Sashe 61
Kura Da Fatar Akuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba su wani ɗauki tsawon lokaci ba suka iso garin Abuja, saboda shi yake tuƙin kuma ya ƙure maneji.
Ba su yi mamakin kyan gidan da tsarinsa ba domin sun san wace ce Halima uwa ba da mama.
A falo aka ije su wanda ko ruwa ba su sha ba Huzaifah ya duƙa yana kuka a gaban dad.
"Dad Allah dad, kar ku raba ni da ita wallahi ina sonta ban taɓa jin son wata 'ya mace kamar ta ba, and we are compatible, zan barta ta yi duk a abin da take so, ba zan zamo azzalimi ba."
Sai ya yi matuƙar ba shi tausayi matuƙar gaske har yana jin ƙwallah na shirin zubo masa, yayin da momeries na tsawon shekaru suka dawo masa wanda ya fuskanci irin wannan ranar da ya sha tozarcin da ba a taɓa masa.
Sosai ya yi na'am da shi saboda duk da hutu da waye da gata, da aka ƙawata rayuwarsa bai hana shi zama cikakken namiji wanda kowa ne uba zai yi burin 'yarsa ta aura. Uwa uba ga kyau da tashen ƙuruciya da natsuwa, musamman yadda yake masa maganar yana hawaye, ya san idan ya aureta zai kula masa da ita saboda tsananin sonta da yake.
Hannunsa ya kama ya riƙe yana shafa bayansa wanda ganin hakan iyayensa suka fara murna suna ganin alamun nasara...
"Calm down, É—an samari. Matsalar ba daga ni ba saboda da ace ni ne ayau zan aura maka Janah, don n yaba da hankalink..."
Mom ce ta katse maganar da yake yi wacce ta yi sallama ta shigo, saboda tun da ta sanar masa ya kira ta.
Sosai suka yi gaisuwar mutunci da girmamawa, bayan sun gama gaisuwa irin ta su ta 'yan boko masu ji da kansu da aljihu, sai mahaifin Huzaifah ya yi gyaran murya ya ce,
"Huzaifah ya sanar mana da soyayyar da yake yi wa 'yarku. Sai dai, ya gaya mana ita yarinyar tana son ta gama karatunta, kuma shima yanzu haka waje za shi ya yi phd ɗinsa, amma kwasam yau ta kira shi take sanar mishi da za a yi mata auren dole. Wanda ba mu yi ƙasa a gwuiwa ba muka zo neman iri tare da ba wa wancan haƙuri tun da tana son Huzaifah."
Shiru suka yi na 'yan sakwanni babu wanda ya ce uffan sai mom ta yi gyaran murya ta ce,
"Eh haka ne wallahi da yake ɗan yayana ne za a haɗa auren muna baku haƙuri yaje ya nemi wata."
"No mom, don Allah karki ce haka ina sonta ba zan iya auren wata in ba ita ba. Ki bani ita na yi miki alƙawarin zan riƙeta duk yadda kike so, amma don Allah don annabi kar ku raba ni da ita." Ya ƙarshe maganar cikin muryar kuka tare da ƙarasowa kusa da ita ya duƙa ya ɗaga hannunsa yana roƙonta.
Babu wansa bai ba shi tausayi ba shiru ta yi tana tuannanin yadda za ta ɓullo ma lamarin, saboda Huzaifah ya yi mata ita kanta za ta so ya aureta. A wancan lokacin da ta kawo wanda take so in har da ba shi aka aura mata shi ba Allah kaɗai ya san halin da za ta shiga.
"Yaran ba so suke ba mahaifiyata ta tilasta hakan, bari na kira muku ita in har kuka shawo kanta shikenan."
"Za ta amince Hajiya Baaba ba ta da matsala, alokacin da naje gidanta hannu biyu-biyu ta karɓe ni." Ya faɗa cikin murna domin shi tunaninsa har ya mallaki Jannah ya gama duba ga yadda ta yi ta nan nan da shi.
Mom kuwa miƙewa ta yi ta shige ciki a ranta tana fatan Allah ya sa ta amince, wataƙila don bai san halinta bane ya sa ya furta haka, amma Hajiya Baaba kura ce da fatar akuya."
Ta same ta a cikin É—akinta tana ta haÉ—a kayanta tana gungunai. Ganin ta shigo ya sa ta haÉ—e rai ba ta ce mata komai ba ta ci gaba da haÉ—a kayanta."Hajiya Baaba shirin tafiyar ake yi?"
"Eh to mene ne amfanin zamana a gidan da ba a da buƙata ta? Kullum ba ki da lokacina ai gara na koma gidan Muhammadu in ya so yanka ni matarsa za ta yi inna mutu baki da asara. Da ninyar zama na zo amma ba zai yi ba."
