Sashe 4
Muwaddat Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
byn wani kankanin lokaci sai gashi ya zama matashi attajiri dake da mallakin gidaje, ya sayi motaci baya ga yaran kauyensu daya Diba suke karkashinsa.
zuwa lokacin yana da yaro daya mai sunan Ibrahim ,suna kiransa da akram da yake sunan mahaifinsa garesa ..
mukarama ta tagama karatunta na gaba da primary, ta zama cikakkiyar budurwa sosai gata da kyau da gogewa da iya tsara kwalliya ,cikin wannan lokacin ishaq abokin Muhammad wanda ya kasance abokin kasuwancinsa ne ya dawo daga kasar maleshia akan harkan kasuwanci da karatunsa .
ishaq hadadden matashi saurayi ne tsayaye mai zati da haiba uwa uba naira ta zauna ajikinsa asalinsa dan Kano ne amman babu inda baya shiga adalilin kasuwanci.
wata rana ya kawowa Muhammad ziyara,inda Muhammad yace "mukarama ta kawowa abokinsa abun motsa baki,tashigo parlour'n cike da natsuwa da kamewa uwa uba kunya, ai kuwa ishaq yana d'aura idanunsa akanta yarasa tsukuni amman dayayi wani tunani sai yayi saurin kawar da abinda yaji akanta, ta ajiye tire ishaq yace "ga leda nan ta wuce dashi tsarabarsu ce aciki, sam mukarama taki d'auka, ya d'auka ya mika mata nan ma taki amsa yace" haba kanwarmu ina ganinki mai kalar wayyayu, a wannan zamanin yaushe ake kunya hk?
mukarama ta juya akunyace zata fice daga parlour'n, 'yar drya Muhammad yayi yace "to in kin shiga ki turomin hajara kawai ,tana fita ishaq yace "amman wannan wani irin kunya ce hk sai kace ba yar zamani ba?
alhj Muhammad yace" ina ruwan mukarama haka Allah yayita komai nata sai ta had'a da kunya yarinya ce mai tsananin kawaici babu ruwanta.
yace "da kyau hk nake son naga mace nada kawaici da alkunya a dukkanin al'amuranta da ganin kanwar tamu mijinta ya dace kwarai ya fad'i hk saboda tunaninsa ko tana da aure.
alhj Muhammad yace"kuma ka gani bata da miji har yanzu bata tsaida miji ba karatu take domin ina da burin akanta,ina son na ingata rayuwarta da karatu boko domin a dama wannan duniyar daita, shiyasa duk masu kawo hari nake katse masu hanzari har sai ta gama, yanzu haka tana matakin diploma .
ishaq ya d'an dubesa a razane domin yasan asaninsa mutane karkara haka ,basu fiyye barin yaransu su jima hk batare da yin aure ba ....
"gsky abokina kayi nmj k'ok'arin gurin ingata rayuwarta ,yanzu dai kace babu kowa akasa masu neman aurenta?
"babu kowa ina suka ga fuska, ai sai sunga fuska tukun zasu zo, ni dai burina tayi karatu mai zurfi ta yadda zata taimaki al'umma da ita kanta, nan dai suka bar zance suka shiga hirar kasuwanci dayake daman harkar kasuwamci ne ta had'asu har suka zama abokai, acikinsu duk wanda wata harka tashigo hannunsa daya san za'a samu alheri y kan janyo dan'uwansa ciki, su samu alkhairi tare kasancewar dukansu ba masu kyashi ko bakinciki bane ,kowa yana k'aruwa da kowa suna harkar arziki tare gwanin sha'awa.
tunda ishaq yakoma gida sai ya kasa samun sukunin zuciya duk yadda ya runtse idanunsa mukarama yake gani tana yi masa gizo ,haka nan abin mamaki jiyayi gbdy ya tsinci kanshi da matsanancin kaunar mukarama ,ganin dayayi mata ya gigita kwalkwaluwarsa ,sosai yarinyar ta rikitashi ,ya rikice akanta har tunaninta na neman hanashi sukuni yin barci, shi kansa sai juya al'amarin yake aransa yadda farat daya ya gigice akanta gashi dan'uwanta na da buri akanta, dan hk ya danne abun aransa yacigaba da hakuri ,haka soyayar mukarama yayita cinsa arai har sai da aka samu wasu yan watani.
