Sashe 41
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hannunta yaja yakaita gefen gado ya zaunar da ita ya karasa gaban mirror yafara shiryawa, man touch me nacikin wani gwangwani yayi amfani dashi ya shafe jikinsa sannan yafeshe ko ina najikinsa da turare bayan ya taje sajensa zuwa dan madaidaicin gemunsa,
Kayan bacci ya dauko dark blue yasaka amma har lokacin goodness idonta akasa yake bata iya kallonsa ba har sai da ya gama,
Falo suka koma ta zuba mishi abincin yafara ci,
"Ungo" ya debo acikin spoon tareda mika mata, matsawa tayi ta dafa kafarsa ta bude bakinta ya saka mata, hakika tana jin dadin irin kulawar da jabir yake bata,
Haka yaci gaba da ci itama yana bata har ya gama, alokacin ya tuna da cewar ya shigo mata da kayan dadi amma ya ajiye a babban falo,
"Binti jeki falon farko akwai abinda nasiyo ki dauko akan kujera"
Tashi tayi tafita tana juyi domin ko ina nata motsi yake,
Kawo masa tayi ta ajiye, kayan marmarine kankana da apple sai tsire gasasshe wanda yasha tumatir da albasa,
Kankanar da apple din ta dauka taje kitchen dinta tayi blending dinsu tazuba masa madara da suga ta kawo masa,
"Wai ni binti menene wannan ne kiketa bani?" Ya tambayeta yana kallonta duk da cewar yasan ko menene kuma yasan amfaninsa,
"Abbu lemo ne"
"To meye amfaninsa?"
"Abbu yana kara lafiya"
"Da me kuma?"
Shiru tayi cikeda kunya fata take aranta Allah dai yasa bai ganota ba,
"Kin dage sai abu kiketa dura min binti alhalin ke kuma raguwace,gashi kullum cikin period kike, ki barni haka kar kisa naje matakin da sai na kwanta agadon asibiti"
Jikinshi ta shiga ta kankameshi ta boye kanta acikin kirjinsa tana dariya,
"Kai dan Allah abbu"
Tafada cikin shagwaba,
"Ai gaskiyace binti"
Lemon ya tsiyaya ya fara sha yana bata itama, tsiren ya bude ya dauko yanka daya yasaka mata abaki ai tana cinyewa tafara tsalle ajikinsa tana huhhura bakinta,
"Menene?"
"Abbu yaji" harshenta ta turo waje wai yasha iska yadaina yi mata yajin,
Bata ankara ba kawai sai ji tayi jabir ya cafki harshen nata yafara yi mata maganin yajin da take ji, ya jima yana yi mata wani salo mai nauyin fada kafin ya saki bakinta yana yi mata dariya,
Tsiren yake taunawa har sai ya tsotse shi sannan sai ya saka mata acikin bakinta, mamaki da farin ciki fal cikin zuciyarta saboda ganin jabir yagama sakewa da ita yanzu,
"Abbu da ace haka sauran maza suke yin rayuwar aure da matansu to da kowacce mace ta dawwama agidanta tare da mijinta har abada, da baza su rinka samun sabani mai yawa ba"
Murmushi jabir yayi yaja karan hancinta,
"Hakika maza da yawa basa zama su karanci mace kafin su aureta, kawai auren akeyi ake zama, zama irin na kai da kafa, yawancin mutane basa binciken wacce irin rayuwa annabi ya gudanar tare da iyalinsa, annabi ya kasance yana wasa da iyalinsa yana cin abinci dasu har wanka annabi yana yi tareda matarsa nana A'isha Allah ya kara mata yarda tace muna yin wanka tare da annabi har hannuwanmu suna haduwa acikin kwaryar ruwan da muke yin wankan da ita, kinga kenan ya kamata kowanne miji ya kasance mai wasa da raha acikin iyalinsa anfi son miji ya dauki matarsa a matsayin abokiya,duk wadannan hadisan zan koya miki su insha Allah domin suna nan acikin zadizzaujaini"
Fuskarta ta rufe "kuma abbu muma zamu yi wankan tare?" Ta tambayeshi tana boye fuskarta,
"Sosai ma, ko kina so mufara practical daga yanzu?"
