Sashe 31
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
To amma sai _Barnaby_ wanda akafi sani da Barnabas sai ya nuna cewa akarbeshi tunda ya tuba kasancewar ko Allah ma yana karbar laifi idan aka tuba, amma matasan tafiyar irinsu _Mathew_ sam basu amintu da tuban bulus ba,
Haka suka ci gaba da tafiya _Barnabas_ ya aminta da bulus amma _Mathew_ bai aminta ba ana nan ba adade ba sai bulus yace yayi mafarki yaga annabi Isah (AS) yace ya rubuta injila (Bible) cikin jeren almajiran annabi Isah masu rubuta injila,
Sai aka ga gashi ya rubuta injila amma tana dauke da cewa Isah dan Allah ne, Allah yana da d'a, maryama Allah ce, mala'ika jibrilu Allah ne, sai aka samu wadannan akidodi sun fantsama cikin mutane wasu har sunyi na'am dasu, saboda yayi da'awar cewa annabi Isah ne ya bashi umarnin ya rubuta,
Koda maganar ta fito sai mabiyan annabi Isah sukace basu yarda ba amma ya rigada yayi musu raraka dayawa domin jama'a da dama sun yarda da abinda ya rubuta,
Koda mabiyan annabi Isah sukace basu yarda ba sai magoyan bayan bulus sukace su sun aminta tunda mafarki yayi kuma acikin addinin annabi Isah akwai halarcin kayi mafarki da shi ya fada maka abu ka rubutashi kabayar akarba ba tare da anyi bincike ba,
Dan haka shima dole akarbi abinda ya rubuta, Ashe dan kwangila ne, kwangila ya karbo daga wurin yan uwansa yahudawa ciki harda Sarkin wata kasa (kwantastaniya), wato kasar turkiya wanda shi wannan sarkin ya kasance bamaguje ne mai bautar Alloli dayawa sakamakon haka suka sha alwashin sai sun bata addinin annabi Isah, shiyasa suka dauki kwangila suka bashi, da ya hada wannan rikici yaga komai ya rikice sai yace to mai zai hana adauki wannan case din akaiwa wani wanda shi abinda yake bautawa dabanne da nasu, sai sukace kamar wa? Sai yace kamar sarki kotasten,
Cikin rashin sani sai suka amince, koda suka je suka fada masa sai ya karbe dukkan injilar datake hannunsu yace za asamu babban abu azuba aciki asamu kyalle arufe da daddare, idan gari yawaye duk wadda aka samu asama sauran na lullube to itace ta gaskiya dukkaninsu sukace sun yarda,
Koda aka wayi gari sai aka ga wannan injilar mai cewa Allah yanada da, maryamu Allahce, jibrilu Allah ne alloli ukune sai aka tarar itace asama, _Mathew da Barnabas_ da suka ga haka sai sukace to lallai yaune ranar farko na lalacewar addinin da annabi Isah yazo dashi,dan haka bazasu tsaya suga wannan barna da idanunsu ba, sai suka kama hanya domin yin hijira, Adaji akaga gawawwakinsu an daddaba musu wuka an kashesu"
Daga kanta tayi tana kallonsa "ehem ina jinka, duk nasan wannan labarin karshen nake son ji"
Cigaba yayi da cewa "ba asan waye ya kashesu ba amma ana tunanin su bulus ne da sarki kotastan ko kuma wasu yan ta'adda wadanda ba a sansu ba, sai aka koma cikin gari aka hallakar da duk injilolin in banda wadda Allah ya tseratar kwaya daya wacce yanzu akafi sani da _the gospel of Barnabas_, har yanzu tana nan ayadda take da asalin rubutun hannunta tana nan a _Barnabas square_ akasar _Italy_ an kewayeta acikin wani gilashi,yawanci Christians yanzu kuna inkarinta saboda sunayen annabi Muhammad ya bayyana karara acikinta, amma kuma itace injila mafi kusantar gaskiya da sauran injilolin da suke hannunku ayanzu,