************
ran nan dai ishaq ya kasa hakuri adalilin soyayyar mukarama da kullun take sake huda kahon zuciyarsa, dan hk a zaunen da yake agaban mahamud yasoma maganar yadda yake son mukarama.
mahamud yayi shr yana sauraron abokinsa har yagama zayyana masa irin kaunar dayake yiwa mukarama,Muhammad yace "naji dadi kwarai kuma ina matukar farinciki da wannan bayani naka ,sanin kanka ne kafi karfin komai agurina ,zai yi wuya ka nemi wani abu a wurina na hanaka, musamman ma irin wannan alfarma ta aure, to amman akwai wani hanzari ba gudu ba kmr yadda kasani, bazan aurawa mukarama mijin da bazai barta tacigaba da karatunta ba, matsawar ka amince zata cigaba da karatunta agidanka shikenan na amince kaje ka nemi yardarta matukar ta amince da kai zan aura maka ita.
ishaq ya sauke naunauyen ajiyar zuciya kana yace "wannan ba wata matsala bace ni kaina har yanzu akan karatu nake kasan da haka ,domin lamarin kasuwancinmu na bukatar ilimi mai zurfi,bugu da kari ilimin mace nada matukar mahimmanci arayuwa.
"haka ne kam Allah yasa mu dace kana iya turo magabatanka idan ta amince , ishaq yace "ameen had'e dayiwa abokinsa godiya " domin sosai yaji dadin lafazinsa mahamud na gama fadar hk ya bari parlour'n.
ishaq ya nemi ganawa da mukarama ,byn tashigo parlour'n suka dan yi shru kad'an sannan yakira sunanta "ko kinsan zuwan nawa na yau dominki ne sabanin sauran lokuta?
ta d'an kalleshi cikin natsuwa, yayinda ta zuba masa idanu tana kallonsa da sauraren abinda zaice dan gabad'aya zuciyarta ta matsu da son jin abinda ke cin ransa akanta, domin itama tana jin wani abu a game dashi .
yacigaba "hakika mukarama dazaki min alfamar dana dan gutsara miki abinda ke cin raina a game dake, Allah yasamin tsananin kaunarki tun ranar farko dana d'aura idanuna akanki dayake nasan ba aure yayanki zai miki a wannan lokacin ba sai nayi kokarin danne sonki cikin zuciyata har sai yanxu ,a yanzu dai ina gabatar miki da kaina amatsayin wanda yake son aurenki amman menene ra'ayinki akaina ?
mukarama dai tayi shiru saboda batasan amsar dazata bashi ba, domin mutumin yana yi mata kwarjini ganin bata da niyyar bashi amsa yace "haba mukarama ya kikayi shr ai gara kiyi magana shi sha'anin aure ai ba'a yinsa da wasa zan so jin ta bakinki koda bakya sona barema bana fatan haka nafi son kiyi min alfarma bisa soyayya kar ma ki tsaya duba alaka don ba itace tasani sonki ba.
" kyawawan halaiyenki da dabi'unki na kirki ne suka janyo zazzafar kaunarki ,ki taimawa rayuwar wannan tsohon tuxuron ki aureshi domin idan kika ki aurensa ina tabbatar miki hk zai k'arasa sauran rayuwarsa batare daya ajiye iyali ba.
mukarama ta cigaba da yin shiru sai dai wannan karon kanta na sunkuye ,murmushi yayi saboda sanin halinta na kunya "haba zuciyar ishaq ki dan yi min magana ko naji dadi "tayi dariya amman batace komai ba yace"kenan dai ana son ishaq ya hakura," mai yiwuwa ina da wani abun da baza a soni dominsa ba?
