Sashe 51
Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Al'amin ya tambayeta yana rungumeta,
"Ehh al'amin, me kakeci hakane naga ka sake zama kato?"
"Anty shinkafa kaza kema idan kina so ummu na zata dafa miki ta iya sosai"
Dariya tayi ta saukeshi kasa,"ohh al'amin ashe har yanzu dai kana nan da labarin nan ko?"
"Kuzo mu karasa gidan tukunna" muryar ummu ta katsesu kafin al'amin yabada amsa, tare suka jera suka nufi wurin da zasu samu taxi suhau,
Ganin yanda ummu ta shige jikin jabir tana yi masa rada suna dariya yasanya bahijja jin wani kololon bakin ciki yataho ya tokareta akirji, ita kam badai zafin kishiba musamman ma akan jabir,
Suna tsaye abakin titi tana rike da al'amin da yar trolley dinta tana kallon yanda jabir yasakala hannunshi tabayan ummu ya karata jikinshi sai rade rade suke yi suna dariya, duk ji tayi tsayuwar ta isheta alla alla take su samu taxi su isa gida dan ta daina ganin wannan abun haushin,
Sun dade atsaye kafin suka samu taxi, jabir ne ya shiga gaba sukuma suna baya azaune har lokacin al'amin yana manne da ita,
Tafiyar da batafi ta mintuna 20 bace takaisu kofar gidan da ummu take, nan suka firfito ita dai bahijja kallon garin kawai take tabbas wannan gari mai ni'ima ne domin iskar dake kadawa ma aciki daban take da sauran iskar dake kadawa aduniya, jabir ne ya biya mai taxi din sannan suka dunguma zuwa cikin gidan,
A falo suka yada zango inda ummu ta shisshirya musu kayan tarba kala kala, abincin larabawa tayi musu iri iri wani kuma ta siyo musu a restaurant,
Bin dan madaidaicin gidan bahijja take yi da kallo aranta tana tunanin gaskiya indai mutum yana zaune awannan wurin babu abinda zai dameshi shiyasa ummu da al'amin sukayi fes dasu gashi al'amin larabci abakinsa kamar sudais,
Abincin ummu ta fara zuzzuba musu, tana cewa,
"Antyn al'amin anzo lafiya? Ya mutanen gida?"
"Lafiya lau maman al'amin, kowa lafiya" bahijja tabata amsa tana gyarawa al'amin zama ajikinta,
Acikin babban faranti ummu ta zuba musu abincin dukkaninsu suka hadu suka fara ci ita dai bahijja duk jinta take atakure saboda yadda taga ummu sai rawar jiki take da ganin jabir, hakan yasata niyyar suna gama cin abincin nan zata nemi da anuna mata wurin zamanta domin ta tafi tabasu wuri,
Kallonsu take yi kasa kasa yanda ummu take manne dashi ta dora hannunta akan nashi tana wasa dashi gashi ko acikin kwanon abincin ma sai tsokanarshi take yi tana daukar spoon dinshi wai adole sai dai suci da spoon daya ita dashi,
Duk jin zaman tayi ya gundureta dan haka ta mike ta koma saman kujera ta zauna akujerar da tasan bazata cigaba da hangosu ba, al'amin ne ya biyota ya dale jikinta suka ci gaba da labarinsu.
Murmushi tayi takama hannuwan al'amin ta rirrike "al'amin kaga yanda ka zama kato kuwa? Sai kace irin kajin agric dinnan"
Dariya yayi yana jan mayafinta "hakama ummu na take cewa kullum"
Su jabir sun dade agaban kwanon abincin shida ummu suna dan taba soyayya,tashi jabir yayi yana kallon wurinda bahijja suke,
"Binti muje nakaiki masaukinki saboda ki samu kiyi wanka ki huta"
Yafada yana shafa sumar kanshi, kallonsa ta juyo tayi dama ta gaji da wannan zaman takurar dan haka batare da tace dashi komai ba ta tashi tana rike da hannun al'amin,
"Abu al'amin bari nazo muje mu kaita"
"To amma ki dan daukowa al'amin kayanshi koda guda 3 ne sai su zauna tare ya tayata hira" yafada yana kamo dayan hannun al'amin din,
"Al'amin ni bazaka kulani bane sai iya antynka zaka kula?"