To kinga kenan wannan shine asalin addinin kiristanci da kike bi wanda Barnabas ya tsarawa mabiyan annabi Isah akarshen zamani, har suka dauki cross suna ratayawa awuyansu wanda har yahudawa suka fara yi musu ba'a suna kiransu da chritian wato masu bautar wanda aka gicciye, to da zamani yayi tsawo sai su da kansu suka yarda suka amsa sunansu na Christians, kinga kenan idan kin fahimci abinda nafada miki wannan addinin da kike bi ayanzu ba shine asalin addinin da annabi Isah yazo dashi ba, wani abune ake bi daga cikin tsarin sarki kotastan bamaguje da bulus wanda ya shigo domin ya lalata addinin,wannan shine asalin addinin kiristanci, shin idan baki san wannan ba baza kiyi mamaki ba kiji Allah ya tsinewa bani isra'ila ta harshen annabi Isah da annabi dawud ba? Alhalin shima annabi Isah ba'isra'iliye ne,
Shi kansa bani isra'ila ne amma meyasa Allah ya tsine musu? Allah ya tsinewa wadannan masu sauya littafin Allahn ne Wanda ya turo annabi Isah dashi,
Wannan tarihin nasan kin sanshi domin haka yazo acikin Bible kuma mutane da dama sunyi bincike sun ganoshi har sunyi rubutu akansa misali Alhaji _Adelege_ ya rubuta littafi mai suna _historical Jesus_ wato Jesus nagaskiya da kuma almasihu wanda aka kirkira domin abata addinin, acikin wannan littafin akwai tarihi nagaskiya na injila wanda yasha banban da tarihin wannan littafin ayau"
Hannuwanshi ta sake rikewa cikin nata tana kallon kyakkywar fuskarshi,hakika yau ta yarda cewar jabir mutum ne mai ilimin gaske wanda ba iya na addininsa kadai ba har na addininta ya hada,
"Abu dukkan abubuwan da kafada nasan gaskiya ne sai dai akwai daga cikin labaran da ka fada min wanda mu ba haka yazo mana acikin Bible ba"
Manyan idanuwanshi ya zuba mata yana wani salihin murmushi,
"Shiyasa nace miki tun farko ancanja littafin ne kuma labaran da suka zo acikin Bible suna wuce iyakane, suna zarce inda ya kamata su tsaya shiyasa acikin alqur'ani mai girma ubangiji ya kira yahudawa da wadanda suka sauya littafinsa, Allah yace "'Gwalalon azaba ya tabbata ga wadanda suka yi rubutu da hannunsu sannan suke cewa wannan rubutun daga Allah yake saboda wasu yan kudi kadan wanda zasu samu ,
Azaba ta tabbata agaresu gameda abinda suke rubutawa, azaba ta tabbata akansu gameda kudin da suke samu"' _(alqur'an, chapter 3)_,
Kinga kenan shi kansa Bible din littafine wanda aka canjashi tunda ansaukar da alqur'ani ne abayan an saukar da injila (Bible) amma gaba daya acikin ayoyin alqur'ani mai girma duk inda Allah ya tashi yin magana akan injila yana cewa an canja littafin, Allah yayi mana bayanin hakan dalla dalla acikin suratul Al'imran surah ta uku daga farkon aya har zuwa ta karshe"
"Hakane abbu,yanzu nagane jawabanka gaba daya"
"Tunda kin gane to ki kwanta kiyi bacci saboda dare yayi sosai"
"To kar ka sake yin wani kukan pls" tafada cikin shagwaba tana zare hannuwanta daga cikin nashi, tashi yayi ya shiga bathroom yayi alwala ya fito yana kallon agogon dake makale a bangon cikin dakin, karfe 2:30 nadare, gafen gadon yaje ya kwanta yana kokarin jan bargo domin rufe jikinshi,
"Abbu yau baka yimin addu'a ba" ya jiyo muryar goodness abayanshi tana fada, juyawa yayi yafara karanta mata addu'a, sai da yagama sannan yayi wa kansa ya shafe jikinsa yagyara kwanciyarsa,
Goodness najinshi tana kwance tana kallonsa ta kasa bacci tunani ne kala kala ke zagaya kwakwalwarta, ita dai tasan acikin Bible akwai abubuwan da suka zo nagaskiya amma basa aiki dasu misali, abangaren hukunce hukunce akwai hukuncin saka hijabi amma kuma basa sakawa, sannan akwai hukuncin alwala wato an koyar dasu yanda zasu yi alwala itama basa yi, akwai hukuncin sata idan mutum yayi nanma ba ayi, kuma ta taba ganin wani hoto da aka zana nana maryam mahaifiyar annabi Isah da hijabi ajikinta taga an zanata ba azanata da siffa irin wacce su suke da ita ayanzu ba, gashi ba salla suke yiba amma idan sunje masallacin Jerusalem aikin hajjinsu dolene sai mutum yayi alwala yayi salla raka'a biyu, kai anya kuwa babu wani boyayyen al'amari acikin wannan lamarin?