sai a lokacin ta girgiza kanta, yace "ni kam muddin ba magana ki kai ba, gani nake ban canci asoni ba ,shi yasa kika barni da kokon barana a hannu, ai sauran maneman ba hk ake musu ba, ko kuma ko dan anga ni babban yaya ne kike ganin nayi miki tsufa?
maganarsa ta bata dariya har ta sa ta d'ago kanta da sauri suka dubi juna sannan tace "ko kad'an ba haka bane, ni dai aguna baka da wani aibu da kowace irin mace zata kika ,sai dai abunda nake son kagane ban taba yankewa kaina hukunci ba sai dai yayana ya yanke min.
"idan ta wannan bangare ne mugama magana da yayanki har ya amince har ma da sharadinsa nason ki cigaba da karatunki byn aurenmu, na kuma ji na gani na amince da hakan ,saboda ina matsanamcin sonki "duk da haka ni dai nayiwa kaina alkwarin komai zanyi sai da amincewarsa.
"da kyau kinga wannan biyayyar taki tana daga cikin abubuwan dayasa na kamu da sonki tunda kin tabbatar zabin d'anuwanki shine zabinki, a she dai naci babu hamayya kenan, domin na tabbatar d'anuwanki ba zai iya zaba miki wani fiyye dani ba.
"amman duk da hk xan baki lokaci kije kuyi shawara da matar yayanki tunda itace ta hannun damarki, dan ta abokina shi bana jin komai domin shine yace in nemi soyayya agurinki domin yana son baki cikakkiyar yanci shiyasa nake ganin yanzu shawara ta rage keda hajara babu ruwan aminina ,dan ko yau muka daidaita gobe ma yana iya d'aura mana aure.
ta dan fad'ad'a murmushinta "shikenan Allah yayi mana zabi mafi alkhari "yauwa masoyayyita abinda nake son ji kenan daga gareki, domin zabin Allah shine mafi alkhairi a gurinmu, gbdy dai ishaq ya gama kashewa mukarama jiki da salon soyayyarsa wanda sukayi tasiri a zuciyarta.
sosai yasamu matsugunni agurinta ,byn sunyi sallama tare da yi mata alkwarin zai dawo wani sati domin jin shawarar data yanke, kafin su rabu sai da yayi mata alkhairi mai yawa wanda kunya ta hanata kar'ba ,sai daya takurata sosai sannan ta amsa game da yi masa godiya tashige ciki, tana shiga Kai tsaye d'akin hajara tashiga domin ta fesa mata labari da bata ganta cikin parlour'n ba sai ta bita uwar daka ta isketa kwance ita da akram akan lafiyayyen gadonta suna ta sharar bacci cikin nishadi ta dan ja ta tsaya tana jan tsaki .
"ke kam aunty hajara kin cika so baccin tsiya ta fad'i hkn a fii yayinda tasa hannu tana girgizata, ta d'an motsa kadan tare da rungume d'anta ajikinta batare da ta bud'e idanunta ba ta sake komawa bacci abinta .
a hanzarce mukarama ta maka mata duka, hajara a firgice ta d'an bud'e idanunta ganin mukaramaa tsaye akansu tace "kai d'an Allah mukarama in banda d'aukar haki ki barmu muyi baccinmu .
mukarama cikin zolaya tace "mijinki yace na taimaka na tasheki sai nayi laifi?
hajara da sauri ta watseke tare da tashi, zaune har da d'an murmushinta, mukarama ta kwashe da dry "uhm yar dadi miji daga jin zance miji kin wani wartsetake to karya ne bashine yake nemanki ba ni nake son mgn dake hajara ta d'an kai mata duka "kyaji da karyarki ke daman babu damar kiga mutun yayi bacci sai kin tasheshi .
mukarama tace "ai ina ganin akan shegen baccin nan naki sai nayi miki kishiya in tura amarya d'akin yayana kina nan kina shirgar bacci.
"haba dan Allah kin isa ai dagani babu kari ai ni nafi karfin amarya.