Kai ta girgiza "a'a abbu ba yau ba"
Murmushi yayi yana kokarin cire hannuwanta wanda ta boye fuskarta aciki,
"Yanzu karatu zan dora miki cigaban najiya, karanto naji"
"Abbu alqur'ani yanada girma, ayoyinsa sunada yawa surorinsa kuma sunada tsawo nikam har na karaya nasan bazan iya haddace koda rabinsa ba"
Tausayinta yaji har cikin ransa, hannunta yakamo yasake matso da ita jikinshi sosai "binti alqur'ani yanada sauki wurin karantawa, duk yawan nan nashi Allah yace zai saukakawa duk Wanda yaso karantashi, shiyasa babban abin kunyane ga duk wani musulmi wanda bai iya karatun alqur'ani ba, sai kiga mutum ya iya karatun hausa, ya iya karatun turanci amma bai iya karatun alqur'ani ba, yakamata mu dawo cikin hayyacinmu domin babu hanyar samun lada acikin sauki kamar karatun alqur'ani domin indai kana karantashi to duk harafi daya da zaka furta zaka samu lada goma, bafa kalma daya ba harafi daya kinga kuwa ai garabasar takai garabasa"
Kwantar da kanta tayi ajikin kirjinsa "gaskiya kam abbu, nima Allah ya taimakeni in iya karantashi domin na samu nadace da falalar da wadanda suke karantashi suke samu"
"Amin binti insha Allah zaki iya domin karantashi akwai falala mai yawan gaske shiyasa akalla koda shafi dayane arana yana dakyau mutum ya rinka karantawa"
Kwantar da kanta tayi akan cinyarshi yafara koya mata karatun, yana fada tana fada yana shafa gashin kanta har yagama dora mata karashen surar da yafara koyar da ita jiya,
Tashi tayi bayan sun kammala karatun tatafi sashenta domin yin shirin bacci, wanka ta silla ta shafe ko ina na jikinta da turaren white musk, sannan ta fesa body fantasy mai dadin kamshi,
Wata doguwar rigar bacci ta dauko acikin kayan da ummu al'amin ta aiko mata dasu,rigar doguwace mai budadden kirji kalarta kalar ruwan zuma, bata da nauyi ko kadan sai dan karan santsi,
Sashen jabir ta nufa bayan tagama kulle nata sashen,
Tana shiga dakinsa ta sameshi akishingide akan gado yana waya, sai da zuciyarta tayi rawa saboda jin yadda yake yin wayar, bazata iya tantancewa koda ummu yake wayar ba ko kuma da budurwarsa,
Kamar ta koma sashenta take ji domin zuciyarta wani irin bugu taji tana yi mata kamar zata fito daga cikin kirjinta,
Tafi minti goma kwance tana jinsa yana wayar jin bashida niyyar gamawa alokacin ya sanyata tashi ta fita daga dakin, sashenta ta koma ta kwanta adakinta tareda rungume katotuwar teddy dinta, sai kuma tafara kuka wanda bata san ko namenene ba,
Wani irin zafi takeji acikin ranta, ta dade ahaka har jabir ya shigo ya sameta, tun daga kofar dakin yake jiyo shasshekar kukanta har ya karaso kan gadon,
"Binti" ya kira sunanta ahankali,
Shiru tayi ta daina kukan sai dai har lokacin hawaye basu daina bin kumatunta ba,
Ahankali ya dago da ita ya zubawa fuskarta manyan idanuwansa,
"Binti meya faru?" Ya tambayeta muryarsa asanyaye,
Shiru tayi masa tafara share hawayen fuskarta,
"Binti wayar da kikaji inayi ce ta sakaki kuka?"