Juyi tayi takoma rigingine tana kallon sama acikin duhun dakin, tafi minti 30 tana tunane tunane wanda ta kasa gane kansa daga karshe taja jikinta ahankali taje ta kwanta ajikin jabir tana mai kudurin idan gari ya waye akwai tambayar da zata yi masa, hannunshi ta lalubo ta rike cikin nata tana matsawa ahankali, duk jabir najinta domin ba bacci yake yiba idonshi biyu kawai yayi mata shiru ne.
Yana jinta ta fara fitar da numfashi ahankali alamun tayi bacci, hannuwanshi yasaka ya zageyata ya rungumeta acikin jikinsa, hannunshi guda daya yasa ya shafo tulin gashin kantin dake kanta wanda yake himili guda shi dai har yanzu bazai iya cewa ga yanayin gashinta ba saboda tun zuwanta gidan kullum cikin attach take idan ba kitso ba to kalba,
Yanata yan tunane tunane har baccin shima yayi nasarar awon gaba dashi.
Kamar kullum washe gari da safe bayan ta kammala shirya komai tayi wanka da ruwan data zuba turaren almiski aciki kasancewar ita bata San amfaninsa ba,
Kwalliya tayi tasaka English wears wanda jabir ya siyo mata lokacin da yaje _madinahtul munawwara_ rigar bakace mai adon duwatsu yayinda skirt din kuma blue colour ce mai santsi, bakar hula ta saka ta sake shafe jikinta da turaren muski da sauran turaruka masu dadin kamshi,
Breakfast din jabir ta dauka ta nufi part dinsa, tana shiga yana fitowa daga cikin bedroom dinsa cikin hadadden farin danyen boyel dinkin riga da wando da kuma babbar riga, ba karamin kyau yau dinnan yayi ba dan ji take inama tana da camera da ta haska shi,
"Good morning abbu" ta fada tana karkace kanta gamida langabar dashi,
"Morning, kar ki ajiye min anan miko min shi nan" yafada lokacin da ya ke zama kan kujerar dake cikin falon, fasa dorawa tayi akan dining table din ta dauko ta kawo masa ta dora akan center table din gaban kujerar da yake zaune,
Tea ta tsugunna ta soma hada masa, kasa kasa yake kallonta gaba daya kamshinta ya gama cika masa hanci ji yake yasan kamshin tiraren amma ya kasa gane wanne irine,haka itama kamshinsa gaba daya ya cika mata hancinta domin numfashinta har wani sauya launin fitarsa yayi,
"Gashi abbu" tafada tana dora masa bisa kan table din
"Yawwa nagode ya fada ahankali"
Zama tayi agefensa tana kallon yanda yake shan tea din cikin sanyinshi ahankali ahankali kamar wani marar lafiya,
"Abbu inada tambaya,Acikin bible an fada mana cewar Jesus zaiyi ceto shida ruhu (haske),Ku wa akace muku zaiyi ceto acikin littafinku?"
