← Book details Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 64

Sashe 49

Wani Haske Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallonshi tayi da mamaki "abbu shifa mal idi ko yaganni ba wani abu bane"

Kallon jikinta yayi duk hips dinta da kirjinta sun bayyana cikin kayan data saka domin sun fito radau,

"Waye yafada miki? Allah cewa yayi kar ki bayyanar da adonki ga kowa sai ni sai ko wanda yake muharraminki"

"To abbu bazan sakeba"

Jan hannunta yayi har lokacin tana rabe ajikinsa yayi part dinsa da ita.

_Gaisuwa mai yawa gareku Hawy na & AG tawa ni daya._[truncated by WhatsApp]

[10/26, 1:51 PM] 🍬🛍💍Salma🍬🛍💍: [10/15, 2:21 PM] Ummi A'isha👌🏻: *WANI HASKE*

_*NA*_

_*UMMI A'ISHA*_

_111-115_

_Sak'on gaisuwa gareki Batool Mamman masoyiyar wani haske, na gaisheki sosai_

~~~A tsakiyar falonshi sukayi burki, kallo sosai jabir yake binta dashi saboda ba karamin kyau tayi ba gashi sai kamshine mai dadi yake tashi daga jikinta,

Kafadunta ya dafa yana yi mata murmushi na musamman,

"Binti kinyi kyau sosai.." Yafada yana sinsinar wuyanta,

"Abbu nagode, kaima kayi kyau din ai"

Rike hannuwanshi tayi tana faman sunkuyar da kanta, "binti menene hakan? Me hakan yake nufi?"

Dagowa tayi ta kalleshi, "abbu muje kayi wanka"

Hannunshi tafara ja tana tafiya, binta yayi har cikin bedroom dinshi, hularshi ta cire ta nufi drewar domin adanawa, tana ajiyewa ta dawo inda yake tafara kokarin cire masa babbar rigar jikinshi, yana tsaye yana aikin kallonta duk wani motsinta akan idonshi ne har ta gama cire masa kayan ta barshi dagashi sai farar vest da gajeren wando blue,

"Bari nazuba maka ruwan wankan abbu"

Binta yayi har cikin toilet din tana hada masa ruwan yana ta bayanta atsaye sai da ta kammala cika wani katon baho da ruwa sannan ta jiyo gareshi,

"Abbu gashi" tana gama fada tafara kokarin fita, hannunta ya riko da tausassan hannunshi,

"Kar ki tafi binti, ki tsaya ki karasa ladanki"

Hannunta tafara kokarin zamewa daga nashi tana mammake kafadarta, cikin shagwaba tafara magana,

"Nidai abbu nayi wanka na dazu, dan Allah ka bar min kwalliyata kar ka bata min"

Janta yayi da karfi yayi mata masauki acikin kirjinshi "tsaya kiji bintina, kawo kunnenki nafada miki wani abu"

"Nidai a'a, abbu wlh kazama marar hakuri yanzu, gaskiya gobe kayi azumi"

"Babu azumin da zanyi, kuma ai kece kika sani nazama marar hakurin"

Daukarta yayi cak ya ajiyeta cikin bahon wankan.

Daukota yayi ya ajiyeta agefen gado yana yi mata dariya "binti da kikace bakya so, ashe dama gulma ce kinma fini so"

Fuskarta ta rufe da tafin hannunta,"abbu kabari ko inyi maka kuka"

Murmushi yayi yaje ya dauko lotion yazo inda take "yi hakuri kar kiyi pls"

Ajiyar zuciya ta saki daidai lokacin da yafara warware towel din jikinta domin shafa mata mai,

Agurguje ya shiryata shima ya shirya dama yanzu tanada kaya ajiyayyu acikin dakinsa kusan ma duk abubuwan da zata bukata ta ajiyesu adakin,

Hannunta yakama zuwa falo domin saura kadan lokacin sallar mangarib yayi, sai alokacin suka tuna da files din dake ajiye akofar falon

"Binti kina sani ina mantuwa fa" yafada yana jan hancinta,

Hannunshi ta rike "nidai kar ka dora min laifi abbu"

Tana manne ajikinsa sukaje suka dauko files din suka shigo dashi, zama tayi akan cinyarsa tareda kwantar da kanta ajikin kirjinsa,

"Zaki barni na iya yin aikin nan kuwa? Yace da ita yana shafar kanta,

"Zan barka mana abbu"

