Sashe 60
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwantar da kanta tayi akafadarshi tana goge hawayen fuskarta,
"Kar wannan ya dameki kinji bintina, kema yanzu bakida banbanci dasu wadanda aka haifa acikin addinin, banbancinku kawai wanda yafi tsoron Allah to shine yafi daraja awurin Allah, ko bakida labarin wani mutum wanda za atafi yaki yazo wurin manzon Allah yace ya musulunta, annabi yabashi kalmar shahada yace idan andawo daga yaki zaiyi sauran abubuwan da suka wajaba akansa, lokacin da akaje yakin sai mutumin ya rasu acan da aka dawo sai annabi yake tambayar yana ina akace ai ya rasu sai annabi yace yana aljanna, kinji wani ikon Allah ya shiga aljanna batare da yayiwa Allah salla ba, baiyi azumi ba, baiyi zakka ba, amma mu yanzu nawane daga cikinmu zasu shiga wuta bayan suna salla suna azumi? Kar wannan yadameki kinji bintina, zo muje kiga dinkunanki da na karbo miki saboda zakifi sakewa acikinsu duk bubu nasa aka yi miki"
Murmushi tayi tabi bayanshi yana rike da hannunta har zuwa dayan bedroom dinta.
Ranar da su ummu al'amin zasu dawo bahijja tasha aiki domin tun 9 ta shiga kitchen tafara yi musu kayan saukarsu girki kala kala tayi musu da lemuka masu dadi da kamshi,
Kasancewar saukar rana sukayi ana kiran sallar azahar suka shigo gidan, murna wurin bahijja ba a magana lokacin da sukayi ido biyu da al'amin, ganinshi tayi yasake girma ya zama saurayi,ummu al'amin kuwa ido ta zubawa bahijja aranta tana tunanin cewa ashe badan sun zo ba da sai dai suji haihuwa,
Al'amin ne ya tayata ta gabatar musu da girke girken data tanadar musu, basu fi minti biyar da zuwaba jabir ya taho daga office nan gida ya kancame da murna, ummu tana nanike da jabir duk inda yayi ita kam dama bahijja aranta ta kudiri niyyar basu kwana 7 kyauta dan haka sashenta ta koma bayan sun gama gaggaisawa, bata sake ganin jabir ba sai da yamma nan dinma tareda ummu suka shigo da al'amin lokacin tana kwance afalo sannu suka yimata suka fice suka barta ita da al'amin suna hirarsu.
Daren ranar bata samu bacci ba domin dama jabir ne yake yi mata dabara yake kwantar da ita ajikinshi ta yanda ba zasu takura ba ita da babyn, yadda taga rana haka taga dare, asuba tanayi tayi salla ta shiga kitchen ta shirya musu abin karyawa, harda su dambun kifi da albasa da attaruhu ga wani irin hadadden hadi da tayiwa dankalin hausa ta sarrafashi _(masu karatu babu space da nakawo muku yadda ta sarrafa wannan dankalin)_, dakinta ta koma tayi wanka tashirya cikin doguwar riga yar kanti ta koma falo ta zauna.
Sai misalin karfe 9 da yan mintuna jabir ya shigo sashen nata tana zaune tasaka katon cikinta agaba tana cin taliya da manja mai da yaji,
Tausayinta yaji ya kamashi ganin yanda kafufunta suka dan kunbura gashi daga ganin idonta yasan bata samu bacci ba daren jiya yau kuma ta tashi sassafe tayi musu hidima,agabanta ya zauna yana kallonta ita kuma ta dauke kanta,
"Morning binti, me kike ci ne?"
