Sashe 29
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kansa ya girgiza yana murmushi "Allah ne ya sanar damu acikin littafinsa mai tsarki, duk wannan labarin da na baki ba wani bane ya zauna ya shiryashi ko ya kirkireshi ba, no, abunda ya farune Allah ya sanar damu ta harshen annabinsa"
Kallonsa kawai take yi yanda yake furta maganganun daya bayan daya da dan mitsitsin bakinshi,
"Duk wani abu da kika sani na rayuwar duniya da rayuwar da za ayi bayan anbar duniya to duk alqur'ani ya sanar damu"
"Tunda hakane kullum zaka rinka bani labarin nima ina ji, sannan nima zan fada maka irin namu labarin wanda Bible yazo mana dashi"
Murmushi ya danyi mai kayatarwa wanda har sai da fararen hakoransa masu mutukar haske kamar farar takarda suka bayyana,
"Ashe kema kina da labari?"
Ya tambayeta,
"Yes, i have it, indai zaka ji zan baka"
Murmusawa ya sake yi yana kallonta, tana kwance ta rungume pillow sannan duk wadannan maganganun da suke yi idanuwanta a lumshe suke, amma aranta tunani take yi lallai tunda aka samu labari irin wannan acikin littafin musulmai to za asamu wasu labaran masu kayatarwa wadanda suka fi wannan.
"Nima ina so indai zaki fada min" ya bata amsa yana kallonta,
"Zan baka sai bayan ka bani wani gobe"
"Allah ya kaimu, yanzu dare yayi ki kwanta kiyi bacci nima bacci zanyi tunda yau kin rikeni kin hanani sallar dare"
Murmushi tayi bata ce komai ba ta juya ta gyara kwanciyarta, toilet ya tashi ya shiga ya dauro alwala ya fito yazo ya kwanta agefen gadon bayan ya gabatar da addu'o'insa, tana jinsa har ya gama ya kashe wutar dakin, kasa bacci tayi sai tunanin labarin da jabir ya bata take yi amma wannan abin mamaki da yawa yake yanzu wannan labarin dagaske ya faru? Ta tambayi kanta, tana nan kwance tana ta sharhin wannan labarin har bacci ya dauketa.
Asubar fari jabir ya tashi kamar jiya yau ma ganinta yayi kwance ajikinsa ta rungumeshi tana ta bacci, janyeta daga jikinshi yayi ya tashi ta shiga _bathroom_,masallaci ya tafi bashi ya dawo ba sai wurin 6:30,lokacin da ya dawo yana shiga bedroom dinshi ya hangota acikin kitchen tana aiki, kwanciya yayi ya dan mike domin jiya bai samu bacci da yawa ba.
Wunin ranar goodness ta yishi ne cikin doki domin alla alla take yi dare yayi su zauna da jabir domin ya bata labari, tunda wuwwuri tayi wanka ta shirya tasaka _sleeping dress_ dinta light brown colour, ta kinkimi abincin jabir ta nufi sashensa amma har lokacin bai dawo ba gashi wurin karfe 9,cike da damuwa ta ajiye kwanukan abincin ta juya ta koma sashenta, kallo ta kunna ta fara kallon wani american film mai suna _the chronicles of narniar_ tana kwance tana kallon har ta fara dan bacci sama sama daga karshe ma baccin ya dauketa gaba daya.
Karfe _10_ jabir ya dawo, sashensa yaje ya ci abinci yayi wanka ya sake sabon shiri cikin gajeren wando baki da yar t shirt fara mai gajeren hannu (su mal jabir an dawo samari), net ya shiga na wasu yan mintuna, baifi 30 minutes ba ya fita ya rufe laptop dinshi,
Sashen goodness ya shiga ta baya, tana falo tana bacci ga tv tana yi ita kadai,
Sunkuyawa yayi ya fara kiranta ahankali "goodness" sai da ya kirata wurin sau uku sannan tayi firgigit ta tashi,
"Abbu yaushe ka dawo?" Ta tambayeshi tana murtsuke idanuwanta,
"Yau ba kya son labarin ne kika kwanta kike bacci?"