"kiyi cika bakinki kigama zanyi maganinki .
suka fashe da drya .
kiyi driyarki ahankali karki tasar min da yaro inji cewar mukarama.
zuwa lokacin yana da yaro daya mai sunan Ibrahim ,suna kiransa da akram da yake sunan mahaifinsa garesa ..
mukarama ta tagama karatunta na gaba da primary, ta zama cikakkiyar budurwa sosai gata da kyau da gogewa da iya tsara kwalliya ,cikin wannan lokacin ishaq abokin Muhammad wanda ya kasance abokin kasuwancinsa ne ya dawo daga kasar maleshia akan harkan kasuwanci da karatunsa .
ishaq hadadden matashi saurayi ne tsayaye mai zati da haiba uwa uba naira ta zauna ajikinsa asalinsa dan Kano ne amman babu inda baya shiga adalilin kasuwanci.
wata rana ya kawowa Muhammad ziyara,inda Muhammad yace "mukarama ta kawowa abokinsa abun motsa baki,tashigo parlour'n cike da natsuwa da kamewa uwa uba kunya, ai kuwa ishaq yana d'aura idanunsa akanta yarasa tsukuni amman dayayi wani tunani sai yayi saurin kawar da abinda yaji akanta, ta ajiye tire ishaq yace "ga leda nan ta wuce dashi tsarabarsu ce aciki, sam mukarama taki d'auka, ya d'auka ya mika mata nan ma taki amsa yace" haba kanwarmu ina ganinki mai kalar wayyayu, a wannan zamanin yaushe ake kunya hk?
mukarama ta juya akunyace zata fice daga parlour'n, 'yar drya Muhammad yayi yace "to in kin shiga ki turomin hajara kawai ,tana fita ishaq yace "amman wannan wani irin kunya ce hk sai kace ba yar zamani ba?
alhj Muhammad yace" ina ruwan mukarama haka Allah yayita komai nata sai ta had'a da kunya yarinya ce mai tsananin kawaici babu ruwanta.
yace "da kyau hk nake son naga mace nada kawaici da alkunya a dukkanin al'amuranta da ganin kanwar tamu mijinta ya dace kwarai ya fad'i hk saboda tunaninsa ko tana da aure.
alhj Muhammad yace"kuma ka gani bata da miji har yanzu bata tsaida miji ba karatu take domin ina da burin akanta,ina son na ingata rayuwarta da karatu boko domin a dama wannan duniyar daita, shiyasa duk masu kawo hari nake katse masu hanzari har sai ta gama, yanzu haka tana matakin diploma .
ishaq ya d'an dubesa a razane domin yasan asaninsa mutane karkara haka ,basu fiyye barin yaransu su jima hk batare da yin aure ba ....
"gsky abokina kayi nmj k'ok'arin gurin ingata rayuwarta ,yanzu dai kace babu kowa akasa masu neman aurenta?
"babu kowa ina suka ga fuska, ai sai sunga fuska tukun zasu zo, ni dai burina tayi karatu mai zurfi ta yadda zata taimaki al'umma da ita kanta, nan dai suka bar zance suka shiga hirar kasuwanci dayake daman harkar kasuwamci ne ta had'asu har suka zama abokai, acikinsu duk wanda wata harka tashigo hannunsa daya san za'a samu alheri y kan janyo dan'uwansa ciki, su samu alkhairi tare kasancewar dukansu ba masu kyashi ko bakinciki bane ,kowa yana k'aruwa da kowa suna harkar arziki tare gwanin sha'awa.
tunda ishaq yakoma gida sai ya kasa samun sukunin zuciya duk yadda ya runtse idanunsa mukarama yake gani tana yi masa gizo ,haka nan abin mamaki jiyayi gbdy ya tsinci kanshi da matsanancin kaunar mukarama ,ganin dayayi mata ya gigita kwalkwaluwarsa ,sosai yarinyar ta rikitashi ,ya rikice akanta har tunaninta na neman hanashi sukuni yin barci, shi kansa sai juya al'amarin yake aransa yadda farat daya ya gigice akanta gashi dan'uwanta na da buri akanta, dan hk ya danne abun aransa yacigaba da hakuri ,haka soyayar mukarama yayita cinsa arai har sai da aka samu wasu yan watani.