"Morning" tafada atakaice cikin kishi,
Murmushi yayi "sorry my binti, meyasa bakiyi bacci ya isheki ba? Kalli yanda kafafunki suka kunbura"
Bata bashi amsaba taci gaba da cin taliyarta har tagama, mikewa yayi ya shiga kitchen ya dauko ruwa da sabulu yazo ya wanke mata hannunta ya mayar ya dawo ya dauketa ya nufi dakinta da ita, kwantar da ita yayi ya soma daddanna mata kafafuwanta yana cewa,
"Kar ki sake wahalar da kanki wurin yimana girki, kawai ki yi wanda zakici tunda kin gama yin nauyi yanzu, sannan ki dage da addu'a ki rinka rokon Allah yasa ki haihu lafiya kuma tun yanzu kifara yiwa abinda zaki haifa addu'a domin wannan yana daya daga cikin hakkokin'yaya akan iyaye wato yi musu addu'a tun suna cikin ciki, kuma ki yawaita fadin ya hayyu ya k'ayyum birahmatka astangis akoda yaushe ako wanne lokaci domin samun rahma daga wurin Allah, sannan kowacce safiya kafin kici komai kifara diban ruwa a cup dan kadan idan kuma kinada zamzam to kiyi amfani dashi ki karanta ya hayyu ya k'ayyum birahmatika astangis sau bakwai sai kiyi bisimilla kisha, sai abu nagaba shine yawaita sadaka wannan sune abubuwan da duk wata mai ciki ya kamata ta rik'e musamman ma lokacin da cikin ya girma"
Tana kwance tana jinshi amma bata iya bashi amsa ba saboda baccin da ya hau kanta, babu jimawa bacci ya dauketa, gyara mata kwanciyar yayi ya fita yabarta.
Daren ranar kuwa tana zaune atsakiyar gado tanata addu'a sai ga jabir ya shigo agogo ta kalla karfe 2 nadare, zama yayi agefenta ya kamo hannunta,
"Abbu me kazo yi? Idan ummun al'amin ta tashi taga ka taho nan ai sai ta zargi wani abu"
Bakinta ya rufe mata da hannunsa "binti ko annabi ai yana ziyartar iyalanshi ba aranar girkinsu ba, nasan dama bakiyi bacci ba why?"
Ido ta mutsuttsuka "abinci zanci"
Tashi yayi yaje ya hado mata Golden morn da madara cikin cup ya kawo mata,akusa da ita ya zauna yasoma bata abaki tana sha,
"Abbu gaskiya wannan babyn naka da mugun cin abinci yake motsi kadan sai inji yunwa"
Murmushi yayi yakai spoon din bakinta "to ai binti dama yanzu komai naki ya karu jinki ankara miki, ganinki ma ankara shi sannan uwa uba shakar numfashinki ma duk ya karu saboda bake kadai bace, duk abinda zakiyi yanzu na mutane biyu zaki"
Fuska ta shagwabe "to abbu kace ya rage cin abinci gaskiya"
"To kai baby ka rage cin abinci da yawa" yafada bayan ya kara kunnenshi ajikin cikin nata, sai da yagama bata abincin tayi dam ya lallabata ta kwanta sannan ya tafi ya barta.
Washe gari da yamma bayan ya dawo daga office yayi wanka ya nufi part dinta lokacin da ya shiga tana kwance afalo daga ita sai daurin kirji tana shan iska ga al'amin yana tsaye tasakashi yana taka mata tafin kafarta, tafin hannunta da kafarshi,wani irin tausayinta ne ya ziyarci jabir,
"Al'amin jeka wurin ummunka" yace da al'amin yana mika masa hannu domin yin musabaha,shima al'amin din hannu ya mika masa suka gaisa yana cewa "assalamu alaikum abbu"
Fita al'amin yayi shikuma jabir ya fara dan taka mata kafar tata ahankali da kafarshi,
"Abbu yunwa, bani abincina a kitchen" tafada tana kokarin tashi,
Kitchen yaje ya zubo mata jalop din macaroni da kifi wanda ta girka ya kawo mata sai kuma ya tarar da ita tana kuka hawaye sai bin kumatunta yake,
"Binti lafiya"
"Abbu wallahi kacewa babynka ya daina naushina, kullum sai yayita naushina, Allah nima zan rama idan bai daina ba" tafada tana kuka,
Abin dariya yaso yabawa jabir amma sai ya guntse dariyarshi "yi hakuri kar ki rama yunwa yake jine shiyasa yake naushinki"
"Babu wani yunwa kofa kwanciya nayi ta gefen nan sai ya fara naushina idan nasaka rigar da ta dan kamani nanma sai ya yita naushina, Allah ka yi masa magana"
Abincin ya ajiye yamatsa kusa da cikin nata yana murmushi "babyn abbu stop biting your mom kaji, kabarta da dawainiyar da take yi da abbunka ma ya isheta"
Dago kanshi yayi, "basai kin ramaba nayi masa magana zai daina, amma takura shi kikeyi binti shiyasa, kidaina saka kayan da suka matseki wannan bubu din da nakawo miki tun jimawa su zaki rinka sakawa"
Baki ta zumburo ta dauki spoon tafara diban abincin tana ci, karba yayi yaci gaba da bata.