"No, ina so na kwantane kafin ka dawo"
Tv din ta kashe tabi bayanshi zuwa sashensa, ba karamin kyau yayi mata ba domin ya zama dan saurayi sak,
Acan inda ta saba kwanciya yauma ta kwanta, shi kuma yana daga farkon gadon azaune,
"Yau wanne labari zan baki? Ko kece zaki bani?"
"Ka fara bani, nima zan baka idan ka gama"
K'issar annabi musa da dan uwansa annabi harun ya fara bata da irin gwagwarmayar da suka yi da fir'auna da hamana da dan karuna,
Bakinshi kawai take bi da kallo tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta wai yau itace jabir yake yiwa dogon labari irin wannan duk da tasan sa'a kawai take ci domin surutu ba sabonsa bane,a bangare daya kuma na zuciyarta tana jinjina labarin domin labarin yakai inda duk wata hikima takai domin ba karamar hikima bace acikin rayuwar annabi musa,
Zumbur ta tashi zaune tana kallon jabir,
"Abbu kar ka cemin basuyi nasara ba a gasar da aka shirya ta matsafan nahiyar"
Kallonta ya daga kai yayi "sunyi nasara ai sandar annabi musa micijiya ta zama ta rinka hadiye duk wasu abubuwa wanda suke ba kanana ba, anan sauran mutane suka yi imani dasu"
Komawa tayi ta kwanta tana murmushi domin labarin da yake bata har wani imagining din abin take acikin kwakwalwarta.
Lokacin da ya kammala fada mata k'issar ba karamin mamaki tayi ba jin wai har yanzu fir'auna yana nan aduniya agidan tarihi a kasar misra,
"Abbu wannan labarin da ka fada min dagaske ya faru?"
Daga mata kai yayi "its true life story, ni har fir'aunan nagani lokacin da naje gidan tarihin, ai Allah ne ya fada cewar zai tseratar da gawar fir'auna daga lalacewa domin ta zama aya ga mutane"
Mikewa tayi daga kwanciyar da take "gaskiya sunsha gwagwarmaya daga shi har dan uwanshi, sannan abinda yafi bani tausayi agame dashi shine irin yanda dan uwansa d'an karuna ya juya masa baya yakoma ya hada kai da fir'auna bayan ya zama mai arziki, ya manta da cewar shine yayi masa addu'a har Allah ya bashi arzikin"
"Ba mantawa yayi ba tsabar shak'iyanci ne kawai,amma duk wannan tawayen dasu fir'auna suka yi hakan bai hana annabi musa samun nasara ba domin yanada yawan al'umma shiyasa afilin alk'iyama za ahango wasu al'umma masu yawan gaske har annabi Muhammad (s.a.w) zai taso domin ya zata al'ummarsa ce sai ace wannan al'ummar annabi Musa ne (A.S)"
Shiru tayi zuciyarta cikeda mamakin yadda aka yi har teku ya daskare ya rabe gida biyu mutane suka wuce ta cikinsa,
"Tunda nagama baki labarin to nima ki bani wani inji" yace da ita yana gyara kwanciyarsa,
Dan murmushi tayi tace "ni labarin ruhu zan baka domin labarinsa yazo mana acikin Bible, shi ruhu ba mutum bane kuma ba aljan bane sannan bashi da farko kuma bashida karshe....!"
Katseta yayi "shima kenan ubangijinku ne?"
Kai ta girgiza "no, he's not our lord but...!"