************
ran nan dai ishaq ya kasa hakuri adalilin soyayyar mukarama da kullun take sake huda kahon zuciyarsa, dan hk a zaunen da yake agaban mahamud yasoma maganar yadda yake son mukarama.
mahamud yayi shr yana sauraron abokinsa har yagama zayyana masa irin kaunar dayake yiwa mukarama,Muhammad yace "naji dadi kwarai kuma ina matukar farinciki da wannan bayani naka ,sanin kanka ne kafi karfin komai agurina ,zai yi wuya ka nemi wani abu a wurina na hanaka, musamman ma irin wannan alfarma ta aure, to amman akwai wani hanzari ba gudu ba kmr yadda kasani, bazan aurawa mukarama mijin da bazai barta tacigaba da karatunta ba, matsawar ka amince zata cigaba da karatunta agidanka shikenan na amince kaje ka nemi yardarta matukar ta amince da kai zan aura maka ita.
ishaq ya sauke naunauyen ajiyar zuciya kana yace "wannan ba wata matsala bace ni kaina har yanzu akan karatu nake kasan da haka ,domin lamarin kasuwancinmu na bukatar ilimi mai zurfi,bugu da kari ilimin mace nada matukar mahimmanci arayuwa.
"haka ne kam Allah yasa mu dace kana iya turo magabatanka idan ta amince , ishaq yace "ameen had'e dayiwa abokinsa godiya " domin sosai yaji dadin lafazinsa mahamud na gama fadar hk ya bari parlour'n.
ishaq ya nemi ganawa da mukarama ,byn tashigo parlour'n suka dan yi shru kad'an sannan yakira sunanta "ko kinsan zuwan nawa na yau dominki ne sabanin sauran lokuta?
ta d'an kalleshi cikin natsuwa, yayinda ta zuba masa idanu tana kallonsa da sauraren abinda zaice dan gabad'aya zuciyarta ta matsu da son jin abinda ke cin ransa akanta, domin itama tana jin wani abu a game dashi .
yacigaba "hakika mukarama dazaki min alfamar dana dan gutsara miki abinda ke cin raina a game dake, Allah yasamin tsananin kaunarki tun ranar farko dana d'aura idanuna akanki dayake nasan ba aure yayanki zai miki a wannan lokacin ba sai nayi kokarin danne sonki cikin zuciyata har sai yanxu ,a yanzu dai ina gabatar miki da kaina amatsayin wanda yake son aurenki amman menene ra'ayinki akaina ?
mukarama dai tayi shiru saboda batasan amsar dazata bashi ba, domin mutumin yana yi mata kwarjini ganin bata da niyyar bashi amsa yace "haba mukarama ya kikayi shr ai gara kiyi magana shi sha'anin aure ai ba'a yinsa da wasa zan so jin ta bakinki koda bakya sona barema bana fatan haka nafi son kiyi min alfarma bisa soyayya kar ma ki tsaya duba alaka don ba itace tasani sonki ba.
" kyawawan halaiyenki da dabi'unki na kirki ne suka janyo zazzafar kaunarki ,ki taimawa rayuwar wannan tsohon tuxuron ki aureshi domin idan kika ki aurensa ina tabbatar miki hk zai k'arasa sauran rayuwarsa batare daya ajiye iyali ba.
mukarama ta cigaba da yin shiru sai dai wannan karon kanta na sunkuye ,murmushi yayi saboda sanin halinta na kunya "haba zuciyar ishaq ki dan yi min magana ko naji dadi "tayi dariya amman batace komai ba yace"kenan dai ana son ishaq ya hakura," mai yiwuwa ina da wani abun da baza a soni dominsa ba?
sai a lokacin ta girgiza kanta, yace "ni kam muddin ba magana ki kai ba, gani nake ban canci asoni ba ,shi yasa kika barni da kokon barana a hannu, ai sauran maneman ba hk ake musu ba, ko kuma ko dan anga ni babban yaya ne kike ganin nayi miki tsufa?
maganarsa ta bata dariya har ta sa ta d'ago kanta da sauri suka dubi juna sannan tace "ko kad'an ba haka bane, ni dai aguna baka da wani aibu da kowace irin mace zata kika ,sai dai abunda nake son kagane ban taba yankewa kaina hukunci ba sai dai yayana ya yanke min.