Rungumeshi al'amin yayi yana cewa "abbu zan kulaka mana,ai tare zamuje da anty ko?"
Kafin jabir ya bashi amsa Ummu har tafito hannunta rikeda wata yar karamar jaka mai kyalkyali wacce ta zubowa al'amin kayansa aciki,
Dukkaninsu suka dunguma zuwa hotel din da za a kamawa bahijja daki domin gidan da ummu take ciki daki dayane sai falo da toilet da kitchen dama gidane na yan makaranta,
Wani hotel sukaje jabir ya biya kudin dakin ya karbi key suka dunguma zuwa dakin, sai da suka shigar dasu har ciki suka dudduba yanda tsarin dakin yake sannan suka yi musu sallama zasu tafi, ko jiyowa bahijja bata yi ba ayanda take ta juya musu baya tana ninke zanin gadon da suka samu acikin dakin domin shinfida nata,bata ko jiyoba tace su gaida gida domin bata ma son ta juya ta gansu saboda taga tun ahanya acikin mota suke wani shisshigewa junansu kamar wasu sabbin shiga,
"Abbu mu anan zamu kwana nida anty ko?"
"Ehh al'amin, bye bye ko"
Al'amin bai ko damuba saima daga musu hannu da yafara yana yi musu bye bye,
"Binti babu wani abu ko?"
"Babu" tafada atakaice, jan hannunshi ummu tayi suka fice daga cikin dakin suka tafi,zama bahijja tayi agefen gadon ta dafe goshinta kafin wani lokaci har hawaye sun fara sintiri akan kuncinta, al'amin ne yaje kusa da ita yana leka fuskarta,
"Anty bakida lafiya?"
Kai ta daga masa tayi sauri tafara share hawayen fuskarta, "idona ne yake ciwo al'amin"
"Sannu anty, ki fadawa abbuna ya kawo miki magani"
Kai ta sake daga masa amma bata kara magana ba domin ita kadai tasan yanda takeji acikin zuciyarta.
Dakyar ta iya tashi ta karasa gyara kan gadon ta tube ta shiga toilet tayi wanka amma acikin toilet dinma ta dan jima tana sharar hawaye sannan ta yi alwala tafito tadawo cikin dakin amma al'amin baya ciki, falo ta leka anan ta hangoshi ya kunna tv ya kwanta yana kallo,
Simple make up tayi tazira riga kalar ruwan madara marar nauyi doguwa tayi salla ta kwanta domin kanta ciwo taji yana yi mata saboda kukan da tayi,
Baccine yayi nasarar daukarta har lokacin sallar magrib yayi, sai alokacin ta iya tashi tana jin jikinta yana yi mata wani ciwo marar dadi ga kanta shima kamar zai fashe dan azaba.
_Masu karatu mu hadu ashafi nagaba domin jin karshen labarin wani haske, nagode sosai da kulawarku_
*_Ummi A'isha_*👌🏻
[10/26, 1:51 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: [10/19, 4:35 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_116-120_
~~~Ahankali cikin sanyin jiki ta sauko daga kan gadon tafara tafiya ahankali ta shiga bathroom, alwala tayi ta fito tana tafiya tana hada hanya saboda duhun da take gani agabanta sakamakon rufe mata idanuwanta da ciwon kan dake damunta yayi,
Azaune tayi sallar tana idarwa ta kwanta awurin tana rike da kanta saboda jinsa take kamar zai fice daga jikinta,
Al'amin ne ya shigo cikin dakin yana faman kwala mata kira,
"Anty zo muje muyi kallon tom and jerry...!"
Ganinta kwance tana hawaye yasashi yin shiru ya karasa kusa da ita,
"Anty har yanzu bakida lafiya?"
