Sashe 61
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Nagode abbu amma ni yanzu wanne kyau zanyi da wannan katon cikin" tafada fuskarta ashagwabe,
"Duk da haka kinyi kyau binti"
Hannunshi ta kama suka dauki hanyar falo, "abbu a asibiti ance na rinka exercise amma banda yin shara"
Akan kujera ta zauna shikuma yana daga tsaye yana kallonta,
"Kibar sharar to al'amin zai rinka yi miki sannan aikin ma ba kowanne zaki nayi ba"
"To abbu" tafada tana gyara zamanta akan kujerar, kallonta kawai jabir yake cikeda tausayawa domin ba karamin kumbura tayi ba kullum kunburin sake karuwa yake yi, yar kwallar tausayinta ce ta taru agefen idonshi amma bai bari ta gani ba,
"Binti bari naje salla nadawo ko? Idan nadawo za muje kiga gari"
Murna tafara yi tana dariya "yawwa abbu sai ka dawo"
Kissing din goshinta yayi ya juya ya fita domin zuwa masallaci.
Ana idar da sallar isha ya dawo gida, agurguje ya shiga dakin ummu ya tarar ta shirya masa abincin dare,kadan yaci, yana ci suna hira har ya kammala ya fita zuwa wurin bahijja,
A falo ya samesu itada al'amin ta baje tana cin tuwon biskin masarar da ummu al'amin ta kawo mata miyar taushe sai kamshin man shanune ke tashi,shi kuma al'amin yana kallon wa'azi atashar manara tv,
"Abbu kazo adaidai" tace dashi tana side hannunta,
Agabanta jabir ya tsugunna yana kallonta,
"Kuma meyasa ba zaki sude kwanon ba? Ki sudeshi binti sai ki samu cikakken lada,ko baki san haka annabi yake yi ba? Nana A'isha tace annabi ya kasance idan yaci abinci yana sude kwanon har sai kwanon ya zamana kamar an wankeshi"
Murmushi tayi ta dauki kwanon ta fara sudeshi itama "Allah ya saka da alkairi abbu"
Mikewa yayi yaje inda fridge yake ya dauko mata ruwa ya tsiyayo a cup ya dawo inda take ya mika mata, kwanon data gama cin abincin ya dauka yakai kitchen ya dawo ya mika mata hannunshi ta kama ya tayar da ita tsaye,
Kallo tabishi dashi yanda yayi kyau sosai cikin bakin trouser da doguwar farar jallabiya ga yar karamar hularta itama fara yasaka sai kace wani balarabe,
Waigawa tayi ta kalli al'amin wanda hankalinsa gaba daya ya tattara akan wa'azin da yake kallo,
"Al'amin bani hijab dina adaki pls"
Tashi al'amin yayi ya shiga dakinta kafin ya fito ta kalli jabir "abbu sunkuyo kaji" tafada ahankali, kasancewar yafita tsayi ba kadan ba ya sanyashi kawo fuskarshi saitin tata,
Kiss tayi masa akan lips dinshi, "abbu kayi kyau ne adaren nan"
Murmushi yayi ya riko hannunta, "hakama budurwa ta tace"
Kallonsa tayi ta dan bata rai "a ina taganka?"
"Gidansu naje" yace da ita yana kallon cikin idonta,
"Yayi kyau" tafada tana kokarin kwace hannunta, daidai lokacin al'amin ya fito hannunshi rikeda zunbulelen hijab dinta, karba tayi ta saka suka dunguma suka fita,
Ahankali suke tafiya akafa shida al'amin sun sakata a tsakiya yana rikeda hannunta amma fa tafiya kadan zata zauna ta huta da haka har suka yi yar tafiya mai nisa.
Basu suka dawo gida ba sai 9:30 nadare suna zuwa tsakar gida ta tsaya ta rike kunkuminta,
"Wash abbu bayana"
Daukarta jabir yayi zuwa part dinta al'amin yana tsaye yana kallonsu yana dariya,
"Abbu da anty ashe kun jima da shiryawa" yafada aranshi tareda juyawa ya nufi part din ummunshi.
