babu hula akanshi.
Wani irin kyau taga yayi mata sosai domin yafito kamar dan saurayi das dashi,
Agefenta ya zauna yana gyarawa babyn zama ajikinshi,
"Al'amin yayi nacin sai ya biyoni amma ban taho dashi ba saboda dare yayi, sai gobe zai zo yaga kanwarshi"
"Abbu dama ka taho min dashi"
Kallonta yayi yakai hannunshi kan kafafuwanta yafara dannawa ahankali, "binti har yanzu fa akunbure kike"
"Bp dina ne bai sauka ba abbu sai nan da wani lokaci"
"To Allah ya baki lafiya ya raya baby ya kawo kannenta kwana kusa"
Juya baya tayi tana cewa "hum um, ni yanzu sai na dade ban sake haihuwa ba abbu, nasha wahala dayawa"
Murmushi jabir yayi yana kallonta yadda ta juya baya "nima zan so ki huta din amma kuma hakan ba mai yiyuwa bane, kinga ummun al'amin har yau itama bata sake haihuwa ba mutane har cewa suke yi wai nine bana son haihuwa"
Juyowa bahijja tayi "abbu mutane dama ai ba a iya musu sai dai kawai mutum ya toshe kunnuwansa domin duk yanda yake sai sun yi korafi akanshi"
Hira suka ci gaba dayi har wurin daya saura sai da bacci ya dauketa sannan jabir ya ajiye babyn ya tafi gida, haka yan uwa da abokan arziki suketa zarya zuwa asibitin ganin baby, wasu ma bahijja ba saninsu tayi ba,wasu daliban jabir ne wasu kuma ma'aikatanshi, kai bahijja taga jama'a daga karshe ma dr din hanawa yayi arinka shiga dakin da take domin har yau jininta bai sauka ba shiyasa yace akyaleta ta huta.
Ana saura kwana biyu suna aka sallamesu zuwa gida, anan wata sabuwar hidimar ta tashi, tunda suka koma gida kuma jama'a suke kai kawo, tana daki zaune da babyn a hannunta tanata kukan huda kunnen da aka yi mata domin da a asibitin ba ayi mata ba, ita kanta bahijja ji take kamar itama tayi kukan saboda tausayin yarinyar,
Jabir ne ya shiga dakin ganin baby na kuka ya karbeta yana cewa "meya samu babyn abbu take kuka?"
"Kunne aka huda mata"
"Ina fata ba huda biyu aka yi mata ba?" Yafada yana duban kunnen jaririyar,
"Kai abbu idan biyune menene?"
"Ban so ne abarta idan ta girma in tanada ra'ayi sai tayi da kanta"
Lebenshi ya sawa babyn abaki ya fara jijjigata yana rarrashinta har tayi shiru, shidai tunda babyn nan tazo duniya yake kallonta domin komai nata irin nashine, yanzun ma anyi mata ado cikin blue din kaya riga da wando harda safa da hula tana nade cikin farin towel,
"Zo muje malam ne ya zo ganinku"
Hijab bahijja ta dauka suka fita zuwa sashen jabir inda malam yake, daukar yarinyar yayi yaita yi mata addu'a yana sakawa bahijja albarka.
Ana saura daya suna mai lalle tazo tayiwa bahijja hadadden kunshi baki da ja sannan aka yi mata kitso kananu three step mai 7,7,shi kam jabir lokacin yana can yana yi musu shirye shiryen walimar da za agudanar ranar sunan, al'amin kam koda wanne lokaci yana nanuke da yar jaririyar kamar zai hadiyeta.
Sai dare sannan jabir ya samu ya shigo gidan, part dinshi yaje ya kira ummu ta hada mishi ruwan wanka ta gabatar mishi da abinci yaci sannan ya kira bahijja,
Yana bakin gadonshi azaune lokacin ummu ta tafi bahijja ta shigo tana sanye da blue din t shirt da bakin skirt na jeans, hannunta dauke da jaririyar,
Kallonta jabir ya tsaya yi ganin yadda tayi kyau, gashi tasha kunshi da kitso, babyn ya karba yana shafar hannun bahijja,
"Kunshin nan yayi kyau binti"
"Nagode abbu" tafada cikin fara'a,
Jikinshi ya jata yahada ta da nashi yaci gaba da shafar kitson kanta da kunshin dake hannunta,
"Binti har yau baki tambayi sunan babynki ba"
"To ai abbu kai nake jira ka fada min"
Murmushi yayi yakama jelar kitsonta guda daya, "sunanta _Bahijja_ mai sunanki kika haifa"
Ya rada mata acikin kunnenta, dago da kanta tayi ta kalleshi "dagaske abbu?"
Sai da yayi kissing din hannunta sannan yabata amsa "dagaske binti, yanzu me zaki kirata dashi?"
"Abbu ni dama imtisal zan nace mata"
"Imtisal? Binti kin san ma'anar imtisal din?"
Girgiza kai tayi alamun a'a,
"To imtisal yana nufin kwatance kwatance ko misalce misalce, kina son arinka kwatanta abubuwa akan yarki?"
Nanma kai ta girgiza "indai hakane to ki hakura da kiranta da wannan sunan, nidama a niyyata mu kirata da *_TASLEEM_* sunan tasleem sunane mai kyau domin yana nufin wanda ya mika wuya, kinga idan kin sake haihuwa idan namiji ne sai mu kirashi da aslam ko?"