Kai ta daga masa sannan ta bude bakinta dakyar tace "al'amin anyi salla fa, ka bar kallon nan kaje kayi salla"
Hannunta ya kamo yana kallon "nayi sallar ai anty yanzun nan nadawo daga masallaci"
Zama yayi ra'as agabanta yana kallonta, "anty ki yiwa abbu na waya ya kawo miki magani"
Kasancewar bata son surutu yau yasata daga masa kai, wayar ta yaje ya dauko mata ya kawo mata sai alokacin ma tagane ashe kiran bazai yiyu ba,
"Al'amin bazan samu abbu awaya ba sai dai mubari har sai lokacin da ya gama abinda yake yi yazo"
Tana fadar maganar ne cikeda damuwa domin hawayene ke bin kumatunta,rike hannunta al'amin yayi yana girgizashi,
"Anty inyi miki addu'ar kamun kai?"
Kai ta daga masa, hannunsa yasa ya rike kan nata ya fara yi mata addu'a tana jinsa yayi bisimillah kafa uku sannan yafara karanto mata "As'alul lahil azim rabbil arshil azim an yashfiki" itama sau uku yana yi yana tofa mata a goshinta,
Babu laifi ta dan ji sausauci kam amma kuma ciwon da zuciyarta take yi mata ahalin yanzu ji take kamar tacireta ta yar,
Tana nan kawance al'amin akusa da ita suka fara jin bugun kofa, murna al'amin ya shiga yi "anty watakila abbuna ne yadawo"
Dagudu yaje ya bude kofa, ma'aikatan hotel din yagani masu bi daki daki suna raba abinci, nasu suka mika masa suka juya sukayi gaba,
Jikinsa asanyaye ya nufi wurin bahijja wacce duk tana jiyosu shida masu rabon abincin,
"Anty ba abbu bane, masu raba abincine"
"Al'amin ajiye abincin a falo bana son ganinshi,dama nasan ba abbu bane domin abbu bazai taba iya tunawa damu a wannan lokacin ba"
Tana maganar tana goge hawayen fuskarta, tashi tayi ta gabatar da sallar isha sannan tasake kwanciya a inda tayi sallar, kwanciyarta keda wuya wani naunauyan bacci yace muje zuwa,shi kansa al'amin shima baici abincin ba yana dawowa daga salla yayi kwanciyarsa a falo akan doguwar kujera.
Misalin karfe 2 nadare ta tashi daga naunauyan baccin da ya dauketa, bude idonta tayi tafara tuno jabir acikin kwakwalwarta, yanzu tasan yana can tare da ummu al'amin suna shan soyayyarsu,
Zaune ta tashi tayi tagumi tana karewa dakin da take ciki kallo, hakika kishi abune mai nauyin gaske wanda indai mutum baiyi takatsantsan ba zai iya halaka shi ta raya hakan acikin zuciyarta domin ita yanzu ji take ko kadan bata kaunar ganin fuskar jabir, haushinsa take ji sosai babu laifin tsaye babu na zaune,
Tana nan zaune tana karanta wasikar jaki zuciyarta ta shawarceta da taje tayi alwala tazo tayi salla ko dan koyi da jabir domin haka taga yana yi akowanne dare kai kusan ma baccinsa kullum ragagge ne bashida yawa, tsayuwar darensa tafi baccinsa yawa domin ko sunyi bacci tare to tsakiyar dare sai ya tashi yayi sallar nafilar da ta zame masa jiki,
Tashi tayi tafara bin jikin bango har ta shiga toilet din tayi alwala ta fito tazo kan abun salla, zata tada kabbara kenan taji motsi a falo, ahankali taje ta leka abun mamaki al'amin tagani shima yana tsaye yana sallar,
"Kyan da ya gaji ubansa" tafada ahankali gamida komawa cikin dakin tana tunanin babu ta inda al'amin yabar abbunshi a fannin dabi'u da halayya,
Salla tayi rak'a hudu domin kasala take ji ajikinta sosai, zama tayi tafara yiwa kanta da mijinta addu'a sannan tafara addu'ar Allah ya ganar da mahaifiyarta gaskiya itama tabi addinin da farin jakada masoyinmu na hakika annabi Muhammad yazo dashi.