Suna shiga jabir bai direta ako inaba sai a dakinta akan gadonta,
"Abbu yunwa bani abinci, amma banda abu mai madara, akwai guntun tuwona a cikin kitchen"
Kitchen din yaje ya dauko mata tuwon ya kawo mata yabata taci yakaita tayi wanka ta fito ta saka doguwar rigar baccinta ta kwanta, kasancewar ta gaji mintuna kadan bacci yayi awon gaba da ita, lullubeta jabir yayi yaje fuskarta yayiwa bakinta kiss yafita bayan ya kashe mata wutar dakin.
Washe gari tunda misalin karge 4 tafara shirye shiryen karbar jabir domin yace yau itace dashi dole babu yadda ta iya haka ta daure ta fada kitchen tayi masa girki na alfarma tayi wanka ta shirya ta danyi make up sama sama tasaka doguwar riga ta atamfa pink colour,
Ganin tanata zaune shiru gashi babu al'amin yau yatafi wurin jaddi wato kakanshi kamar yadda yake kiran Malam din, kayan jabir ta hado tafita corridor dinta tafara wankewa, kasancewar harda su jeans ya sa duk ta jijjike gashi ta jijjika corridor din ma,
Tana tsaka da shanyar kayan jabir ya shigo,
"Binti me kike yi?"
"Abbu wanki nayi maka na kayanka a asibiti ne akace idan muna yin aiki haihuwa zata fi zuwa mana da sauki"
Hannunta jabir ya kama zuwa cikin falonta "kiga yanda kika jika jikinki, wannan kayan ai sunyi miki nauyi binti, jeki ki sauya kayan jikinki kin ga duk sun jike, ai ba sai lallai wanki ba, ko hidima dani ma zai kawo miki nakuda mai sauki"
Kafada ta make "naki wayon"
Juyawa tayi zuwa cikin dakinta shikuma ya koma corridor din domin gyarawa gashi kayanma duk basu wankuba kasancewar sunyi nauyi da yawa.
Corridor din ya gyara tsaf sannan yabita dakinta, lokacin da ya shiga tana daure da zani tana kokarin saka riga, gabanta ya karasa yakai hannunshi ya dafa cikinta yana murmushi,
"Babyn abbu yau ba a naushin ne?" Ya fada cikeda tsokana yana kallon idanuwan bahijja,
"Ai wlhi abbu shiyasa manzon Allah yace abi uwa kafin yace abi uba saboda mata sunfi maza shan wahala awurin hidimar yara"
Rigar ya karba ya saka mata yana cewa "babu komai binti sakamakon ku yana wurin Allah"
Gefen gado taje ta zauna bayan ya gama saka mata rigar, kusa da ita ya matsa ya dan duka ya dafe gwiwowinsa yana kallonta,
"Muje ki rakani nayi wanka binti"
Mikewa tayi dakyar "nidai abbu shiyasa nace nayafe kace kai baka yafeba, nidai gaskiya...!"
Ta bayanta ya rungumeta, "haba binti bakya son Allah ya baki lada ne?"
"Ina so" tafada cikin shagwaba,
"Yawwa binti ko kefa, maza muje ki rakani"
Binshi tayi amma dakyar take iya tafiya da haka har suka shiga sashen shi, toilet ta wuce kai tsaye ta hada masa ruwa tafito ta iskeshi daga shi sai gajeren wando yana kallon sumar kanshi a mirror,
"Abbu kaima fa dan gayune kullum kai kenan cikin kallon mudubi kamar wata mace"
Murmushi yayi ya juyo yana kallonta,
"Annabi ma ai dan gayune binti shiyasa indai mutum da shi yake koyi to ya kamata shima ya zama dan gayu ba kazami ba"
Hannunshi ta kama "hakane Malam"
"Oh yau kuma sunan da kika bani kenan binti na"
Tare suka shiga toilet din ta zage ta wankeshi tas suka fito tana rikeda dan karamin towel tana tsane masa jikinshi,
Mai ta shafa masa ta taje masa sumar kanshi da sajenshi da gemunshi mai mutukar kyau,
Kayan da zai saka ta ciro masa bayan ta feshe shi da turarruka masu dadi,
Falonta suka koma taje ta hada masa abincin data girka masa mai mutukar dadi, suna nan tare har lokacin salla yayi sai sannan yafita zuwa masallaci.