"To dagani naje masallaci nadawo" kiss tayi masa akan kumatunsa kafin ta dagashi tana kallonsa, masallaci ya fita ita kuma ta koma sashenta, sai da yayi har sallar isha sannan ya dawo gidan nan ya iske bahijja ta sake caba ado tasha kwalliya sosai cikin leshi yellow mai stones ajiki,

Zama tayi ajikinsa suka fara mikawa junansu sakonnin soyayya masu nauyin gaske, sun dade suna nunawa junansu soyayya kafin su hau dining table suka ciyar da junansu,

Falo suka dawo jabir yafara ayyukansa amma kuma duk hankalinsa yana kan bahijja motsi kadan sai ya kalleta dakyar ya samu ya duba files guda biyar daga nan ya rufe babin aikin ya bude babin soyayya shida bintinsa.

Misalin karfe 10 suna kwance adakinshi yana rike da hannunta yana da wasa dashi ya fara tambayarta akan littafin da yafara koyar da ita na akdari,

"Menene farkon abinda ke wajaba akan baligi?"

Juyi tayi akan kirjinshi kafin ta bashi amsa "farkon abinda yake wajaba akan baligi shine ya inganta imaninsa sannan yasan da wanne abune zai gyara farillan ainihinsa dashi"

Sake tambayarta yayi "kamar da wanne abune zai inganta farillan ainihinsa dashi?"

"Abbu kamar hukunce hukuncen sallah, dana tsarki, dana azumi"

Sake rungumeta yayi yana yimata sumba akan goshinta, "yarinya ashe kina gane karatun da nake dora miki, wannan hukunce hukunce ya wajaba akan dukkan baligi ya sansu kuma yayi aiki dasu domin kowacce ibada ana son mutum yasan hukunce hukuncen da suka shafeta kafin ya gabatar da ita, misali salla, ana son baligi yasan abubuwan da suke warwareta da wadanda suke gyarata kamar kabli da ba'adi, hakama tsarki, azumi shima yakamata baligi yasan abubuwan da suke batashi da kuma abunda mai azumi ya kamata ya nisanta domin akwai abubuwa da dama da suke warware azumi wadanda bamu daukesu a matsayin manyan laifuffuka ba kamar giba yi da wani, kazafi da karya"

"Abbu menene giba?" Ta tambayeshi tana dago kanta domin kallon fuskarsa,

"Binti baki san giba ba? Giba itace gulma, zancen wani, annamimanci, fadin abu marar kyau ga wani wanda baya nan amma annabi ya siffatanta giba da cin naman mutum domin wani lokaci suna zaune da sahabbai sai yace dasu _"shin dayanku yana iya cin naman dan uwansa? Sai sahabbai sukace tayaya dayanmu zai ci naman dan uwansa ya rasulillah? Sai annabi yace duk wanda yayi zancen dan uwansa baya nan yafadi mummunan abu akansa yaci mutuncinsa to kamar yana yankan naman jikinsa yana cine"_,kinga kuwa indai hakane ya zama dole mu rinka kame harshenmu domin shine yafi komai hatsari atattare damu shiyasa alokacin sahabbai akwai sahabin da yake zuba duwatsu acikin bakinsa saboda kar yafadi wata magana wacce ta kaucewa shari'a,shiyasa sai kiga sahabi yayi kwana uku baiyi magana ba yana ta juya maganar acikin zuciyarshi yana tunanin shin ya fadeta ko yayi shiru, akwai wania sahabi wanda ya nemida annabi yayi masa nasiha sai annabi ya zaro harshensa ya nuna masa yace kaji tsoron wannan domin yana halakarwa,amma mu ya muke ayanzu? Bamu dauki gulma da annamimanci amatsayin laifi ba gashi mun iya cin mutuncin junanmu bayan kuma acikin wani hadisi annabi yace _"'duk wanda yaci mutuncin dan uwansa to Allah zaici mutuncin fuskarsa da wuta aranar alqiyama"'_ bafa wai dan uwa najini ba a'a dan uwa musulmi domin musulmi dan uwan musulmi ne haka annabi yafada, shiyasa yana da kyau mutane su rinka sauraron malamai saboda su gane illar gulma da annamimanci da k'azafi domin dukkaninsu laifuka ne masu nauyin gaske shi kansa mai yin annamimancin ma annabi cewa yayi _"'La yadkulil jannatu nammamun, wato annamimi bazai shiga aljannaba"'_ wannan hadisin daga wurin huzaifa dan yamani aka karbo shi,bukhari da muslim kuma suka rawaitoshi"