Nanma shirun tayi taci gaba da goge fuskarta,
"Da ummun al'amin nake yin wayar fa, kiyi hakuri kinji, binti kina da kishi da yawa amma akwai addu'ar da zan baki wacce zata sanyaya miki kishinki,kina so in fada miki?" Ya tambayeta yana kokarin kamo hannuwanta, (jabir idan ka tashi bayar da addu'ar ka fadeta afili domin masu so sunada yawa ciki harda ummi A'isha),
Kanta ta daga masa duk ranta babu dadi,
"Tashi muje ki kwanta kinji"
Kafada ta make tana kokarin kwanciya "ni yau anan zan kwana"
Murmushi yayi ya murza hannunta, "binti kefa rigimammiya ce, kina son nima na kwana anan ne yau?"
"Kai kayi tafiyarka dakinka kaje ka kwana" tafada tana turo baki domin haushinsa take ji haka kawai,
Rankwafawa yayi saitin fuskarta wanda har tana iya jiyo fitar numfashinsa wanda yake sauka akan kumatunta,
"Yau bakya jin tsorone da zaki kwana ke daya?"
"Yeah" tafada atakaice gamida kokarin juya masa baya, batayi zatoba taji ya dauketa cancak yana kokarin sauka da ita daga kan gadon, zillewa ta fara yi tana tutturo baki,
"Nidai ka ajiyeni natafi da kafata"
Direta yayi yaja hannunta suka fita, shine ya tsaya ya rufe mata part din nata sannan suka wuce,
Tana gaba tana doddoka kafa shikuma yana baya biye da ita har suka shiga cikin bedroom dinshi,
Can karshen gadon taje ta kwanta ta juya kanta ta kalli bango, murmushi yayi ya matsa kusa da ita,aranshi yana tunanin hali irin na mata kwata kwata ba a iya musu domin ita kanta ummu al'amin complain take yi masa wai ya rage bata kulawa ba kamar da ba saboda ya sake aure alhalin itace bata sani ba shi har yanzu ma babu abinda ya hadashi da amaryar, wannan dalilinne ya sashi fara kwantar mata da hankali yana bata hakuri har goodness ta shigo ta sameshi to ashe itanma nata borin yana gaba,
Yan yatsun kafarta ya kama yafara jansu daya bayan daya ahankali,
"Binti fushi kike yi dani ko? Ki fada min abinda nayi miki sai in baki hakuri"
Idanuwanta ta rufe kamar meyin bacci, tashi yayi yana kallonta,
"Kici gaba da yimin shiru idan ina yi miki magana, shekaran jiyama ai hakkina ne yasa wannan kwaron ya cijeki, yauma idan da rabon zai cijeki shikenan"
Fitila yaje ya kashe, ai goodness najin haka tayi maza ta matsa kusa da barin da yake kwanciya, yana zuwa yajita kwance awurin, murmushi yayi ya kwanta agefenta ya lalubo hannuwanta ya hada ya rike cikin nashi,
"Abbu kayi hakuri bazan sakeba"
"Na hakura binti, karma ki sake bani hakuri akan wannan maganar"
Kanta yafara shafawa yana sinsinar daddadan kamshin turaren da jikinta ke futarwa so yake ya gane kowanne irin turare ne amma ya kasa, haka yaci gaba da sinsinarta har bacci ya daukesu bayan yayi musu addu'o'in neman tsari.
***
Washe gari da safe misalin karfe 10 tana falonshi zaune kusa dashi taji yana waya kan akawo masa kayan abinci wadanda zai rabawa makotansu sadaka, girgiza kai tayi agaskiya jabir dan aljanna ne domin yana kare hakkin duk wanda yake tare dashi ta raya hakan acikin zuciyarta,
Hannunta taji yana matsawa ashe har ya kammala wayar batare da tasani ba saboda ta tafi duniyar tunani,
"Binti tunanin me kikeyi ne?"