Rayuwa mai dadi suka ci gaba da gudanarwa har cikin bahijja ya shiga wata na tara, tunda watan haihuwarta ya kama ta dage da addu'a kan Allah ya sauketa lafiya shima jabir ba abarshi abaya ba kullum cikin yin sadaka yake da addu'o'i domin Allah ya sauki bahijjansa lafiya.
Ranar laraba da daddare haihuwa tace salamu alaikum, bahijja tana tsaka da bacci taji ciwo ya turnuketa dolenta ta tashi babu shiri, jabir dake kwance kusa da ita tafara tashi,
"Abbu, abbu bayana, abbu cikina,abbu marata..!"
Tashi jabir yayi yai maza ya taimaka mata suka fita, ganin tana tafiya dakyar ya sanyashi daukarta ya saka acikin mota, harda dan gudunshi yaje ya taso ummu al'amin,
Lokacin da suka isa asibitin karfe 3:30 nadare nan aka karbi bahijja aka nufi maternity da ita,
Tunda aka shiga da ita jabir yarasa nutsuwarsa hankalinsa gaba daya ya gama tashi, ba karamin wahala bahijja take sha ba amma haihuwa shiru tun ana sa rai har aka fara jiran tsammani,
Har asuba tayi bahijja bata haihu ba gashi likitocin sunce zata iya haihuwa da kanta, gaba daya jabir ya shiga damuwa kallo daya zaka yi masa kasan baya cikin kwanciyar hankali,
Har aka wuni haihuwa shiru, jabir na zaune bai san lokacin da kwalla ta tarar masa ba a idanuwanshi, tausayin bahijja yake ji sosai, har yamma tayi babu haihuwa sai bayan sallar isha sannan Allah yayi ikonshi bahijja ta haifo katuwar jaririyarta jajur da ita mai mutukar kama da jabir, kasancewar jininta ya hau sosai ya sa aka yi mata allurar bacci domin ta samu hutu,
Su jabir suna zaune shida ummu al'amin aka sanar musu da cewar ta haihu, hamdala jabir ya shiga yi amma acan karkashin zuciyarshi kuma wani irin tausayin bahijja yakeji marar misaltuwa,
Suna nan suna jira jabir sai waya yake yana sanarwa da yan uwa haihuwar aka fito da bahijja zuwa postnatal lokacin misalin karfe 11 daidai nadare,
Ummu al'amin ce ta fara shiga dakin ta yiwa bahijja sannu ta dauki jaririyar tana kallonta kamarsu daya sak da al'amin dinta lokacin da ta haifeshi lallai jabir jininsa yanada karfi sosai ta raya aranta,
Ajiye jaririyar tayi ta zubawa bahijja abinci tafara ci domin shi jabir yana can wurin hidimar biyan kudaden da asibitin take bukata awurinsu,
Fita ummu tayi domin tafiya gida saboda taji jabir yace yayar bahijja zata zo lokacin,
Bata jima da tafiya ba jabir ya shiga dakin fuskarsa dauke da farin ciki mai yawan gaske, kusa da bahijja yaje ya zauna yana kallonta cikeda tausayawa,hannunta ya kamo ya rike cikin nashi,
"Sannu _*BAHIJJA*_ hakika nasan kinsha wahala, Allah ubangiji yasa sanadiyyar wannan wahalar da kika shiga yayi miki sakamako da gidan aljanna"
Kallonsa bahijja tayi domin tunda take dashi bata taba jin ya kira sunanta ba sai yau gashi ya iya fadin sunan domin har wani jan sunan yayi,
"Amin abbu" ta amsa mishi ahankali,
"Yanzu inane yake miki ciwo?"