Tana koshi ya dauketa zuwa dakinta ya ajiyeta akan gado "binti kin kara nauyi da yawa, ki shirya gobe awurinki zan kwana"
Zabura tayi ta tashi tana zare ido "abbu nayafe, kayi zamanka awurin ummu har sai bayan na haihu, nidai kawai kubani aron al'amin mu rinka kwana tare"
"A'a binti idan ke kin yafe to ni ban yafe ba"
"Nidai abbu a'a" tafada tana tuttura baki,
"Saboda yanzu kin gaji dani ko?"
"Nidai abbu ka kawo min al'amin"
"Allah babu al'amin din da za akawo miki kinji nace Allah nidin dai da bakya so nine abokin kwananki agobe"
Komawa tayi ta kwanta tana tuttura masa baki sai kunkuni take "shi abbun nan wallahi wayone dashi kullum kullum sai yayita yimin wayo" yana jiyota tana kunkunin amma baya iya jin abinda take fada, cigaba da mammatsa mata jikinta yayi yana cewa
"Idan Allah ya saukeki lafiya zan sanar dake wasu hakkoki wadanda suka rataya akanki binti na".
_Masu karatu kusake hakuri mu hadu a page nagaba inda zamuji karshen labarin da yardar Allah, gaisuwa mai tarin yawa gareku dinbin masoyana masu karanta wannan labarin hakika ina alfahari daku._
*_Ummi A'isha_*👌🏻
[11/1, 8:18 AM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE..!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_131-135_
~~~Bata ce dashi komai ba saboda ita yanzu ta kanta take yi domin alla alla take ta rabuda wannan cikin dake jikinta lafiya,
"Binti bakice komai ba ko natafi?" Ya tambayeta bayan ya zauna akusa da kafafunta yana jan yan yatsunta,
"Kafin katafi abbu ka hada min ruwa zanyi wanka" tace dashi tanata faman tutturo masa baki saboda abinda taji yafada dazu,
"Binti menene na fushin ne? Shi al'amin din idan nakawoshi me zai iya yimiki? Nikuwa kinga ko babu komai da daddare zan tashi na hada miki abincinki kici"
"Abbu nikam ka hada min ruwan wanka Allah zafi nake ji"
Mikewa jabir yayi ya shiga toilet dinta ya tara mata ruwan wanka a katon baho ya dawo ya taimaka mata zuwa cikin bathroom din, wankan ya tayata ya rakata dakinta ta zauna abakin gado,cikeda tausayawa jabir yake kallonta domin cikin nata ba karamin girma yayi ba sai kace wacce zata haifi 'yan biyu alhalin kuma a asibiti ance yaro dayane,
Mai ya mika mata ya nufi wurin kayan sawarta ya ciro mata wata koriyar atamfa mai hoton cokali ajiki wadda tasha dinkin bubu,
Ba wata kwalliya mai yawa tayi ba powder kawai ta shafa tasaka kwalli domin kwalli yana da mutukar amfani agun'ya mace yana daya daga cikin abubuwan da yake dawowa da mace martabarta a matsayinta na ya mace shiyasa ko ba zatayi wata kwalliya da yawaba to takan saka kwalli,
Turarruka kala kala ta fesa ta saka doguwar bubu din da jabir ya dauko mata, juyowa yayi yana kallonta bayan ya ajiye mata kayan kwalliyarta agaban mirror dinta,
"Kinyi kyau sosai bintina"
"Kar wannan ya dameki kinji bintina, kema yanzu bakida banbanci dasu wadanda aka haifa acikin addinin, banbancinku kawai wanda yafi tsoron Allah to shine yafi daraja awurin Allah, ko bakida labarin wani mutum wanda za atafi yaki yazo wurin manzon Allah yace ya musulunta, annabi yabashi kalmar shahada yace idan andawo daga yaki zaiyi sauran abubuwan da suka wajaba akansa, lokacin da akaje yakin sai mutumin ya rasu acan da aka dawo sai annabi yake tambayar yana ina akace ai ya rasu sai annabi yace yana aljanna, kinji wani ikon Allah ya shiga aljanna batare da yayiwa Allah salla ba, baiyi azumi ba, baiyi zakka ba, amma mu yanzu nawane daga cikinmu zasu shiga wuta bayan suna salla suna azumi? Kar wannan yadameki kinji bintina, zo muje kiga dinkunanki da na karbo miki saboda zakifi sakewa acikinsu duk bubu nasa aka yi miki"
Murmushi tayi tabi bayanshi yana rike da hannunta har zuwa dayan bedroom dinta.