"Abbu babu komai kawai dai ina tunanin irin yadda kake kyautatawa kowane duk wanda zama ya hadaka dashi ciki kuwa harda makotanka"
Kayan bacci ya dauko dark blue yasaka amma har lokacin goodness idonta akasa yake bata iya kallonsa ba har sai da ya gama,
Falo suka koma ta zuba mishi abincin yafara ci,
"Ungo" ya debo acikin spoon tareda mika mata, matsawa tayi ta dafa kafarsa ta bude bakinta ya saka mata, hakika tana jin dadin irin kulawar da jabir yake bata,
Haka yaci gaba da ci itama yana bata har ya gama, alokacin ya tuna da cewar ya shigo mata da kayan dadi amma ya ajiye a babban falo,
"Binti jeki falon farko akwai abinda nasiyo ki dauko akan kujera"
Tashi tayi tafita tana juyi domin ko ina nata motsi yake,
Kawo masa tayi ta ajiye, kayan marmarine kankana da apple sai tsire gasasshe wanda yasha tumatir da albasa,
Kankanar da apple din ta dauka taje kitchen dinta tayi blending dinsu tazuba masa madara da suga ta kawo masa,
"Wai ni binti menene wannan ne kiketa bani?" Ya tambayeta yana kallonta duk da cewar yasan ko menene kuma yasan amfaninsa,
"Abbu lemo ne"
"To meye amfaninsa?"
"Abbu yana kara lafiya"
"Da me kuma?"
Shiru tayi cikeda kunya fata take aranta Allah dai yasa bai ganota ba,
"Kin dage sai abu kiketa dura min binti alhalin ke kuma raguwace,gashi kullum cikin period kike, ki barni haka kar kisa naje matakin da sai na kwanta agadon asibiti"
Jikinshi ta shiga ta kankameshi ta boye kanta acikin kirjinsa tana dariya,
"Kai dan Allah abbu"
Tafada cikin shagwaba,
"Ai gaskiyace binti"
Lemon ya tsiyaya ya fara sha yana bata itama, tsiren ya bude ya dauko yanka daya yasaka mata abaki ai tana cinyewa tafara tsalle ajikinsa tana huhhura bakinta,
"Menene?"
"Abbu yaji" harshenta ta turo waje wai yasha iska yadaina yi mata yajin,
Bata ankara ba kawai sai ji tayi jabir ya cafki harshen nata yafara yi mata maganin yajin da take ji, ya jima yana yi mata wani salo mai nauyin fada kafin ya saki bakinta yana yi mata dariya,
Tsiren yake taunawa har sai ya tsotse shi sannan sai ya saka mata acikin bakinta, mamaki da farin ciki fal cikin zuciyarta saboda ganin jabir yagama sakewa da ita yanzu,
"Abbu da ace haka sauran maza suke yin rayuwar aure da matansu to da kowacce mace ta dawwama agidanta tare da mijinta har abada, da baza su rinka samun sabani mai yawa ba"
Murmushi jabir yayi yaja karan hancinta,
"Hakika maza da yawa basa zama su karanci mace kafin su aureta, kawai auren akeyi ake zama, zama irin na kai da kafa, yawancin mutane basa binciken wacce irin rayuwa annabi ya gudanar tare da iyalinsa, annabi ya kasance yana wasa da iyalinsa yana cin abinci dasu har wanka annabi yana yi tareda matarsa nana A'isha Allah ya kara mata yarda tace muna yin wanka tare da annabi har hannuwanmu suna haduwa acikin kwaryar ruwan da muke yin wankan da ita, kinga kenan ya kamata kowanne miji ya kasance mai wasa da raha acikin iyalinsa anfi son miji ya dauki matarsa a matsayin abokiya,duk wadannan hadisan zan koya miki su insha Allah domin suna nan acikin zadizzaujaini"
Fuskarta ta rufe "kuma abbu muma zamu yi wankan tare?" Ta tambayeshi tana boye fuskarta,
"Sosai ma, ko kina so mufara practical daga yanzu?"