Girgiza masa kai tayi "abbu ga babyn baka dauketa ba"
Sai alokacin ya tashi yaje inda babyn take tasha kayan sanyi pink colour masu digon fari ajiki, an saka mata hula da safa duk kalar kayan, yarinyar ya zubawa ido yana murmushi sai fito da harshe take tana lasar lips dinta,
"Duk da haka kinyi kyau binti"
Hannunshi ta kama suka dauki hanyar falo, "abbu a asibiti ance na rinka exercise amma banda yin shara"
Akan kujera ta zauna shikuma yana daga tsaye yana kallonta,
"Kibar sharar to al'amin zai rinka yi miki sannan aikin ma ba kowanne zaki nayi ba"
"To abbu" tafada tana gyara zamanta akan kujerar, kallonta kawai jabir yake cikeda tausayawa domin ba karamin kumbura tayi ba kullum kunburin sake karuwa yake yi, yar kwallar tausayinta ce ta taru agefen idonshi amma bai bari ta gani ba,
"Binti bari naje salla nadawo ko? Idan nadawo za muje kiga gari"
Murna tafara yi tana dariya "yawwa abbu sai ka dawo"
Kissing din goshinta yayi ya juya ya fita domin zuwa masallaci.
Ana idar da sallar isha ya dawo gida, agurguje ya shiga dakin ummu ya tarar ta shirya masa abincin dare,kadan yaci, yana ci suna hira har ya kammala ya fita zuwa wurin bahijja,
A falo ya samesu itada al'amin ta baje tana cin tuwon biskin masarar da ummu al'amin ta kawo mata miyar taushe sai kamshin man shanune ke tashi,shi kuma al'amin yana kallon wa'azi atashar manara tv,
"Abbu kazo adaidai" tace dashi tana side hannunta,
Agabanta jabir ya tsugunna yana kallonta,
"Kuma meyasa ba zaki sude kwanon ba? Ki sudeshi binti sai ki samu cikakken lada,ko baki san haka annabi yake yi ba? Nana A'isha tace annabi ya kasance idan yaci abinci yana sude kwanon har sai kwanon ya zamana kamar an wankeshi"
Murmushi tayi ta dauki kwanon ta fara sudeshi itama "Allah ya saka da alkairi abbu"
Mikewa yayi yaje inda fridge yake ya dauko mata ruwa ya tsiyayo a cup ya dawo inda take ya mika mata, kwanon data gama cin abincin ya dauka yakai kitchen ya dawo ya mika mata hannunshi ta kama ya tayar da ita tsaye,
Kallo tabishi dashi yanda yayi kyau sosai cikin bakin trouser da doguwar farar jallabiya ga yar karamar hularta itama fara yasaka sai kace wani balarabe,
Waigawa tayi ta kalli al'amin wanda hankalinsa gaba daya ya tattara akan wa'azin da yake kallo,
"Al'amin bani hijab dina adaki pls"
Tashi al'amin yayi ya shiga dakinta kafin ya fito ta kalli jabir "abbu sunkuyo kaji" tafada ahankali, kasancewar yafita tsayi ba kadan ba ya sanyashi kawo fuskarshi saitin tata,
Kiss tayi masa akan lips dinshi, "abbu kayi kyau ne adaren nan"
Murmushi yayi ya riko hannunta, "hakama budurwa ta tace"
Kallonsa tayi ta dan bata rai "a ina taganka?"
"Gidansu naje" yace da ita yana kallon cikin idonta,
"Yayi kyau" tafada tana kokarin kwace hannunta, daidai lokacin al'amin ya fito hannunshi rikeda zunbulelen hijab dinta, karba tayi ta saka suka dunguma suka fita,
Ahankali suke tafiya akafa shida al'amin sun sakata a tsakiya yana rikeda hannunta amma fa tafiya kadan zata zauna ta huta da haka har suka yi yar tafiya mai nisa.
Basu suka dawo gida ba sai 9:30 nadare suna zuwa tsakar gida ta tsaya ta rike kunkuminta,
"Wash abbu bayana"
Daukarta jabir yayi zuwa part dinta al'amin yana tsaye yana kallonsu yana dariya,
"Abbu da anty ashe kun jima da shiryawa" yafada aranshi tareda juyawa ya nufi part din ummunshi.