"But what? Goodness don't deceive your self,indai wannan ruhun da kike fada ba ubangijinku bane to babu hujjar da zai sa ki kira annabi Isah a matsayin ubangijinki domin shi wannan ruhun da kikace Bible yazo muku da labarinsa ai yafi annabi Isah abin mamaki, dalili shine shi annabi Isah baku bashi wannan siffofin ba amma shi ruhu gashi kun bashi"
Kallo ta bishi dashi tana dan nazari akanshi, "Kaine fa kace in baka labari kuma shine daga fara fada maka zaka yi interrupting dina" ta fada fuskarta ta kwakkwabe kamar zata yi kuka,
"Ba katse ki nayi ba, ki bari gobe zan baki k'issar shi kanshi annabi Isah din da ta mahaifiyarshi Nana maryam, labarin nakine bana son jinshi saboda na rigada na sanshi tun dadewa, ko baki san nima na karanta bible ba?"
Kallonshi tayi da sauri "are you serious?" Ta tambayeshi,
"Am serious goodness, duk wani abu wanda ke cikin Bible na sanshi na karantashi"
Jingina tayi da jikin _pillow_ tana kallonsa, "ki bari sai gobe zan fada miki waye yesu, almasihu, zan sanar dake k'issarsa tun zuwanshi duniya da kuma dawowar da zai yi nan gaba"
"Dawowa? Zai dawo nan gaba?" Tafada cikeda mamaki,
"Yes zai dawo nan gaba haka Allah ya sanar damu" ya bata amsa yana kokarin tashi,
Batare da tace masa komai ba ta koma ta kwanta tana binsa da kallo har ya shige cikin _bathroom_. Tana nan kwance har ya fito ya tsaya agaban gadon ta taso tazo inda yake ta mika masa hannuwanta ya karanto mata addu'o'in kwanciya bacci ta koma ta kwanta tana shasshafe jikinta da tafukan hannayenta.
Ido ta tsura mishi lokacin da ya tada kabbarar sallar nafilar da zaiyi, tana nan kwance tana kallonsa har bacci ya dauketa bata san lokacin da jabir ya dawo kan gadon ya kwanta ba.
Washe gari da safe da ciwon cibiya ta tashi amma bata sanar da jabir ba har ya shirya ya tafi office aranar mamanta tazo gidan domin ganin lafiyarta duk da cewa suna haduwa a church duk ranar lahadi, huduba iri iri ma tayi mata kafin tabar gidan, a irin kudin da wani lokacin jabir yake bata ta dauko ta bawa ma _2000_ haka ma ta karba babu wani farin ciki domin jikinta ya gama yin sanyi da lamarin goodness gani take kamar goodness din zata karbi addinin musulunci.
K'arfe 8:30 jabir yana zaune a falonsa yana kallon huda tv inda ake gudanar da wani program _(Qur'an and the science)_ gefenshi kuma wasu littattafai ne a ajiye wadanda ya gama dubasu,
Kallonsa goodness tayi lokacin da ta shiga cikin falon acikin ranta tana cewa "kullum baka gajiya da karance karance da kallon wannan channel din"
"Sannu abbu" ta fada tareda zama a k'asa can nesa dashi kadan,
"Yawwa" yace ba tare da ya jiyo ya kalleta ba,
"Abbu ina son zuwa hospital gobe, zan ga dr"
Sai a lokacin ya juyo da hankalinsa zuwa gareta,
"Meya faru?"
"Cikina ne yake ciwo" tafada kanta a sunkuye,
"Cikinki ko mararki?"
"No,cikina ne"
"Ba period pain bane?"
"Abbu ba shi bane, cibiyata ce ke yin jini"
"Jini? Tun yaushe?"