"Ehh al'amin, me kakeci hakane naga ka sake zama kato?"
"Anty shinkafa kaza kema idan kina so ummu na zata dafa miki ta iya sosai"
Dariya tayi ta saukeshi kasa,"ohh al'amin ashe har yanzu dai kana nan da labarin nan ko?"
"Kuzo mu karasa gidan tukunna" muryar ummu ta katsesu kafin al'amin yabada amsa, tare suka jera suka nufi wurin da zasu samu taxi suhau,
Ganin yanda ummu ta shige jikin jabir tana yi masa rada suna dariya yasanya bahijja jin wani kololon bakin ciki yataho ya tokareta akirji, ita kam badai zafin kishiba musamman ma akan jabir,
Suna tsaye abakin titi tana rike da al'amin da yar trolley dinta tana kallon yanda jabir yasakala hannunshi tabayan ummu ya karata jikinshi sai rade rade suke yi suna dariya, duk ji tayi tsayuwar ta isheta alla alla take su samu taxi su isa gida dan ta daina ganin wannan abun haushin,
Sun dade atsaye kafin suka samu taxi, jabir ne ya shiga gaba sukuma suna baya azaune har lokacin al'amin yana manne da ita,
Tafiyar da batafi ta mintuna 20 bace takaisu kofar gidan da ummu take, nan suka firfito ita dai bahijja kallon garin kawai take tabbas wannan gari mai ni'ima ne domin iskar dake kadawa ma aciki daban take da sauran iskar dake kadawa aduniya, jabir ne ya biya mai taxi din sannan suka dunguma zuwa cikin gidan,
A falo suka yada zango inda ummu ta shisshirya musu kayan tarba kala kala, abincin larabawa tayi musu iri iri wani kuma ta siyo musu a restaurant,
Bin dan madaidaicin gidan bahijja take yi da kallo aranta tana tunanin gaskiya indai mutum yana zaune awannan wurin babu abinda zai dameshi shiyasa ummu da al'amin sukayi fes dasu gashi al'amin larabci abakinsa kamar sudais,
Abincin ummu ta fara zuzzuba musu, tana cewa,
"Antyn al'amin anzo lafiya? Ya mutanen gida?"
"Lafiya lau maman al'amin, kowa lafiya" bahijja tabata amsa tana gyarawa al'amin zama ajikinta,
Acikin babban faranti ummu ta zuba musu abincin dukkaninsu suka hadu suka fara ci ita dai bahijja duk jinta take atakure saboda yadda taga ummu sai rawar jiki take da ganin jabir, hakan yasata niyyar suna gama cin abincin nan zata nemi da anuna mata wurin zamanta domin ta tafi tabasu wuri,
Kallonsu take yi kasa kasa yanda ummu take manne dashi ta dora hannunta akan nashi tana wasa dashi gashi ko acikin kwanon abincin ma sai tsokanarshi take yi tana daukar spoon dinshi wai adole sai dai suci da spoon daya ita dashi,
Duk jin zaman tayi ya gundureta dan haka ta mike ta koma saman kujera ta zauna akujerar da tasan bazata cigaba da hangosu ba, al'amin ne ya biyota ya dale jikinta suka ci gaba da labarinsu.
Murmushi tayi takama hannuwan al'amin ta rirrike "al'amin kaga yanda ka zama kato kuwa? Sai kace irin kajin agric dinnan"
Dariya yayi yana jan mayafinta "hakama ummu na take cewa kullum"
Su jabir sun dade agaban kwanon abincin shida ummu suna dan taba soyayya,tashi jabir yayi yana kallon wurinda bahijja suke,
"Binti muje nakaiki masaukinki saboda ki samu kiyi wanka ki huta"
Yafada yana shafa sumar kanshi, kallonsa ta juyo tayi dama ta gaji da wannan zaman takurar dan haka batare da tace dashi komai ba ta tashi tana rike da hannun al'amin,
"Abu al'amin bari nazo muje mu kaita"
"To amma ki dan daukowa al'amin kayanshi koda guda 3 ne sai su zauna tare ya tayata hira" yafada yana kamo dayan hannun al'amin din,
"Al'amin ni bazaka kulani bane sai iya antynka zaka kula?"