"Haba Hajiya, ina iyakan ƙoƙarina fa aiki ne suka sha mini gab.."
"Ki je ki kashe kanki akan al'umma ke kika sani."
"Ni ba wannan ya kawo ni ba muna da baki a guest room."
"Mene ne haka?"Ta tambayeta a ƙubule tana mata mugun kallo.
Dafe kanta ta yi sam ta manta ta yi turancin."Ɗakin baƙi nake nufi"
"To shine sai an nuna mini iyaka na rashin turanci?" Tsaki ta yi ta ci gaba da haÉ—a kayanta ba tare da ta kalle ta ba.
"Hajiya jiranki fa suke yi." Ta faɗa cikin ƙosawa wanda ta taso mata a harzuƙe.
"Su waye ne? Wa na sani a garin Abuja da za su zo mini? Ki fita idanuna ki barni na haɗa kayana, na koma Zariya tun kafin na taɓa miki halina."
"Ni dai don Allah ki zo ki gannin ma idanunki." Ta ce tana ƙoƙarin ficewa.
Tsaki ta ƙara saki kamar ba za ta je ba komai ta tuna sai ta ije jakar da take shiryawa ta fice.
Jannah dake laɓe a bayan labule don tun da suka shigo ta zo gurin ta laɓe, tana addu'ar Allah ya sanya kunnuwanta su ji mata Hajiya Baaba ta amince, wanda za ta sa a sanya rana a gurin don kar ta canza shawara.
Hajiya Baaba da ta so za ta shige ɗakin sai ta hangi ƙafafunta a basu shige ba. Yaye labulen ta yi tana kallonta wanda ta fara mazurai.
"Uban me kike yi a gurinan? Yaushe kika zama munafuka kike laɓe?"
"Ban sani ba kuma ba ruwanki da ni." Ta ce a hankali kuma cikin tsiwa.
Jikinta ya bata bakin na ta ne ko iyayen Huzaifah. Wani rashin mutunci ta saka a ranta don ko maka fa madina za su ba ta ba za ta fasa auren nan ba.
"Iyayen Huzaifah kika ɗauko mini ko? To ko shugaban Ƙasa kika kawo bai isa yasa na janye ƙudirna ba. Shashasha kawai."
Ta saki labulen tana mata mugun kallo wanda ba ta ce komai ba saboda da ƙarfi take maganar, kuma ta san tana yi ne don mutane suji.
Da sallama ta shiga falon yayin da ta yi fiƙi-fiƙi da ido sannan ta haɗe rai tamkar an aiko mata da mala'ikan mutuwa.
Zama ta yi a hamshaƙe tana masa gaisiwar da iyayen Huzaifah suka yi mata a gajarce do ko na Huzaifah da lafiya kawai ta masa ta sha kunu.
Jikinsu ne ya yi sanyi ganin yadda ta karɓe su.
"Hajiya Baaba don Allah ki taimaka kar ki raba ni da Jannah wallahi ina sonta zan iya mutuwa in ban sa.."
"Kai ko Huzaifah kake ko wa? Wane irin rashin kunya kake da shi? A gaban manya kake maganar son da kake ma mace? To ai ni ban ga amfanin zuwan iyayenka ba matuƙar kai za ka yi magana." Ta faɗa tana salati da tafa hannu sai ka ce wanda ya aikata mugun zunubi
Huzaifah sai ya cika da matuƙar mamaki, take ya gane ita ɗin kura ce da fara kauya, domin lokacin da ya je gidanta ba haka ta karɓe shi ba. Jikinsa a sanyaye ya koma ya zauna lokaci guda hawayen da yake ƙoƙarin mayarwa suka wanke masa fuska.
Ganin hakan, sai jikinsu ya ƙara matuƙar sanyi jin abin da ta ce, don ba su ga abin aibu ba mahaifinsa ne ya yi gyaran murya.
"Ki yi haƙuri kin san sha'anin yara da abin da suke so. Ki taimaka mana ki bamu auren Jannah za ki yi alfahari da hakan."
"Haka ne, ai dama ban ce ba zan yi ba, amma gida bai ƙoshi ba ina za a bawa dawa? Adamun da zan haɗa shi aure da ita shine kawai zai iya zama da ita domin kura ce da fatar akuya. Kuma tunani juya Adamun ya aura in har ba aure na yi masa ba, yadda matarsa ta mallake shi ba zai iya ƙara aure ba ni kuma ina son kafin na mutu na aurar da yarsa."
"Hajiya magamar da ya kawo shi daban da wanda kike masa. Yaran suna son junansu don Allah karki raba so.."
"Sannu Laila da Majnun! Na gaya maka Jabiruu in ima magana kana saka mini baki wallahi sai na yi maka tonon silili, saboda ba ka da ta ido har baki kake da shi."