"Abbu dama ya jima yana yi to yanzu ne yayi yawa yau da safe naga jinin yana fita da yawa"
"Let me see"
D'agowa tayi ta kalleshi amma ta kasa motsawa daga inda take,
"Ba kiji abinda na fada bane? Zo nagani"
Hada ido suka yi amma har lokacin bata da niyyar tashi,
"Abbu ba sai ka gani ba"
"Ok ni ba sai Nagani ba amma zaki iya nunawa dr shi yagani ko? You are not serious"
Wayarshi ya dauka ya fara kiran dr din da yake dubashi idan ba shida lfy, nan ya fara fada masa matsalar goodness, tambayarshi dr din yayi cewar yaya cibiyar tayi, tayi rami ne ko kuma daga can ciki jinin ke fitowa,
Kallonsa kawai take yi yanda yake furta maganganun daya bayan daya da dan mitsitsin bakinshi,
"Duk wani abu da kika sani na rayuwar duniya da rayuwar da za ayi bayan anbar duniya to duk alqur'ani ya sanar damu"
"Tunda hakane kullum zaka rinka bani labarin nima ina ji, sannan nima zan fada maka irin namu labarin wanda Bible yazo mana dashi"
Murmushi ya danyi mai kayatarwa wanda har sai da fararen hakoransa masu mutukar haske kamar farar takarda suka bayyana,
"Ashe kema kina da labari?"
Ya tambayeta,
"Yes, i have it, indai zaka ji zan baka"
Murmusawa ya sake yi yana kallonta, tana kwance ta rungume pillow sannan duk wadannan maganganun da suke yi idanuwanta a lumshe suke, amma aranta tunani take yi lallai tunda aka samu labari irin wannan acikin littafin musulmai to za asamu wasu labaran masu kayatarwa wadanda suka fi wannan.
"Nima ina so indai zaki fada min" ya bata amsa yana kallonta,
"Zan baka sai bayan ka bani wani gobe"
"Allah ya kaimu, yanzu dare yayi ki kwanta kiyi bacci nima bacci zanyi tunda yau kin rikeni kin hanani sallar dare"
Murmushi tayi bata ce komai ba ta juya ta gyara kwanciyarta, toilet ya tashi ya shiga ya dauro alwala ya fito yazo ya kwanta agefen gadon bayan ya gabatar da addu'o'insa, tana jinsa har ya gama ya kashe wutar dakin, kasa bacci tayi sai tunanin labarin da jabir ya bata take yi amma wannan abin mamaki da yawa yake yanzu wannan labarin dagaske ya faru? Ta tambayi kanta, tana nan kwance tana ta sharhin wannan labarin har bacci ya dauketa.
Asubar fari jabir ya tashi kamar jiya yau ma ganinta yayi kwance ajikinsa ta rungumeshi tana ta bacci, janyeta daga jikinshi yayi ya tashi ta shiga _bathroom_,masallaci ya tafi bashi ya dawo ba sai wurin 6:30,lokacin da ya dawo yana shiga bedroom dinshi ya hangota acikin kitchen tana aiki, kwanciya yayi ya dan mike domin jiya bai samu bacci da yawa ba.
Wunin ranar goodness ta yishi ne cikin doki domin alla alla take yi dare yayi su zauna da jabir domin ya bata labari, tunda wuwwuri tayi wanka ta shirya tasaka _sleeping dress_ dinta light brown colour, ta kinkimi abincin jabir ta nufi sashensa amma har lokacin bai dawo ba gashi wurin karfe 9,cike da damuwa ta ajiye kwanukan abincin ta juya ta koma sashenta, kallo ta kunna ta fara kallon wani american film mai suna _the chronicles of narniar_ tana kwance tana kallon har ta fara dan bacci sama sama daga karshe ma baccin ya dauketa gaba daya.
Karfe _10_ jabir ya dawo, sashensa yaje ya ci abinci yayi wanka ya sake sabon shiri cikin gajeren wando baki da yar t shirt fara mai gajeren hannu (su mal jabir an dawo samari), net ya shiga na wasu yan mintuna, baifi 30 minutes ba ya fita ya rufe laptop dinshi,
Sashen goodness ya shiga ta baya, tana falo tana bacci ga tv tana yi ita kadai,
Sunkuyawa yayi ya fara kiranta ahankali "goodness" sai da ya kirata wurin sau uku sannan tayi firgigit ta tashi,
"Abbu yaushe ka dawo?" Ta tambayeshi tana murtsuke idanuwanta,
"Yau ba kya son labarin ne kika kwanta kike bacci?"