Kai ta girgiza "a'a abbu ba yau ba"
Murmushi yayi yana kokarin cire hannuwanta wanda ta boye fuskarta aciki,
"Yanzu karatu zan dora miki cigaban najiya, karanto naji"
"Abbu alqur'ani yanada girma, ayoyinsa sunada yawa surorinsa kuma sunada tsawo nikam har na karaya nasan bazan iya haddace koda rabinsa ba"
Tausayinta yaji har cikin ransa, hannunta yakamo yasake matso da ita jikinshi sosai "binti alqur'ani yanada sauki wurin karantawa, duk yawan nan nashi Allah yace zai saukakawa duk Wanda yaso karantashi, shiyasa babban abin kunyane ga duk wani musulmi wanda bai iya karatun alqur'ani ba, sai kiga mutum ya iya karatun hausa, ya iya karatun turanci amma bai iya karatun alqur'ani ba, yakamata mu dawo cikin hayyacinmu domin babu hanyar samun lada acikin sauki kamar karatun alqur'ani domin indai kana karantashi to duk harafi daya da zaka furta zaka samu lada goma, bafa kalma daya ba harafi daya kinga kuwa ai garabasar takai garabasa"
Kwantar da kanta tayi ajikin kirjinsa "gaskiya kam abbu, nima Allah ya taimakeni in iya karantashi domin na samu nadace da falalar da wadanda suke karantashi suke samu"
"Amin binti insha Allah zaki iya domin karantashi akwai falala mai yawan gaske shiyasa akalla koda shafi dayane arana yana dakyau mutum ya rinka karantawa"
Kwantar da kanta tayi akan cinyarshi yafara koya mata karatun, yana fada tana fada yana shafa gashin kanta har yagama dora mata karashen surar da yafara koyar da ita jiya,
Tashi tayi bayan sun kammala karatun tatafi sashenta domin yin shirin bacci, wanka ta silla ta shafe ko ina na jikinta da turaren white musk, sannan ta fesa body fantasy mai dadin kamshi,
Wata doguwar rigar bacci ta dauko acikin kayan da ummu al'amin ta aiko mata dasu,rigar doguwace mai budadden kirji kalarta kalar ruwan zuma, bata da nauyi ko kadan sai dan karan santsi,
Sashen jabir ta nufa bayan tagama kulle nata sashen,
Tana shiga dakinsa ta sameshi akishingide akan gado yana waya, sai da zuciyarta tayi rawa saboda jin yadda yake yin wayar, bazata iya tantancewa koda ummu yake wayar ba ko kuma da budurwarsa,
Kamar ta koma sashenta take ji domin zuciyarta wani irin bugu taji tana yi mata kamar zata fito daga cikin kirjinta,
Tafi minti goma kwance tana jinsa yana wayar jin bashida niyyar gamawa alokacin ya sanyata tashi ta fita daga dakin, sashenta ta koma ta kwanta adakinta tareda rungume katotuwar teddy dinta, sai kuma tafara kuka wanda bata san ko namenene ba,
Wani irin zafi takeji acikin ranta, ta dade ahaka har jabir ya shigo ya sameta, tun daga kofar dakin yake jiyo shasshekar kukanta har ya karaso kan gadon,
"Binti" ya kira sunanta ahankali,
Shiru tayi ta daina kukan sai dai har lokacin hawaye basu daina bin kumatunta ba,
Ahankali ya dago da ita ya zubawa fuskarta manyan idanuwansa,
"Binti meya faru?" Ya tambayeta muryarsa asanyaye,
Shiru tayi masa tafara share hawayen fuskarta,
"Binti wayar da kikaji inayi ce ta sakaki kuka?"