Suna shiga jabir bai direta ako inaba sai a dakinta akan gadonta,
"Abbu yunwa bani abinci, amma banda abu mai madara, akwai guntun tuwona a cikin kitchen"
Kitchen din yaje ya dauko mata tuwon ya kawo mata yabata taci yakaita tayi wanka ta fito ta saka doguwar rigar baccinta ta kwanta, kasancewar ta gaji mintuna kadan bacci yayi awon gaba da ita, lullubeta jabir yayi yaje fuskarta yayiwa bakinta kiss yafita bayan ya kashe mata wutar dakin.
Washe gari tunda misalin karge 4 tafara shirye shiryen karbar jabir domin yace yau itace dashi dole babu yadda ta iya haka ta daure ta fada kitchen tayi masa girki na alfarma tayi wanka ta shirya ta danyi make up sama sama tasaka doguwar riga ta atamfa pink colour,
Ganin tanata zaune shiru gashi babu al'amin yau yatafi wurin jaddi wato kakanshi kamar yadda yake kiran Malam din, kayan jabir ta hado tafita corridor dinta tafara wankewa, kasancewar harda su jeans ya sa duk ta jijjike gashi ta jijjika corridor din ma,
Tana tsaka da shanyar kayan jabir ya shigo,
"Binti me kike yi?"
"Abbu wanki nayi maka na kayanka a asibiti ne akace idan muna yin aiki haihuwa zata fi zuwa mana da sauki"
Hannunta jabir ya kama zuwa cikin falonta "kiga yanda kika jika jikinki, wannan kayan ai sunyi miki nauyi binti, jeki ki sauya kayan jikinki kin ga duk sun jike, ai ba sai lallai wanki ba, ko hidima dani ma zai kawo miki nakuda mai sauki"
Kafada ta make "naki wayon"
Juyawa tayi zuwa cikin dakinta shikuma ya koma corridor din domin gyarawa gashi kayanma duk basu wankuba kasancewar sunyi nauyi da yawa.
Corridor din ya gyara tsaf sannan yabita dakinta, lokacin da ya shiga tana daure da zani tana kokarin saka riga, gabanta ya karasa yakai hannunshi ya dafa cikinta yana murmushi,
"Babyn abbu yau ba a naushin ne?" Ya fada cikeda tsokana yana kallon idanuwan bahijja,
"Ai wlhi abbu shiyasa manzon Allah yace abi uwa kafin yace abi uba saboda mata sunfi maza shan wahala awurin hidimar yara"
Rigar ya karba ya saka mata yana cewa "babu komai binti sakamakon ku yana wurin Allah"
Gefen gado taje ta zauna bayan ya gama saka mata rigar, kusa da ita ya matsa ya dan duka ya dafe gwiwowinsa yana kallonta,
"Muje ki rakani nayi wanka binti"
Mikewa tayi dakyar "nidai abbu shiyasa nace nayafe kace kai baka yafeba, nidai gaskiya...!"
Ta bayanta ya rungumeta, "haba binti bakya son Allah ya baki lada ne?"
"Ina so" tafada cikin shagwaba,
"Yawwa binti ko kefa, maza muje ki rakani"
Binshi tayi amma dakyar take iya tafiya da haka har suka shiga sashen shi, toilet ta wuce kai tsaye ta hada masa ruwa tafito ta iskeshi daga shi sai gajeren wando yana kallon sumar kanshi a mirror,
"Abbu kaima fa dan gayune kullum kai kenan cikin kallon mudubi kamar wata mace"
Murmushi yayi ya juyo yana kallonta,
"Annabi ma ai dan gayune binti shiyasa indai mutum da shi yake koyi to ya kamata shima ya zama dan gayu ba kazami ba"
Hannunshi ta kama "hakane Malam"
"Oh yau kuma sunan da kika bani kenan binti na"
Tare suka shiga toilet din ta zage ta wankeshi tas suka fito tana rikeda dan karamin towel tana tsane masa jikinshi,
Mai ta shafa masa ta taje masa sumar kanshi da sajenshi da gemunshi mai mutukar kyau,
Kayan da zai saka ta ciro masa bayan ta feshe shi da turarruka masu dadi,
Falonta suka koma taje ta hada masa abincin data girka masa mai mutukar dadi, suna nan tare har lokacin salla yayi sai sannan yafita zuwa masallaci.