Rungumeshi al'amin yayi yana cewa "abbu zan kulaka mana,ai tare zamuje da anty ko?"
Kafin jabir ya bashi amsa Ummu har tafito hannunta rikeda wata yar karamar jaka mai kyalkyali wacce ta zubowa al'amin kayansa aciki,
Dukkaninsu suka dunguma zuwa hotel din da za a kamawa bahijja daki domin gidan da ummu take ciki daki dayane sai falo da toilet da kitchen dama gidane na yan makaranta,
Wani hotel sukaje jabir ya biya kudin dakin ya karbi key suka dunguma zuwa dakin, sai da suka shigar dasu har ciki suka dudduba yanda tsarin dakin yake sannan suka yi musu sallama zasu tafi, ko jiyowa bahijja bata yi ba ayanda take ta juya musu baya tana ninke zanin gadon da suka samu acikin dakin domin shinfida nata,bata ko jiyoba tace su gaida gida domin bata ma son ta juya ta gansu saboda taga tun ahanya acikin mota suke wani shisshigewa junansu kamar wasu sabbin shiga,
"Abbu mu anan zamu kwana nida anty ko?"
"Ehh al'amin, bye bye ko"
Al'amin bai ko damuba saima daga musu hannu da yafara yana yi musu bye bye,
"Binti babu wani abu ko?"
"Babu" tafada atakaice, jan hannunshi ummu tayi suka fice daga cikin dakin suka tafi,zama bahijja tayi agefen gadon ta dafe goshinta kafin wani lokaci har hawaye sun fara sintiri akan kuncinta, al'amin ne yaje kusa da ita yana leka fuskarta,
"Anty bakida lafiya?"
Kai ta daga masa tayi sauri tafara share hawayen fuskarta, "idona ne yake ciwo al'amin"
"Sannu anty, ki fadawa abbuna ya kawo miki magani"
Kai ta sake daga masa amma bata kara magana ba domin ita kadai tasan yanda takeji acikin zuciyarta.
Dakyar ta iya tashi ta karasa gyara kan gadon ta tube ta shiga toilet tayi wanka amma acikin toilet dinma ta dan jima tana sharar hawaye sannan ta yi alwala tafito tadawo cikin dakin amma al'amin baya ciki, falo ta leka anan ta hangoshi ya kunna tv ya kwanta yana kallo,
Simple make up tayi tazira riga kalar ruwan madara marar nauyi doguwa tayi salla ta kwanta domin kanta ciwo taji yana yi mata saboda kukan da tayi,
Baccine yayi nasarar daukarta har lokacin sallar magrib yayi, sai alokacin ta iya tashi tana jin jikinta yana yi mata wani ciwo marar dadi ga kanta shima kamar zai fashe dan azaba.
_Masu karatu mu hadu ashafi nagaba domin jin karshen labarin wani haske, nagode sosai da kulawarku_
*_Ummi A'isha_*👌🏻
[10/26, 1:51 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: [10/19, 4:35 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_116-120_
~~~Ahankali cikin sanyin jiki ta sauko daga kan gadon tafara tafiya ahankali ta shiga bathroom, alwala tayi ta fito tana tafiya tana hada hanya saboda duhun da take gani agabanta sakamakon rufe mata idanuwanta da ciwon kan dake damunta yayi,
Azaune tayi sallar tana idarwa ta kwanta awurin tana rike da kanta saboda jinsa take kamar zai fice daga jikinta,
Al'amin ne ya shigo cikin dakin yana faman kwala mata kira,
"Anty zo muje muyi kallon tom and jerry...!"
Ganinta kwance tana hawaye yasashi yin shiru ya karasa kusa da ita,
"Anty har yanzu bakida lafiya?"
