← Book details Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 64

Sashe 47

Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Awaje papa ya tare bahijja yayi mata nasiha ya bata hakuri akan abinda mamanta take yimata yanzu, sai da ya kwantar mata da hankali sannan suka tafi gida ita da jabir.

Duk da tana tsoron halin da ta tsinci kanta aciki a hannun abbu rannan hakan bai hanata shirya kanta awannan daren ba domin wanka ta silla ta caba ado tasha wata rikitacciyar rigar bacci ruwan toka mai mutukar santsi, gaban rigar abude yake hakama bayanta, turarruka masu dadi tabi jikinta dasu ta shafa ta dauki kamshi tako ina, kwalliyar da tayiwa fuskarta kuwa tamkar mai shirin zuwa dinner,

Afalo ta iske jabir yana zaune yana waya da matarsa, ganin shigowar bahijja yasashi yaji ya fara rudewa, hannu ya mika mata yaci gaba da yin wayar, ahankali cikin tafiyar jan hankali ta karasa jikinsa ta zauna tana murmushi,

Sinsinar jikinta yafara yi yana shakar kamshin jikinta, sallama yayiwa ummu al'amin ya kashe wayar yana yiwa bahijja wani irin kallo na musamman,

"Muje ki kwanta ko binti" yafada cikin muryarsa wacce taji tasake yin sanyi,

"Abbu tun yanzu?" Tafada tana kada masa idanuwanta,

"Ehhh, zo muje"tashi yayi yaja hannunta suka shiga cikin dakin nasa,

Yauma kamar rannan babu canji hakan yasata niyyar zama dashi domin su fuskanci juna kamar yadda yayarta tabata shawara, wannan shine abinda ummu al'amin takasa tabarshi acikin ranta gashi har yau bata samu waraka ba.

Kwanan ma 10 a asibiti aka sallameta bayan dr ya dorata akan magani wanda zata runka sha domin samin sauki,

Kayansu suka harhada suka tafi gida koda sukaje gidanma ma taki sakin fuska musamman ma ga bahijja sai dai harara take aika mata amma baya ga haka taki cemata komai, har bayan sallar isha suna gidan itada yayarta,

Jabirne yazo daukarta yayi mata waya yace tafito su tafi, sallama tayiwa ma amma ko kallonta bata yiba hakan yasata fita duk ranta babu dadi, atsakar gida ta iske papa cikin faran faran suka yi sallama fita inda jabir ke jiranta, yau shi kadai ne ko driver baizo dashi ba, yayi wanka yasha t shirt da jeans yayi kyau sosai kamar bashi ba,

Zama tayi akujerar dake gefensa tana kallonsa cikeda so, "abbu wannan kyaun fa?"

Hannunta ya kama yana murmushi, "daga zance nake shiyasa"

Ido ta tsura masa tana kallon dan mitsitsin bakinshi,

"Abbu zansha chocolate"

"Banida chocolate acikin motar nan sai dai agida"

"Da akwai abbu" ta bashi amsa tana mai matsawa jikinsa,

"To dauki a inda kika ganta" yafada yana murmushi, ahankali takai bakinta kan nashi tahada,

"Ga chocolate nan awurinka kuma sai kace min babu"

Girgiza kai yayi "Allah yabaki hakuri ai ban san wannan kike nufi ba"

"Shi nake nufi abbu, ai yafi chocholate ma dadi"

Kallonta yayi da manyan idanuwansa, "dagaske?"

"Um dagaske mana, sai dai abbu meyasa baka jimawa...?" Sai kuma tayi shiru bata karasa ba,

"Bana jimawa ame?"