"Abbu Allah ya rabamu da sharrin harshe"

"Amin binti, kina jin bacci ko wata hirar za muyi?"

Idanuwanta ta rufe da tafin hanunta "abbu sai kanata sani ina jin kunya"

Murmushi yayi ya zare hannun nata daga fuskarta, "hakanma da lada binti domin kunya wani yanki ne daga cikin yanki na imani"

"To nidai bacci zanyi kayi min addu'a"

"To shikenan Allah ya kaimu gobe da asuba sai kiyi biyan bashi"

Shiru tayi tai lakwas ajikinsa yafara karanto mata addu'o'in kwanciya bacci yana tofa mata ajikinta.

Washe gari da safe bayan ya shirya domin zuwa office ya riko hannun bahijja wacce tasha gayu cikin farar atamfarta mai zanen hannu ajiki,

"Binti ki hada min kayana anjima zanyi tafiya, zanje Kaduna wani conference"

Yatsunshi ta riko ta makalkaleshi,

"Abbu tare zamu tafi ko?"

Kai ya girgiza mata "a'a batare zamuje ba, ai kinga hotel ne bazan iya zuwa dake hotel ba, kiyi hakuri kinji kwana 3 kawai zanyi"

Daru tasa masa tafara doddoka kafafunta akasa tana kuka kamar wata yar karamar yarinya,

"Nidai abbu sai nabika, kuma shikenan ni kadai zaka bari, nidai bazan yarda ba, tare zamu tafi" tana fada tana kuka, kallo kawai yake binta dashi dama haka ya guda shiyasa yaki sanar mata da maganar tafiyar tun jiya saboda yasan zaisha rikici da shagwaba iri iri,

Binta yayi inda take tsaye ta juya masa baya tana kuka, ahankali ya rungumeta ta baya yafara kissing din wuyanta, juyo da ita yayi ya zubawa fuskarta ido, kuka take yi sosai kamar wacce aka yiwa mutuwa,

"Kiyi shiru binti, kwana ukune fa"

Idonta ta runtse wasu sabbin hawayen suka sake iyo ambaliya akan Kumatunta,

"Dan Allah abbu kar ka tafi ka barni"

Rungumeta ya sakeyi ajikinsa "to binti, shikenan amma dai ki hada min kayan bari naje office nadawo, ba lallai ne ma nayi tafiyar ba amma dai kihada min kayan kinji"

Kai ta daga masa tafara share hawayen kan fuskarta, dakyar ya iya rarrashinta ta tsaida kukan sannan ta rakashi tsakar gida tadawo tafara hada mishi kayan nan dinma tanayi tana hawaye har ta kammala.

Karfe 3 nayamma ya dawo gidan lokacin tana sashenta tana gyara style din dayan bedroom dinta tana canja salon jeren cikin dakin domin abune mai kyau uwar gida ta rinka sauyawa dakinta fasalin jerensa daga lokaci zuwa lokaci,

Ahankali ya sadada yaje inda take tsaye da pillow ahannunta tana gyarashi acikin rigarsa, ta bayanta ya tsaya yakai hannu ya toshe mata baki,

Mutsu mutsu ta fara yi tana ihun da ba a ji, kokawa take yi iya karfinta tana kokarin kwatar jikinta sai kuma tafara jin kamshin turarensa ahankali yana ziyartar hancinta,

Sakinta yayi yana yi mata dariya,

"Ke matsoraciya ce binti"

Kallonsa tayi sai kawai ta dauki pillow tafara kai masa duka

"Abbu kayi mugun bani tsoro wlh, nazata gardine ya shigo min gidan"

"Yi hakuri bintina, babu wanda ya shigo miki, nine nan"

Dukan ya shiga karewa da hannunsa har yayi nasarar kwace pillow din yajata ya hadata da jikinsa ya rungume,

"Abbu zakayi tafiyar ko ka fasa?"

"Binti kibari kibani abinci naci mana tukunna"

Hannunshi takama suka tasamma part dinshi inda ta shirya masa abinci mai rai da motsi, white rice with stew sai hadin salad,
Chapter 49 · 0% Book details