Kai ta daga masa sannan ta bude bakinta dakyar tace "al'amin anyi salla fa, ka bar kallon nan kaje kayi salla"
Hannunta ya kamo yana kallon "nayi sallar ai anty yanzun nan nadawo daga masallaci"
Zama yayi ra'as agabanta yana kallonta, "anty ki yiwa abbu na waya ya kawo miki magani"
Kasancewar bata son surutu yau yasata daga masa kai, wayar ta yaje ya dauko mata ya kawo mata sai alokacin ma tagane ashe kiran bazai yiyu ba,
"Al'amin bazan samu abbu awaya ba sai dai mubari har sai lokacin da ya gama abinda yake yi yazo"
Tana fadar maganar ne cikeda damuwa domin hawayene ke bin kumatunta,rike hannunta al'amin yayi yana girgizashi,
"Anty inyi miki addu'ar kamun kai?"
Kai ta daga masa, hannunsa yasa ya rike kan nata ya fara yi mata addu'a tana jinsa yayi bisimillah kafa uku sannan yafara karanto mata "As'alul lahil azim rabbil arshil azim an yashfiki" itama sau uku yana yi yana tofa mata a goshinta,
Babu laifi ta dan ji sausauci kam amma kuma ciwon da zuciyarta take yi mata ahalin yanzu ji take kamar tacireta ta yar,
Tana nan kawance al'amin akusa da ita suka fara jin bugun kofa, murna al'amin ya shiga yi "anty watakila abbuna ne yadawo"
Dagudu yaje ya bude kofa, ma'aikatan hotel din yagani masu bi daki daki suna raba abinci, nasu suka mika masa suka juya sukayi gaba,
Jikinsa asanyaye ya nufi wurin bahijja wacce duk tana jiyosu shida masu rabon abincin,
"Anty ba abbu bane, masu raba abincine"
"Al'amin ajiye abincin a falo bana son ganinshi,dama nasan ba abbu bane domin abbu bazai taba iya tunawa damu a wannan lokacin ba"
Tana maganar tana goge hawayen fuskarta, tashi tayi ta gabatar da sallar isha sannan tasake kwanciya a inda tayi sallar, kwanciyarta keda wuya wani naunauyan bacci yace muje zuwa,shi kansa al'amin shima baici abincin ba yana dawowa daga salla yayi kwanciyarsa a falo akan doguwar kujera.
Misalin karfe 2 nadare ta tashi daga naunauyan baccin da ya dauketa, bude idonta tayi tafara tuno jabir acikin kwakwalwarta, yanzu tasan yana can tare da ummu al'amin suna shan soyayyarsu,
Zaune ta tashi tayi tagumi tana karewa dakin da take ciki kallo, hakika kishi abune mai nauyin gaske wanda indai mutum baiyi takatsantsan ba zai iya halaka shi ta raya hakan acikin zuciyarta domin ita yanzu ji take ko kadan bata kaunar ganin fuskar jabir, haushinsa take ji sosai babu laifin tsaye babu na zaune,
Tana nan zaune tana karanta wasikar jaki zuciyarta ta shawarceta da taje tayi alwala tazo tayi salla ko dan koyi da jabir domin haka taga yana yi akowanne dare kai kusan ma baccinsa kullum ragagge ne bashida yawa, tsayuwar darensa tafi baccinsa yawa domin ko sunyi bacci tare to tsakiyar dare sai ya tashi yayi sallar nafilar da ta zame masa jiki,
Tashi tayi tafara bin jikin bango har ta shiga toilet din tayi alwala ta fito tazo kan abun salla, zata tada kabbara kenan taji motsi a falo, ahankali taje ta leka abun mamaki al'amin tagani shima yana tsaye yana sallar,
"Kyan da ya gaji ubansa" tafada ahankali gamida komawa cikin dakin tana tunanin babu ta inda al'amin yabar abbunshi a fannin dabi'u da halayya,
Salla tayi rak'a hudu domin kasala take ji ajikinta sosai, zama tayi tafara yiwa kanta da mijinta addu'a sannan tafara addu'ar Allah ya ganar da mahaifiyarta gaskiya itama tabi addinin da farin jakada masoyinmu na hakika annabi Muhammad yazo dashi.