Murmushi tayi batare da tayi magana ba,yan yatsunta ya kama yafara ja yana murzasu ahankali,
"Binti kisani yanzu wani nauyi yahau kanki, wannan yarinyar da kika haifa wata amana ce Allah ya baki dan haka ki kula mutuka wurin ganin rayuwarta ta inganta, yanzu lokaci yayi wanda zaki san irin abubuwan da zaki runka yi agaban yarki domin idan ta tashi dake zata yi koyi, duk wata dabi'a taki to ita yarki zata dauka dan haka sai kinyi takatsan tsan sosai wurin sanin irin maganganun da zaki rinka furtawa idan ranki ya baci da kuma idan kina cikin halin farin ciki, sannan ki yawaita yi mata addu'a kan Allah ya shiryar da ita yasa mata imani acikin zuciyarta domin hakkin iyaye ne yiwa yayansu addu'a, yanzu gobe za ayi mata aski da safe"
Baki bahijja ta zumbura "nidai ba za ayi mata aski ba abbu"
Kanta ya shafa yana murmushi "binti yin hakan sauke wani hakkine da ya rataya awuyanmu, annabi yace hakkin yaya akan iyayensu sun hadar da yi musu addu'a tun suna ciki, idan aka haifesu kuma to hakki nafarko shine yi musu kiran salla a kunnensu sannan ayi musu huduba da suna mai kyau domin suna yana da tasiri sosai akan mutum amma ku matan yanzu kowanne suna kiran yaranku kuke dashi indai yayi muku dadi,
to tsaya kiji wani mutum yazo ya samu manzon Allah duk kayan mutumin a yayyage da alamun wahala da tsanani atare dashi, sai annabi ya tambayeshi sunanshi sai ya fada sai annabi yace dole ne kasha wahala arayuwa domin fassarar sunanka tana nufin matalauci, marar arzuki mai shan wahala, dan haka yanzu zaka canja suna ka koma wani domin suna yana da mutukar tasiri ga mutum, to kinga indai hakane to dole ku rinka sanin ma'anar suna kafin ku sakawa yaro, sai abu nagaba shine bawa yaro zam zam da dabino ko zuma lokacin da aka haifeshi wannan ma sunna ce,
sannan ranar suna ana son ayiwa jariri ko jaririya aski idan angama za abayar da sadaka kwatankwacin nauyin gashin da aka aske, hakika yin aski itama wata sunnarce amma mata dayawa bakwa son ayi wa yaranku wannan askin indai matane to wannan gashin datti ne, daudar mahaifa ce asketa shine mafi a'ala,
sai hakki nagaba shine yankawa jariri rago idan namiji ne rago biyu idan kuma macece rago daya wannan shine yazo abisa koyarwar manzon Allah amma babu laifi ga wadanda suke da wadata su yanka fiyeda haka, abu nagaba acikin hakkin yara akan iyayensu shine basu tarbiya da kula da tarbiyarsu tun suna cikin tsumma har kawo lokacin da zasu girma su mallaki hankalin kansu, ya kamata iyaye su rinka koyar da yaransu saukakan kalmomi tun suna kanana irinsu alhamdulillah, bisimillahir rahamanur rahim, masha Allah, astagfurullah,
sannan ki sani duk abinda kike yi to yaronki yana lura dake kuma dake zaiyi koyi a dukkan al'amuransa idan ya tashi zai tashine da dabi'unki yanda kike reacting idan ranki ya baci, yanda kike reacting idan abin farin ciki ya sameki da dukkan abubuwan da kikeyi agaban idonshi shiyasa idan ranki ya baci to anfi son kiyi addu'a idan abin farin cikine ya samu nanma kiyi addu'a sai yaronki yataso cikin tarbiya mai kyau.
Sannan alokacin da yaro ya fara tasowa to yana dakyau iyaye su jashi ajiki su bashi kulawa su sakar masa fuska su rinka zama tare dashi suna tattaunawa suna sanar dashi hakkin Allah akanshi da kuma tsoratar dashi da azabar Allah to irin hakane zakiga ko yaro yataso to zai tasone da shakuwa mai karfi tsakaninsa da iyayensa sannan baya iya sanar da kowa damuwarsa sai iyayensa amma indai bamu ja yayanmu ajiki ba to maimakon su sanar damu sai dai suje su sanar da wasu awaje ko su sanar da kawayensu saboda mu suna jin kunyar fada mana bayan kuma iyaye su suka fi cancanta da zama aminan yayansu na kut da kut domin babu mai rufawa da asirinsa sama da iyaye, ke kanki shaidace akaina nida al'amin nadaukeshi tamkar wani abokina shiyasa ya taso bashida wasu abokai sai ni tun yana yaro nakan zaunar dashi nayi wasa dashi muci abinci tare muje salla tare shiyasa ya taso da dukkanin irin halayena da dabi'una sannan baya iya boyemin damuwarsa ko sirrinsa, ko mafarki al'amin yayi sai ya fada min har takai akwai lokacin da nasanar dashi cewa zaiyi mafarki, mafarkin balaga nafada masa cewar duk lokacin da yayi wannan mafarkin to ya girma ya zama cikakken namiji wanda zai iya yiwa mace abinda zata haihu kuma yanzu anbude masa littafin rubuta ayyukansa na alkairi da sharri nayi masa nasihohi masu ratsa jiki, to haka ake son iyaye su zama domin su kansu yayan suna samun sassaukar rayuwa"