Ya tambayeta yana matso da ita jikinsa,

"Abbu baka da zafine gashi kuma bukatarka bata da yawa, shine nace ko akwai matsala ne?" Tafada tareda rufe fuskarta,sai yanzu ya gano inda bayanin nata ya dosa, murmushi yayi,

"Eh akwai matsala amma ai akwai hanyoyin gyarawa, bari muje gida akwai wani littafi da wani shehun malami ya rubuta domin warware irin wannan matsalar, kinga kenan sai ki daura damarar kawo sauyi duk da nidai babu wata matsala, ahakan nan da kika ganni to wlh banida damuwa, amma tunda ke jarababbiya ce sai ingyara saboda ke" ya karasa maganar cikeda zolaya,

"Abbu nice jarababbiyar? Menayi na jaraba?" Ta tambayeshi,

"Binti wasa nake yi miki ai koni banida damuwa to yana da kyau naduba naga ke wanne irin yanayi kike ciki saboda gudun kada na cutar dake domin annabi Muhammad yace gamsar da juna yana daga cikin tushen aure, bai yiyuwa narinka barinki acikin damuwa nikuma alhalin na nishadantu domin a tsarin halitta ta bil'adama mace tafi namiji karfin sha'awa, sha'awar mace ta ninka ta namiji kinga kuwa indai hakane to mata da dama suna cikin wani hali domin suna fuskantar matsala ata fuskar rayuwar auratayya, amma dai bari muje gida"

Dan murmushi tayi batace komai ba har ya tashi motar suka harba titi, hannunta guda daya ya kamo ya rike, cikin gari suka shiga domin yana son ya dan yimata siyayyar kayan makulashe,

Tunda suka shiga ta wuraren da mutane suke suka fara ganin mabarata da almajirai jere atiti suna bara sai kace ba dare ba, wurin da yake ajiye kudi ya bude ya zaro yan ishirin ishirin ya dora mata kudin akan hannunta,

"Ungo binti rinka mika musu sadaka"

Kallonsa tayi tafara mika musu ta gilashin motar,

"Allah yabaka lada abbu"

"Amin amma ba sadakata bace takice binti domin yana da kyau ki yawaita yin sadaka"

Juyowa tayi ta kalleshi bayan ta gama mimmikawa almajiran sadakar,

"Saboda kasancewata bakuwa acikin addinin musulunci?"

Murmushi yayi ya lakuto hancinta "kar kiyi min fassarar abinda bashi nake nufiba, ai sadaka akan kowa abune mai kyau domin annabi ya kwadaitar damu cewa mu kare kanmu daga wuta koda da tsagin dabino ne ta hanyar bayar dashi sadaka, kuma bayan haka ma ai ku mata annabi ya ce ku yawaita bayar da sadaka acikin hadisin da aka karbo daga abdullahi dan mas'ud Allah ya kara masa yarda cewar manzon Allah (S. A. W) yace: _yaku taron mata, ku yawaita bayar da sadaka, domin mafi yawanku yan wutane, sai wata mata tace meyasa mukafi yawa awuta? Sai annabi yace saboda kuna yawaita la'anta sannan kuna kafurcewa abokan zamanku"_ jin haka sai matan dake wurin suka fara ciccire dan kunnayensu da awarwaronsu da abun hannunsu suna hadawa domin abayar da sadakar."

Cigaba da kallonsa bahijja tayi tana jin wani karfin imani yana shigarta har acikin ranta,

"Lallai abbu indai hakane kam amma mata muna cikin fargaba, duk da cewa adunkule kabani hadisin ba awarware ba, kace muna yawaita la'anta sannan kuma muna kafurcewa abokan zama, to kamar yaya?"

Hannunta ya ajiye akan cinyarshi yakarya kan motar suka dauki titin da zai sadasu da _Batool suya spot and soft drinks_,

"Ehh binti yawancin mata gaskiya kunada yawan maganganu marassa dadi, mafi yawa daga cikinku zaginku yafi salatinku yawa, ina nufin wata sai kasamu tayi zagi sau hamsin arana amma batayiwa annabi salati koda sau daya ba, abu kadan sai zagi idan yaro yayi ba daidai ba zagi idan tana yin wani abu ta samu kuskure zagi, idan yan wuta suka dauke zagi,komai zagi,a maimakon zagin nan gara kuna yin addu'a domin annabi yace _addu'a'uh huwa ibadahu, hakika addu'a ita ibada ce_, sannan kuma ku mata agaskiya kuna da manta alkairi dayawa daga cikinku bakwa godewa mazajenku, wata zaka samu mijinta kullum yana kyautata mata amma rana daya idan yayi mata kuskure sai kiji tace me kataba yimin? Ta manta duk alherin da yayi mata abaya, sannan wata kuma miji zai hanata abu amma bazata hanuba sai tayi to irin wadannan abubuwan da kuke ganinsu kamar kanana ne to sune suke kaiku wuta shiyasa annabi yace ku yawaita bayar da sadaka saboda ko lokacin da annabi yaje isra'i da mi'iraji da aka nuna masa wuta mata yagani cike aciki ana yi musu nau'o'in azaba iri iri alokacin hankalin annabi ya tashi sosai har yake tambayar mala'ika jibrilu wanne laifi wadannan matan suka yi ake yimusu irin wannan azaba haka"