Rayuwa mai dadi suka ci gaba da gudanarwa har cikin bahijja ya shiga wata na tara, tunda watan haihuwarta ya kama ta dage da addu'a kan Allah ya sauketa lafiya shima jabir ba abarshi abaya ba kullum cikin yin sadaka yake da addu'o'i domin Allah ya sauki bahijjansa lafiya.
Ranar laraba da daddare haihuwa tace salamu alaikum, bahijja tana tsaka da bacci taji ciwo ya turnuketa dolenta ta tashi babu shiri, jabir dake kwance kusa da ita tafara tashi,
"Abbu, abbu bayana, abbu cikina,abbu marata..!"
Tashi jabir yayi yai maza ya taimaka mata suka fita, ganin tana tafiya dakyar ya sanyashi daukarta ya saka acikin mota, harda dan gudunshi yaje ya taso ummu al'amin,
Lokacin da suka isa asibitin karfe 3:30 nadare nan aka karbi bahijja aka nufi maternity da ita,
Tunda aka shiga da ita jabir yarasa nutsuwarsa hankalinsa gaba daya ya gama tashi, ba karamin wahala bahijja take sha ba amma haihuwa shiru tun ana sa rai har aka fara jiran tsammani,
Har asuba tayi bahijja bata haihu ba gashi likitocin sunce zata iya haihuwa da kanta, gaba daya jabir ya shiga damuwa kallo daya zaka yi masa kasan baya cikin kwanciyar hankali,
Har aka wuni haihuwa shiru, jabir na zaune bai san lokacin da kwalla ta tarar masa ba a idanuwanshi, tausayin bahijja yake ji sosai, har yamma tayi babu haihuwa sai bayan sallar isha sannan Allah yayi ikonshi bahijja ta haifo katuwar jaririyarta jajur da ita mai mutukar kama da jabir, kasancewar jininta ya hau sosai ya sa aka yi mata allurar bacci domin ta samu hutu,
Su jabir suna zaune shida ummu al'amin aka sanar musu da cewar ta haihu, hamdala jabir ya shiga yi amma acan karkashin zuciyarshi kuma wani irin tausayin bahijja yakeji marar misaltuwa,
Suna nan suna jira jabir sai waya yake yana sanarwa da yan uwa haihuwar aka fito da bahijja zuwa postnatal lokacin misalin karfe 11 daidai nadare,
Ummu al'amin ce ta fara shiga dakin ta yiwa bahijja sannu ta dauki jaririyar tana kallonta kamarsu daya sak da al'amin dinta lokacin da ta haifeshi lallai jabir jininsa yanada karfi sosai ta raya aranta,
Ajiye jaririyar tayi ta zubawa bahijja abinci tafara ci domin shi jabir yana can wurin hidimar biyan kudaden da asibitin take bukata awurinsu,
Fita ummu tayi domin tafiya gida saboda taji jabir yace yayar bahijja zata zo lokacin,
Bata jima da tafiya ba jabir ya shiga dakin fuskarsa dauke da farin ciki mai yawan gaske, kusa da bahijja yaje ya zauna yana kallonta cikeda tausayawa,hannunta ya kamo ya rike cikin nashi,
"Sannu _*BAHIJJA*_ hakika nasan kinsha wahala, Allah ubangiji yasa sanadiyyar wannan wahalar da kika shiga yayi miki sakamako da gidan aljanna"
Kallonsa bahijja tayi domin tunda take dashi bata taba jin ya kira sunanta ba sai yau gashi ya iya fadin sunan domin har wani jan sunan yayi,
"Amin abbu" ta amsa mishi ahankali,
"Yanzu inane yake miki ciwo?"
Girgiza masa kai tayi "abbu ga babyn baka dauketa ba"
Sai alokacin ya tashi yaje inda babyn take tasha kayan sanyi pink colour masu digon fari ajiki, an saka mata hula da safa duk kalar kayan, yarinyar ya zubawa ido yana murmushi sai fito da harshe take tana lasar lips dinta,