"Allah ya ba ki haƙuri." Ya ce tare da kama bakinsa bai ƙara cewa komai ba yana kallon mom, da ta dafe kai tana dana-sanin kiranta, yayin da kunya ta kamata kamar za ta nitse, jin ta ɗauko magana daban.
"Da haƙurin ta mutu sadakar nawa ka bani?" Bai tanka mata ba ya yi shiru.
Juyawa ta yi ta kalli iyayen Huzaifah aure da na ƙulla babu uban da ya isa ya sa a fasa ko da iyayensu.
"Ɗanku ya je ya nema a waje ga matanan birjik sai wanda ya zaɓa, don ma bai san halinta bane har yake asarar hawayensa da kun san ita ɗin kura ce da fatar akuya ba za ku nema wa ɗanku ba. Ai Jannah sai Adamuu shine daidai da ita."
Jin abin da ta furta Jannah dake kuka abayan labule ba ta san lokacin da ta banko cikin falon da ƙarfi ba.
"Ina sonsa kuma shine wanda nake jin zan iya rayuwa da shi. Na rantse babu wanda ya isa ya raba ni da shi, in ba haka ba zan kashe kaina
"Shashasha! Wa ya damu don kon mutu. Kafin ke mutane nawa suka mutu akan soyayya kuma har yau ba a daina raba masoya. Ni da kaina iya siyo miki gubar kici ki mutu kuma ba zan fasa aura miki shi ba sai ku yi rayuwar auren a kiyama." Ta ce tare da juya ta kallo iyayensa ta ci gaba da cewa,
Kun ga ku tashi ku fice mini daga gidan 'ya kuka wani zauna É—ika-É—ika daku kun cika kujera."
Wani irin gigicecen ƙara ya saki ta nufi Huzaifah ta faɗa jikinsa.
Ba su yi mamakin kyan gidan da tsarinsa ba domin sun san wace ce Halima uwa ba da mama.
A falo aka ije su wanda ko ruwa ba su sha ba Huzaifah ya duƙa yana kuka a gaban dad.
"Dad Allah dad, kar ku raba ni da ita wallahi ina sonta ban taɓa jin son wata 'ya mace kamar ta ba, and we are compatible, zan barta ta yi duk a abin da take so, ba zan zamo azzalimi ba."
Sai ya yi matuƙar ba shi tausayi matuƙar gaske har yana jin ƙwallah na shirin zubo masa, yayin da momeries na tsawon shekaru suka dawo masa wanda ya fuskanci irin wannan ranar da ya sha tozarcin da ba a taɓa masa.
Sosai ya yi na'am da shi saboda duk da hutu da waye da gata, da aka ƙawata rayuwarsa bai hana shi zama cikakken namiji wanda kowa ne uba zai yi burin 'yarsa ta aura. Uwa uba ga kyau da tashen ƙuruciya da natsuwa, musamman yadda yake masa maganar yana hawaye, ya san idan ya aureta zai kula masa da ita saboda tsananin sonta da yake.
Hannunsa ya kama ya riƙe yana shafa bayansa wanda ganin hakan iyayensa suka fara murna suna ganin alamun nasara...
"Calm down, É—an samari. Matsalar ba daga ni ba saboda da ace ni ne ayau zan aura maka Janah, don n yaba da hankalink..."
Mom ce ta katse maganar da yake yi wacce ta yi sallama ta shigo, saboda tun da ta sanar masa ya kira ta.
Sosai suka yi gaisuwar mutunci da girmamawa, bayan sun gama gaisuwa irin ta su ta 'yan boko masu ji da kansu da aljihu, sai mahaifin Huzaifah ya yi gyaran murya ya ce,
"Huzaifah ya sanar mana da soyayyar da yake yi wa 'yarku. Sai dai, ya gaya mana ita yarinyar tana son ta gama karatunta, kuma shima yanzu haka waje za shi ya yi phd ɗinsa, amma kwasam yau ta kira shi take sanar mishi da za a yi mata auren dole. Wanda ba mu yi ƙasa a gwuiwa ba muka zo neman iri tare da ba wa wancan haƙuri tun da tana son Huzaifah."
Shiru suka yi na 'yan sakwanni babu wanda ya ce uffan sai mom ta yi gyaran murya ta ce,
"Eh haka ne wallahi da yake ɗan yayana ne za a haɗa auren muna baku haƙuri yaje ya nemi wata."
"No mom, don Allah karki ce haka ina sonta ba zan iya auren wata in ba ita ba. Ki bani ita na yi miki alƙawarin zan riƙeta duk yadda kike so, amma don Allah don annabi kar ku raba ni da ita." Ya ƙarshe maganar cikin muryar kuka tare da ƙarasowa kusa da ita ya duƙa ya ɗaga hannunsa yana roƙonta.