Nanma shirun tayi taci gaba da goge fuskarta,
"Da ummun al'amin nake yin wayar fa, kiyi hakuri kinji, binti kina da kishi da yawa amma akwai addu'ar da zan baki wacce zata sanyaya miki kishinki,kina so in fada miki?" Ya tambayeta yana kokarin kamo hannuwanta, (jabir idan ka tashi bayar da addu'ar ka fadeta afili domin masu so sunada yawa ciki harda ummi A'isha),
Kanta ta daga masa duk ranta babu dadi,
"Tashi muje ki kwanta kinji"
Kafada ta make tana kokarin kwanciya "ni yau anan zan kwana"
Murmushi yayi ya murza hannunta, "binti kefa rigimammiya ce, kina son nima na kwana anan ne yau?"
"Kai kayi tafiyarka dakinka kaje ka kwana" tafada tana turo baki domin haushinsa take ji haka kawai,
Rankwafawa yayi saitin fuskarta wanda har tana iya jiyo fitar numfashinsa wanda yake sauka akan kumatunta,
"Yau bakya jin tsorone da zaki kwana ke daya?"
"Yeah" tafada atakaice gamida kokarin juya masa baya, batayi zatoba taji ya dauketa cancak yana kokarin sauka da ita daga kan gadon, zillewa ta fara yi tana tutturo baki,
"Nidai ka ajiyeni natafi da kafata"
Direta yayi yaja hannunta suka fita, shine ya tsaya ya rufe mata part din nata sannan suka wuce,
Tana gaba tana doddoka kafa shikuma yana baya biye da ita har suka shiga cikin bedroom dinshi,
Can karshen gadon taje ta kwanta ta juya kanta ta kalli bango, murmushi yayi ya matsa kusa da ita,aranshi yana tunanin hali irin na mata kwata kwata ba a iya musu domin ita kanta ummu al'amin complain take yi masa wai ya rage bata kulawa ba kamar da ba saboda ya sake aure alhalin itace bata sani ba shi har yanzu ma babu abinda ya hadashi da amaryar, wannan dalilinne ya sashi fara kwantar mata da hankali yana bata hakuri har goodness ta shigo ta sameshi to ashe itanma nata borin yana gaba,
Yan yatsun kafarta ya kama yafara jansu daya bayan daya ahankali,
"Binti fushi kike yi dani ko? Ki fada min abinda nayi miki sai in baki hakuri"
Idanuwanta ta rufe kamar meyin bacci, tashi yayi yana kallonta,
"Kici gaba da yimin shiru idan ina yi miki magana, shekaran jiyama ai hakkina ne yasa wannan kwaron ya cijeki, yauma idan da rabon zai cijeki shikenan"
Fitila yaje ya kashe, ai goodness najin haka tayi maza ta matsa kusa da barin da yake kwanciya, yana zuwa yajita kwance awurin, murmushi yayi ya kwanta agefenta ya lalubo hannuwanta ya hada ya rike cikin nashi,
"Abbu kayi hakuri bazan sakeba"
"Na hakura binti, karma ki sake bani hakuri akan wannan maganar"
Kanta yafara shafawa yana sinsinar daddadan kamshin turaren da jikinta ke futarwa so yake ya gane kowanne irin turare ne amma ya kasa, haka yaci gaba da sinsinarta har bacci ya daukesu bayan yayi musu addu'o'in neman tsari.
***
Washe gari da safe misalin karfe 10 tana falonshi zaune kusa dashi taji yana waya kan akawo masa kayan abinci wadanda zai rabawa makotansu sadaka, girgiza kai tayi agaskiya jabir dan aljanna ne domin yana kare hakkin duk wanda yake tare dashi ta raya hakan acikin zuciyarta,
Hannunta taji yana matsawa ashe har ya kammala wayar batare da tasani ba saboda ta tafi duniyar tunani,
"Binti tunanin me kikeyi ne?"
"Abbu babu komai kawai dai ina tunanin irin yadda kake kyautatawa kowane duk wanda zama ya hadaka dashi ciki kuwa harda makotanka"