"No, ina so na kwantane kafin ka dawo"
Tv din ta kashe tabi bayanshi zuwa sashensa, ba karamin kyau yayi mata ba domin ya zama dan saurayi sak,
Acan inda ta saba kwanciya yauma ta kwanta, shi kuma yana daga farkon gadon azaune,
"Yau wanne labari zan baki? Ko kece zaki bani?"
"Ka fara bani, nima zan baka idan ka gama"
K'issar annabi musa da dan uwansa annabi harun ya fara bata da irin gwagwarmayar da suka yi da fir'auna da hamana da dan karuna,
Bakinshi kawai take bi da kallo tana mai jin wani irin sanyi acikin zuciyarta wai yau itace jabir yake yiwa dogon labari irin wannan duk da tasan sa'a kawai take ci domin surutu ba sabonsa bane,a bangare daya kuma na zuciyarta tana jinjina labarin domin labarin yakai inda duk wata hikima takai domin ba karamar hikima bace acikin rayuwar annabi musa,
Zumbur ta tashi zaune tana kallon jabir,
"Abbu kar ka cemin basuyi nasara ba a gasar da aka shirya ta matsafan nahiyar"
Kallonta ya daga kai yayi "sunyi nasara ai sandar annabi musa micijiya ta zama ta rinka hadiye duk wasu abubuwa wanda suke ba kanana ba, anan sauran mutane suka yi imani dasu"
Komawa tayi ta kwanta tana murmushi domin labarin da yake bata har wani imagining din abin take acikin kwakwalwarta.
Lokacin da ya kammala fada mata k'issar ba karamin mamaki tayi ba jin wai har yanzu fir'auna yana nan aduniya agidan tarihi a kasar misra,
"Abbu wannan labarin da ka fada min dagaske ya faru?"
Daga mata kai yayi "its true life story, ni har fir'aunan nagani lokacin da naje gidan tarihin, ai Allah ne ya fada cewar zai tseratar da gawar fir'auna daga lalacewa domin ta zama aya ga mutane"
Mikewa tayi daga kwanciyar da take "gaskiya sunsha gwagwarmaya daga shi har dan uwanshi, sannan abinda yafi bani tausayi agame dashi shine irin yanda dan uwansa d'an karuna ya juya masa baya yakoma ya hada kai da fir'auna bayan ya zama mai arziki, ya manta da cewar shine yayi masa addu'a har Allah ya bashi arzikin"
"Ba mantawa yayi ba tsabar shak'iyanci ne kawai,amma duk wannan tawayen dasu fir'auna suka yi hakan bai hana annabi musa samun nasara ba domin yanada yawan al'umma shiyasa afilin alk'iyama za ahango wasu al'umma masu yawan gaske har annabi Muhammad (s.a.w) zai taso domin ya zata al'ummarsa ce sai ace wannan al'ummar annabi Musa ne (A.S)"
Shiru tayi zuciyarta cikeda mamakin yadda aka yi har teku ya daskare ya rabe gida biyu mutane suka wuce ta cikinsa,
"Tunda nagama baki labarin to nima ki bani wani inji" yace da ita yana gyara kwanciyarsa,
Dan murmushi tayi tace "ni labarin ruhu zan baka domin labarinsa yazo mana acikin Bible, shi ruhu ba mutum bane kuma ba aljan bane sannan bashi da farko kuma bashida karshe....!"
Katseta yayi "shima kenan ubangijinku ne?"
Kai ta girgiza "no, he's not our lord but...!"
"But what? Goodness don't deceive your self,indai wannan ruhun da kike fada ba ubangijinku bane to babu hujjar da zai sa ki kira annabi Isah a matsayin ubangijinki domin shi wannan ruhun da kikace Bible yazo muku da labarinsa ai yafi annabi Isah abin mamaki, dalili shine shi annabi Isah baku bashi wannan siffofin ba amma shi ruhu gashi kun bashi"
Kallo ta bishi dashi tana dan nazari akanshi, "Kaine fa kace in baka labari kuma shine daga fara fada maka zaka yi interrupting dina" ta fada fuskarta ta kwakkwabe kamar zata yi kuka,
"Ba katse ki nayi ba, ki bari gobe zan baki k'issar shi kanshi annabi Isah din da ta mahaifiyarshi Nana maryam, labarin nakine bana son jinshi saboda na rigada na sanshi tun dadewa, ko baki san nima na karanta bible ba?"