Cup din hannunsa ya ajiye ya dan kalleta
Haka suka ci gaba da tafiya _Barnabas_ ya aminta da bulus amma _Mathew_ bai aminta ba ana nan ba adade ba sai bulus yace yayi mafarki yaga annabi Isah (AS) yace ya rubuta injila (Bible) cikin jeren almajiran annabi Isah masu rubuta injila,
Sai aka ga gashi ya rubuta injila amma tana dauke da cewa Isah dan Allah ne, Allah yana da d'a, maryama Allah ce, mala'ika jibrilu Allah ne, sai aka samu wadannan akidodi sun fantsama cikin mutane wasu har sunyi na'am dasu, saboda yayi da'awar cewa annabi Isah ne ya bashi umarnin ya rubuta,
Koda maganar ta fito sai mabiyan annabi Isah sukace basu yarda ba amma ya rigada yayi musu raraka dayawa domin jama'a da dama sun yarda da abinda ya rubuta,
Koda mabiyan annabi Isah sukace basu yarda ba sai magoyan bayan bulus sukace su sun aminta tunda mafarki yayi kuma acikin addinin annabi Isah akwai halarcin kayi mafarki da shi ya fada maka abu ka rubutashi kabayar akarba ba tare da anyi bincike ba,
Dan haka shima dole akarbi abinda ya rubuta, Ashe dan kwangila ne, kwangila ya karbo daga wurin yan uwansa yahudawa ciki harda Sarkin wata kasa (kwantastaniya), wato kasar turkiya wanda shi wannan sarkin ya kasance bamaguje ne mai bautar Alloli dayawa sakamakon haka suka sha alwashin sai sun bata addinin annabi Isah, shiyasa suka dauki kwangila suka bashi, da ya hada wannan rikici yaga komai ya rikice sai yace to mai zai hana adauki wannan case din akaiwa wani wanda shi abinda yake bautawa dabanne da nasu, sai sukace kamar wa? Sai yace kamar sarki kotasten,
Cikin rashin sani sai suka amince, koda suka je suka fada masa sai ya karbe dukkan injilar datake hannunsu yace za asamu babban abu azuba aciki asamu kyalle arufe da daddare, idan gari yawaye duk wadda aka samu asama sauran na lullube to itace ta gaskiya dukkaninsu sukace sun yarda,
Koda aka wayi gari sai aka ga wannan injilar mai cewa Allah yanada da, maryamu Allahce, jibrilu Allah ne alloli ukune sai aka tarar itace asama, _Mathew da Barnabas_ da suka ga haka sai sukace to lallai yaune ranar farko na lalacewar addinin da annabi Isah yazo dashi,dan haka bazasu tsaya suga wannan barna da idanunsu ba, sai suka kama hanya domin yin hijira, Adaji akaga gawawwakinsu an daddaba musu wuka an kashesu"
Daga kanta tayi tana kallonsa "ehem ina jinka, duk nasan wannan labarin karshen nake son ji"
Cigaba yayi da cewa "ba asan waye ya kashesu ba amma ana tunanin su bulus ne da sarki kotastan ko kuma wasu yan ta'adda wadanda ba a sansu ba, sai aka koma cikin gari aka hallakar da duk injilolin in banda wadda Allah ya tseratar kwaya daya wacce yanzu akafi sani da _the gospel of Barnabas_, har yanzu tana nan ayadda take da asalin rubutun hannunta tana nan a _Barnabas square_ akasar _Italy_ an kewayeta acikin wani gilashi,yawanci Christians yanzu kuna inkarinta saboda sunayen annabi Muhammad ya bayyana karara acikinta, amma kuma itace injila mafi kusantar gaskiya da sauran injilolin da suke hannunku ayanzu,
To kinga kenan wannan shine asalin addinin kiristanci da kike bi wanda Barnabas ya tsarawa mabiyan annabi Isah akarshen zamani, har suka dauki cross suna ratayawa awuyansu wanda har yahudawa suka fara yi musu ba'a suna kiransu da chritian wato masu bautar wanda aka gicciye, to da zamani yayi tsawo sai su da kansu suka yarda suka amsa sunansu na Christians, kinga kenan idan kin fahimci abinda nafada miki wannan addinin da kike bi ayanzu ba shine asalin addinin da annabi Isah yazo dashi ba, wani abune ake bi daga cikin tsarin sarki kotastan bamaguje da bulus wanda ya shigo domin ya lalata addinin,wannan shine asalin addinin kiristanci, shin idan baki san wannan ba baza kiyi mamaki ba kiji Allah ya tsinewa bani isra'ila ta harshen annabi Isah da annabi dawud ba? Alhalin shima annabi Isah ba'isra'iliye ne,