Ranar da su ummu al'amin zasu dawo bahijja tasha aiki domin tun 9 ta shiga kitchen tafara yi musu kayan saukarsu girki kala kala tayi musu da lemuka masu dadi da kamshi,
Kasancewar saukar rana sukayi ana kiran sallar azahar suka shigo gidan, murna wurin bahijja ba a magana lokacin da sukayi ido biyu da al'amin, ganinshi tayi yasake girma ya zama saurayi,ummu al'amin kuwa ido ta zubawa bahijja aranta tana tunanin cewa ashe badan sun zo ba da sai dai suji haihuwa,
Al'amin ne ya tayata ta gabatar musu da girke girken data tanadar musu, basu fi minti biyar da zuwaba jabir ya taho daga office nan gida ya kancame da murna, ummu tana nanike da jabir duk inda yayi ita kam dama bahijja aranta ta kudiri niyyar basu kwana 7 kyauta dan haka sashenta ta koma bayan sun gama gaggaisawa, bata sake ganin jabir ba sai da yamma nan dinma tareda ummu suka shigo da al'amin lokacin tana kwance afalo sannu suka yimata suka fice suka barta ita da al'amin suna hirarsu.
Daren ranar bata samu bacci ba domin dama jabir ne yake yi mata dabara yake kwantar da ita ajikinshi ta yanda ba zasu takura ba ita da babyn, yadda taga rana haka taga dare, asuba tanayi tayi salla ta shiga kitchen ta shirya musu abin karyawa, harda su dambun kifi da albasa da attaruhu ga wani irin hadadden hadi da tayiwa dankalin hausa ta sarrafashi _(masu karatu babu space da nakawo muku yadda ta sarrafa wannan dankalin)_, dakinta ta koma tayi wanka tashirya cikin doguwar riga yar kanti ta koma falo ta zauna.
Sai misalin karfe 9 da yan mintuna jabir ya shigo sashen nata tana zaune tasaka katon cikinta agaba tana cin taliya da manja mai da yaji,
Tausayinta yaji ya kamashi ganin yanda kafufunta suka dan kunbura gashi daga ganin idonta yasan bata samu bacci ba daren jiya yau kuma ta tashi sassafe tayi musu hidima,agabanta ya zauna yana kallonta ita kuma ta dauke kanta,
"Morning binti, me kike ci ne?"