Kallonshi tayi da sauri "are you serious?" Ta tambayeshi,
"Am serious goodness, duk wani abu wanda ke cikin Bible na sanshi na karantashi"
Jingina tayi da jikin _pillow_ tana kallonsa, "ki bari sai gobe zan fada miki waye yesu, almasihu, zan sanar dake k'issarsa tun zuwanshi duniya da kuma dawowar da zai yi nan gaba"
"Dawowa? Zai dawo nan gaba?" Tafada cikeda mamaki,
"Yes zai dawo nan gaba haka Allah ya sanar damu" ya bata amsa yana kokarin tashi,
Batare da tace masa komai ba ta koma ta kwanta tana binsa da kallo har ya shige cikin _bathroom_. Tana nan kwance har ya fito ya tsaya agaban gadon ta taso tazo inda yake ta mika masa hannuwanta ya karanto mata addu'o'in kwanciya bacci ta koma ta kwanta tana shasshafe jikinta da tafukan hannayenta.
Ido ta tsura mishi lokacin da ya tada kabbarar sallar nafilar da zaiyi, tana nan kwance tana kallonsa har bacci ya dauketa bata san lokacin da jabir ya dawo kan gadon ya kwanta ba.
Washe gari da safe da ciwon cibiya ta tashi amma bata sanar da jabir ba har ya shirya ya tafi office aranar mamanta tazo gidan domin ganin lafiyarta duk da cewa suna haduwa a church duk ranar lahadi, huduba iri iri ma tayi mata kafin tabar gidan, a irin kudin da wani lokacin jabir yake bata ta dauko ta bawa ma _2000_ haka ma ta karba babu wani farin ciki domin jikinta ya gama yin sanyi da lamarin goodness gani take kamar goodness din zata karbi addinin musulunci.
K'arfe 8:30 jabir yana zaune a falonsa yana kallon huda tv inda ake gudanar da wani program _(Qur'an and the science)_ gefenshi kuma wasu littattafai ne a ajiye wadanda ya gama dubasu,
Kallonsa goodness tayi lokacin da ta shiga cikin falon acikin ranta tana cewa "kullum baka gajiya da karance karance da kallon wannan channel din"
"Sannu abbu" ta fada tareda zama a k'asa can nesa dashi kadan,
"Yawwa" yace ba tare da ya jiyo ya kalleta ba,
"Abbu ina son zuwa hospital gobe, zan ga dr"
Sai a lokacin ya juyo da hankalinsa zuwa gareta,
"Meya faru?"
"Cikina ne yake ciwo" tafada kanta a sunkuye,
"Cikinki ko mararki?"
"No,cikina ne"
"Ba period pain bane?"
"Abbu ba shi bane, cibiyata ce ke yin jini"
"Jini? Tun yaushe?"
"Abbu dama ya jima yana yi to yanzu ne yayi yawa yau da safe naga jinin yana fita da yawa"
"Let me see"
D'agowa tayi ta kalleshi amma ta kasa motsawa daga inda take,
"Ba kiji abinda na fada bane? Zo nagani"
Hada ido suka yi amma har lokacin bata da niyyar tashi,
"Abbu ba sai ka gani ba"
"Ok ni ba sai Nagani ba amma zaki iya nunawa dr shi yagani ko? You are not serious"
Wayarshi ya dauka ya fara kiran dr din da yake dubashi idan ba shida lfy, nan ya fara fada masa matsalar goodness, tambayarshi dr din yayi cewar yaya cibiyar tayi, tayi rami ne ko kuma daga can ciki jinin ke fitowa,