Shi kansa bani isra'ila ne amma meyasa Allah ya tsine musu? Allah ya tsinewa wadannan masu sauya littafin Allahn ne Wanda ya turo annabi Isah dashi,
Wannan tarihin nasan kin sanshi domin haka yazo acikin Bible kuma mutane da dama sunyi bincike sun ganoshi har sunyi rubutu akansa misali Alhaji _Adelege_ ya rubuta littafi mai suna _historical Jesus_ wato Jesus nagaskiya da kuma almasihu wanda aka kirkira domin abata addinin, acikin wannan littafin akwai tarihi nagaskiya na injila wanda yasha banban da tarihin wannan littafin ayau"
Hannuwanshi ta sake rikewa cikin nata tana kallon kyakkywar fuskarshi,hakika yau ta yarda cewar jabir mutum ne mai ilimin gaske wanda ba iya na addininsa kadai ba har na addininta ya hada,
"Abu dukkan abubuwan da kafada nasan gaskiya ne sai dai akwai daga cikin labaran da ka fada min wanda mu ba haka yazo mana acikin Bible ba"
Manyan idanuwanshi ya zuba mata yana wani salihin murmushi,
"Shiyasa nace miki tun farko ancanja littafin ne kuma labaran da suka zo acikin Bible suna wuce iyakane, suna zarce inda ya kamata su tsaya shiyasa acikin alqur'ani mai girma ubangiji ya kira yahudawa da wadanda suka sauya littafinsa, Allah yace "'Gwalalon azaba ya tabbata ga wadanda suka yi rubutu da hannunsu sannan suke cewa wannan rubutun daga Allah yake saboda wasu yan kudi kadan wanda zasu samu ,
Azaba ta tabbata agaresu gameda abinda suke rubutawa, azaba ta tabbata akansu gameda kudin da suke samu"' _(alqur'an, chapter 3)_,
Kinga kenan shi kansa Bible din littafine wanda aka canjashi tunda ansaukar da alqur'ani ne abayan an saukar da injila (Bible) amma gaba daya acikin ayoyin alqur'ani mai girma duk inda Allah ya tashi yin magana akan injila yana cewa an canja littafin, Allah yayi mana bayanin hakan dalla dalla acikin suratul Al'imran surah ta uku daga farkon aya har zuwa ta karshe"
"Hakane abbu,yanzu nagane jawabanka gaba daya"
"Tunda kin gane to ki kwanta kiyi bacci saboda dare yayi sosai"
"To kar ka sake yin wani kukan pls" tafada cikin shagwaba tana zare hannuwanta daga cikin nashi, tashi yayi ya shiga bathroom yayi alwala ya fito yana kallon agogon dake makale a bangon cikin dakin, karfe 2:30 nadare, gafen gadon yaje ya kwanta yana kokarin jan bargo domin rufe jikinshi,
"Abbu yau baka yimin addu'a ba" ya jiyo muryar goodness abayanshi tana fada, juyawa yayi yafara karanta mata addu'a, sai da yagama sannan yayi wa kansa ya shafe jikinsa yagyara kwanciyarsa,
Goodness najinshi tana kwance tana kallonsa ta kasa bacci tunani ne kala kala ke zagaya kwakwalwarta, ita dai tasan acikin Bible akwai abubuwan da suka zo nagaskiya amma basa aiki dasu misali, abangaren hukunce hukunce akwai hukuncin saka hijabi amma kuma basa sakawa, sannan akwai hukuncin alwala wato an koyar dasu yanda zasu yi alwala itama basa yi, akwai hukuncin sata idan mutum yayi nanma ba ayi, kuma ta taba ganin wani hoto da aka zana nana maryam mahaifiyar annabi Isah da hijabi ajikinta taga an zanata ba azanata da siffa irin wacce su suke da ita ayanzu ba, gashi ba salla suke yiba amma idan sunje masallacin Jerusalem aikin hajjinsu dolene sai mutum yayi alwala yayi salla raka'a biyu, kai anya kuwa babu wani boyayyen al'amari acikin wannan lamarin?