"Morning" tafada atakaice cikin kishi,
Murmushi yayi "sorry my binti, meyasa bakiyi bacci ya isheki ba? Kalli yanda kafafunki suka kunbura"
Bata bashi amsaba taci gaba da cin taliyarta har tagama, mikewa yayi ya shiga kitchen ya dauko ruwa da sabulu yazo ya wanke mata hannunta ya mayar ya dawo ya dauketa ya nufi dakinta da ita, kwantar da ita yayi ya soma daddanna mata kafafuwanta yana cewa,
"Kar ki sake wahalar da kanki wurin yimana girki, kawai ki yi wanda zakici tunda kin gama yin nauyi yanzu, sannan ki dage da addu'a ki rinka rokon Allah yasa ki haihu lafiya kuma tun yanzu kifara yiwa abinda zaki haifa addu'a domin wannan yana daya daga cikin hakkokin'yaya akan iyaye wato yi musu addu'a tun suna cikin ciki, kuma ki yawaita fadin ya hayyu ya k'ayyum birahmatka astangis akoda yaushe ako wanne lokaci domin samun rahma daga wurin Allah, sannan kowacce safiya kafin kici komai kifara diban ruwa a cup dan kadan idan kuma kinada zamzam to kiyi amfani dashi ki karanta ya hayyu ya k'ayyum birahmatika astangis sau bakwai sai kiyi bisimilla kisha, sai abu nagaba shine yawaita sadaka wannan sune abubuwan da duk wata mai ciki ya kamata ta rik'e musamman ma lokacin da cikin ya girma"
Tana kwance tana jinshi amma bata iya bashi amsa ba saboda baccin da ya hau kanta, babu jimawa bacci ya dauketa, gyara mata kwanciyar yayi ya fita yabarta.
Daren ranar kuwa tana zaune atsakiyar gado tanata addu'a sai ga jabir ya shigo agogo ta kalla karfe 2 nadare, zama yayi agefenta ya kamo hannunta,
"Abbu me kazo yi? Idan ummun al'amin ta tashi taga ka taho nan ai sai ta zargi wani abu"
Bakinta ya rufe mata da hannunsa "binti ko annabi ai yana ziyartar iyalanshi ba aranar girkinsu ba, nasan dama bakiyi bacci ba why?"
Ido ta mutsuttsuka "abinci zanci"
Tashi yayi yaje ya hado mata Golden morn da madara cikin cup ya kawo mata,akusa da ita ya zauna yasoma bata abaki tana sha,
"Abbu gaskiya wannan babyn naka da mugun cin abinci yake motsi kadan sai inji yunwa"
Murmushi yayi yakai spoon din bakinta "to ai binti dama yanzu komai naki ya karu jinki ankara miki, ganinki ma ankara shi sannan uwa uba shakar numfashinki ma duk ya karu saboda bake kadai bace, duk abinda zakiyi yanzu na mutane biyu zaki"
Fuska ta shagwabe "to abbu kace ya rage cin abinci gaskiya"
"To kai baby ka rage cin abinci da yawa" yafada bayan ya kara kunnenshi ajikin cikin nata, sai da yagama bata abincin tayi dam ya lallabata ta kwanta sannan ya tafi ya barta.
Washe gari da yamma bayan ya dawo daga office yayi wanka ya nufi part dinta lokacin da ya shiga tana kwance afalo daga ita sai daurin kirji tana shan iska ga al'amin yana tsaye tasakashi yana taka mata tafin kafarta, tafin hannunta da kafarshi,wani irin tausayinta ne ya ziyarci jabir,
"Al'amin jeka wurin ummunka" yace da al'amin yana mika masa hannu domin yin musabaha,shima al'amin din hannu ya mika masa suka gaisa yana cewa "assalamu alaikum abbu"
Fita al'amin yayi shikuma jabir ya fara dan taka mata kafar tata ahankali da kafarshi,
"Abbu yunwa, bani abincina a kitchen" tafada tana kokarin tashi,
Kitchen yaje ya zubo mata jalop din macaroni da kifi wanda ta girka ya kawo mata sai kuma ya tarar da ita tana kuka hawaye sai bin kumatunta yake,
"Binti lafiya"
"Abbu wallahi kacewa babynka ya daina naushina, kullum sai yayita naushina, Allah nima zan rama idan bai daina ba" tafada tana kuka,
Abin dariya yaso yabawa jabir amma sai ya guntse dariyarshi "yi hakuri kar ki rama yunwa yake jine shiyasa yake naushinki"
"Babu wani yunwa kofa kwanciya nayi ta gefen nan sai ya fara naushina idan nasaka rigar da ta dan kamani nanma sai ya yita naushina, Allah ka yi masa magana"
Abincin ya ajiye yamatsa kusa da cikin nata yana murmushi "babyn abbu stop biting your mom kaji, kabarta da dawainiyar da take yi da abbunka ma ya isheta"
Dago kanshi yayi, "basai kin ramaba nayi masa magana zai daina, amma takura shi kikeyi binti shiyasa, kidaina saka kayan da suka matseki wannan bubu din da nakawo miki tun jimawa su zaki rinka sakawa"
Baki ta zumburo ta dauki spoon tafara diban abincin tana ci, karba yayi yaci gaba da bata.