Cinyarshi ta kankame wanda sanadiyyar hakan tasa jabir sakin sitiyarin motar dakyar ya iya saita kan motar ya taka burki domin sun karaso wurin da za suyi siyayyar,

"Binti ya kike nema ki sa muyi accident?"

Fuska ta shagwabe, "abbu na tsorata ne da abinda naji ka fada dan Allah ka sanar dani laifukan da matan nan suka aikata domin nima kar nashiga sahunsu, ka fadamin dan na kiyaye"

Hannuwansa yasa ya tallafi kumatunta yana kallon kwayar idonta wanda yake hango tsantsar kaunarshi da soyayyarshi aciki, hakika ya dade da sanin bahijja tana sonsa so nagaskiya kuma shima yanzu yana jinta acikin ranshi irin jin da bai taba ji ba akan wata mace,

"Insha Allahu binti bakya daga cikin irin wadannan matan amma kibari nadawo zan sanar dake irin laifin da wasu daga cikinsu suka yi har Allah yasakasu acikin azabarsa"

Asanyaye ta shafa hannunshi dake ajiye akan kumatumta, wani kiss ya ajiye mata akan goshinta ya saketa ya fita, bayanshi tabi da kallo tana faman murmushi yau dinnan yayi kyau over cikin farar t shirt din dake jikinsa mai dogon hannu da bakin trouser hadadde,

Fresh milk ya siyo musu roba biyu da gasasshiyar kaza sai kankana da tufa da manyan chocolate guda biyar, motar ya dawo ya zauna ya dorawa bahijja kayan akan cinyarta yana yi mata wani hatsabibin kallo wanda shi kadai yasan fassararshi,

Motar yayiwa key yafara tuki ahankali domin wanda yake tafiya ahankali ma zai iya zuwa ya wucesu,

Chocolate daya ta dauka ta bare ta gutsiri rabi ta mikawa jabir rabin ta hanyar kai masa ita kusa da bakinshi, juyowa yayi ya kalleta bayan ya bude dan karamin bakinshi,

"Wai abbu tayaya spoon yake shiga wannan bakin naka ne?" Ta tambayeshi tana saka masa chocolate din acikin bakinsa,

"Kina son in baki amsa? To ta yanda bakinki yake shiga cikin nawa"

Murmushi tayi tana jin wani farin ciki acikin zuciyarta,

"Kina jina binti? Acikin wutar jahannama annabi yace yaga wasu mataye suna kuka suna bakin ciki suna kira ba amsa musu ba sannan suna kaskantar da kai ba a gafarta musu ba, sai ya tambayi su wanene? Sai mala'ika jibrilu yace masa sune masu yin ado ba dan mazajensu ba, sannan yaga wasu mata akansu akwai wanduna na wuta awuyansu kuma akwai sarkoki da mari mari na wuta sukuma sune masu wulakanta mazajensu wacce dayarsu tana cewa mijinta mummuna mai wari mai mummunar fuska, sannan yaga wasu mata fuskokinsu sun kone harshensu sun zazzago akan kirjinsu sukuma sune masu cewa mazajensu kasakeni batare da wani dalili ba,

Sannan yaga wadansu mataye wanda aka ratayesu da gashinsu kwakwalwarsu tana tafarfasa kamar yadda tukwanen karfe suke tafasa akan wuta sune wadanda basa rufe gashinsu ga mazajen da ba muharramansu ba, sannan yaga wasu mataye an shafe jikinsu kuma yayi baki kamar kwalta sukuma sune masu runa gashin Kansu kuma suke sauya halittar Allah,
Chapter 47 · 0% Book details