Juyi tayi takoma rigingine tana kallon sama acikin duhun dakin, tafi minti 30 tana tunane tunane wanda ta kasa gane kansa daga karshe taja jikinta ahankali taje ta kwanta ajikin jabir tana mai kudurin idan gari ya waye akwai tambayar da zata yi masa, hannunshi ta lalubo ta rike cikin nata tana matsawa ahankali, duk jabir najinta domin ba bacci yake yiba idonshi biyu kawai yayi mata shiru ne.
Yana jinta ta fara fitar da numfashi ahankali alamun tayi bacci, hannuwanshi yasaka ya zageyata ya rungumeta acikin jikinsa, hannunshi guda daya yasa ya shafo tulin gashin kantin dake kanta wanda yake himili guda shi dai har yanzu bazai iya cewa ga yanayin gashinta ba saboda tun zuwanta gidan kullum cikin attach take idan ba kitso ba to kalba,
Yanata yan tunane tunane har baccin shima yayi nasarar awon gaba dashi.
Kamar kullum washe gari da safe bayan ta kammala shirya komai tayi wanka da ruwan data zuba turaren almiski aciki kasancewar ita bata San amfaninsa ba,
Kwalliya tayi tasaka English wears wanda jabir ya siyo mata lokacin da yaje _madinahtul munawwara_ rigar bakace mai adon duwatsu yayinda skirt din kuma blue colour ce mai santsi, bakar hula ta saka ta sake shafe jikinta da turaren muski da sauran turaruka masu dadin kamshi,
Breakfast din jabir ta dauka ta nufi part dinsa, tana shiga yana fitowa daga cikin bedroom dinsa cikin hadadden farin danyen boyel dinkin riga da wando da kuma babbar riga, ba karamin kyau yau dinnan yayi ba dan ji take inama tana da camera da ta haska shi,
"Good morning abbu" ta fada tana karkace kanta gamida langabar dashi,
"Morning, kar ki ajiye min anan miko min shi nan" yafada lokacin da ya ke zama kan kujerar dake cikin falon, fasa dorawa tayi akan dining table din ta dauko ta kawo masa ta dora akan center table din gaban kujerar da yake zaune,
Tea ta tsugunna ta soma hada masa, kasa kasa yake kallonta gaba daya kamshinta ya gama cika masa hanci ji yake yasan kamshin tiraren amma ya kasa gane wanne irine,haka itama kamshinsa gaba daya ya cika mata hancinta domin numfashinta har wani sauya launin fitarsa yayi,
"Gashi abbu" tafada tana dora masa bisa kan table din
"Yawwa nagode ya fada ahankali"
Zama tayi agefensa tana kallon yanda yake shan tea din cikin sanyinshi ahankali ahankali kamar wani marar lafiya,
"Abbu inada tambaya,Acikin bible an fada mana cewar Jesus zaiyi ceto shida ruhu (haske),Ku wa akace muku zaiyi ceto acikin littafinku?"
Cup din hannunsa ya ajiye ya dan kalleta