Tana koshi ya dauketa zuwa dakinta ya ajiyeta akan gado "binti kin kara nauyi da yawa, ki shirya gobe awurinki zan kwana"
Zabura tayi ta tashi tana zare ido "abbu nayafe, kayi zamanka awurin ummu har sai bayan na haihu, nidai kawai kubani aron al'amin mu rinka kwana tare"
"A'a binti idan ke kin yafe to ni ban yafe ba"
"Nidai abbu a'a" tafada tana tuttura baki,
"Saboda yanzu kin gaji dani ko?"
"Nidai abbu ka kawo min al'amin"
"Allah babu al'amin din da za akawo miki kinji nace Allah nidin dai da bakya so nine abokin kwananki agobe"
Komawa tayi ta kwanta tana tuttura masa baki sai kunkuni take "shi abbun nan wallahi wayone dashi kullum kullum sai yayita yimin wayo" yana jiyota tana kunkunin amma baya iya jin abinda take fada, cigaba da mammatsa mata jikinta yayi yana cewa
"Idan Allah ya saukeki lafiya zan sanar dake wasu hakkoki wadanda suka rataya akanki binti na".
_Masu karatu kusake hakuri mu hadu a page nagaba inda zamuji karshen labarin da yardar Allah, gaisuwa mai tarin yawa gareku dinbin masoyana masu karanta wannan labarin hakika ina alfahari daku._
*_Ummi A'isha_*👌🏻
[11/1, 8:18 AM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE..!*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_131-135_
~~~Bata ce dashi komai ba saboda ita yanzu ta kanta take yi domin alla alla take ta rabuda wannan cikin dake jikinta lafiya,
"Binti bakice komai ba ko natafi?" Ya tambayeta bayan ya zauna akusa da kafafunta yana jan yan yatsunta,
"Kafin katafi abbu ka hada min ruwa zanyi wanka" tace dashi tanata faman tutturo masa baki saboda abinda taji yafada dazu,
"Binti menene na fushin ne? Shi al'amin din idan nakawoshi me zai iya yimiki? Nikuwa kinga ko babu komai da daddare zan tashi na hada miki abincinki kici"
"Abbu nikam ka hada min ruwan wanka Allah zafi nake ji"
Mikewa jabir yayi ya shiga toilet dinta ya tara mata ruwan wanka a katon baho ya dawo ya taimaka mata zuwa cikin bathroom din, wankan ya tayata ya rakata dakinta ta zauna abakin gado,cikeda tausayawa jabir yake kallonta domin cikin nata ba karamin girma yayi ba sai kace wacce zata haifi 'yan biyu alhalin kuma a asibiti ance yaro dayane,
Mai ya mika mata ya nufi wurin kayan sawarta ya ciro mata wata koriyar atamfa mai hoton cokali ajiki wadda tasha dinkin bubu,
Ba wata kwalliya mai yawa tayi ba powder kawai ta shafa tasaka kwalli domin kwalli yana da mutukar amfani agun'ya mace yana daya daga cikin abubuwan da yake dawowa da mace martabarta a matsayinta na ya mace shiyasa ko ba zatayi wata kwalliya da yawaba to takan saka kwalli,
Turarruka kala kala ta fesa ta saka doguwar bubu din da jabir ya dauko mata, juyowa yayi yana kallonta bayan ya ajiye mata kayan kwalliyarta agaban mirror dinta,
"Kinyi kyau sosai bintina"