"idan ta wannan bangare ne mugama magana da yayanki har ya amince har ma da sharadinsa nason ki cigaba da karatunki byn aurenmu, na kuma ji na gani na amince da hakan ,saboda ina matsanamcin sonki "duk da haka ni dai nayiwa kaina alkwarin komai zanyi sai da amincewarsa.
"da kyau kinga wannan biyayyar taki tana daga cikin abubuwan dayasa na kamu da sonki tunda kin tabbatar zabin d'anuwanki shine zabinki, a she dai naci babu hamayya kenan, domin na tabbatar d'anuwanki ba zai iya zaba miki wani fiyye dani ba.
"amman duk da hk xan baki lokaci kije kuyi shawara da matar yayanki tunda itace ta hannun damarki, dan ta abokina shi bana jin komai domin shine yace in nemi soyayya agurinki domin yana son baki cikakkiyar yanci shiyasa nake ganin yanzu shawara ta rage keda hajara babu ruwan aminina ,dan ko yau muka daidaita gobe ma yana iya d'aura mana aure.
ta dan fad'ad'a murmushinta "shikenan Allah yayi mana zabi mafi alkhari "yauwa masoyayyita abinda nake son ji kenan daga gareki, domin zabin Allah shine mafi alkhairi a gurinmu, gbdy dai ishaq ya gama kashewa mukarama jiki da salon soyayyarsa wanda sukayi tasiri a zuciyarta.
sosai yasamu matsugunni agurinta ,byn sunyi sallama tare da yi mata alkwarin zai dawo wani sati domin jin shawarar data yanke, kafin su rabu sai da yayi mata alkhairi mai yawa wanda kunya ta hanata kar'ba ,sai daya takurata sosai sannan ta amsa game da yi masa godiya tashige ciki, tana shiga Kai tsaye d'akin hajara tashiga domin ta fesa mata labari da bata ganta cikin parlour'n ba sai ta bita uwar daka ta isketa kwance ita da akram akan lafiyayyen gadonta suna ta sharar bacci cikin nishadi ta dan ja ta tsaya tana jan tsaki .
"ke kam aunty hajara kin cika so baccin tsiya ta fad'i hkn a fii yayinda tasa hannu tana girgizata, ta d'an motsa kadan tare da rungume d'anta ajikinta batare da ta bud'e idanunta ba ta sake komawa bacci abinta .
a hanzarce mukarama ta maka mata duka, hajara a firgice ta d'an bud'e idanunta ganin mukaramaa tsaye akansu tace "kai d'an Allah mukarama in banda d'aukar haki ki barmu muyi baccinmu .
mukarama cikin zolaya tace "mijinki yace na taimaka na tasheki sai nayi laifi?
hajara da sauri ta watseke tare da tashi, zaune har da d'an murmushinta, mukarama ta kwashe da dry "uhm yar dadi miji daga jin zance miji kin wani wartsetake to karya ne bashine yake nemanki ba ni nake son mgn dake hajara ta d'an kai mata duka "kyaji da karyarki ke daman babu damar kiga mutun yayi bacci sai kin tasheshi .
mukarama tace "ai ina ganin akan shegen baccin nan naki sai nayi miki kishiya in tura amarya d'akin yayana kina nan kina shirgar bacci.
"haba dan Allah kin isa ai dagani babu kari ai ni nafi karfin amarya.
"kiyi cika bakinki kigama zanyi maganinki .
suka fashe da drya .
kiyi driyarki ahankali karki tasar min da yaro inji cewar mukarama.