Babu wansa bai ba shi tausayi ba shiru ta yi tana tuannanin yadda za ta ɓullo ma lamarin, saboda Huzaifah ya yi mata ita kanta za ta so ya aureta. A wancan lokacin da ta kawo wanda take so in har da ba shi aka aura mata shi ba Allah kaɗai ya san halin da za ta shiga.
"Yaran ba so suke ba mahaifiyata ta tilasta hakan, bari na kira muku ita in har kuka shawo kanta shikenan."
"Za ta amince Hajiya Baaba ba ta da matsala, alokacin da naje gidanta hannu biyu-biyu ta karɓe ni." Ya faɗa cikin murna domin shi tunaninsa har ya mallaki Jannah ya gama duba ga yadda ta yi ta nan nan da shi.
Mom kuwa miƙewa ta yi ta shige ciki a ranta tana fatan Allah ya sa ta amince, wataƙila don bai san halinta bane ya sa ya furta haka, amma Hajiya Baaba kura ce da fatar akuya."
Ta same ta a cikin É—akinta tana ta haÉ—a kayanta tana gungunai. Ganin ta shigo ya sa ta haÉ—e rai ba ta ce mata komai ba ta ci gaba da haÉ—a kayanta."Hajiya Baaba shirin tafiyar ake yi?"
"Eh to mene ne amfanin zamana a gidan da ba a da buƙata ta? Kullum ba ki da lokacina ai gara na koma gidan Muhammadu in ya so yanka ni matarsa za ta yi inna mutu baki da asara. Da ninyar zama na zo amma ba zai yi ba."
"Haba Hajiya, ina iyakan ƙoƙarina fa aiki ne suka sha mini gab.."
"Ki je ki kashe kanki akan al'umma ke kika sani."
"Ni ba wannan ya kawo ni ba muna da baki a guest room."
"Mene ne haka?"Ta tambayeta a ƙubule tana mata mugun kallo.
Dafe kanta ta yi sam ta manta ta yi turancin."Ɗakin baƙi nake nufi"
"To shine sai an nuna mini iyaka na rashin turanci?" Tsaki ta yi ta ci gaba da haÉ—a kayanta ba tare da ta kalle ta ba.
"Hajiya jiranki fa suke yi." Ta faɗa cikin ƙosawa wanda ta taso mata a harzuƙe.
"Su waye ne? Wa na sani a garin Abuja da za su zo mini? Ki fita idanuna ki barni na haɗa kayana, na koma Zariya tun kafin na taɓa miki halina."
"Ni dai don Allah ki zo ki gannin ma idanunki." Ta ce tana ƙoƙarin ficewa.
Tsaki ta ƙara saki kamar ba za ta je ba komai ta tuna sai ta ije jakar da take shiryawa ta fice.
Jannah dake laɓe a bayan labule don tun da suka shigo ta zo gurin ta laɓe, tana addu'ar Allah ya sanya kunnuwanta su ji mata Hajiya Baaba ta amince, wanda za ta sa a sanya rana a gurin don kar ta canza shawara.
Hajiya Baaba da ta so za ta shige ɗakin sai ta hangi ƙafafunta a basu shige ba. Yaye labulen ta yi tana kallonta wanda ta fara mazurai.
"Uban me kike yi a gurinan? Yaushe kika zama munafuka kike laɓe?"
"Ban sani ba kuma ba ruwanki da ni." Ta ce a hankali kuma cikin tsiwa.
Jikinta ya bata bakin na ta ne ko iyayen Huzaifah. Wani rashin mutunci ta saka a ranta don ko maka fa madina za su ba ta ba za ta fasa auren nan ba.
"Iyayen Huzaifah kika ɗauko mini ko? To ko shugaban Ƙasa kika kawo bai isa yasa na janye ƙudirna ba. Shashasha kawai."
Ta saki labulen tana mata mugun kallo wanda ba ta ce komai ba saboda da ƙarfi take maganar, kuma ta san tana yi ne don mutane suji.
Da sallama ta shiga falon yayin da ta yi fiƙi-fiƙi da ido sannan ta haɗe rai tamkar an aiko mata da mala'ikan mutuwa.
Zama ta yi a hamshaƙe tana masa gaisiwar da iyayen Huzaifah suka yi mata a gajarce do ko na Huzaifah da lafiya kawai ta masa ta sha kunu.
Jikinsu ne ya yi sanyi ganin yadda ta karɓe su.
"Hajiya Baaba don Allah ki taimaka kar ki raba ni da Jannah wallahi ina sonta zan iya mutuwa in ban sa.."
"Kai ko Huzaifah kake ko wa? Wane irin rashin kunya kake da shi? A gaban manya kake maganar son da kake ma mace? To ai ni ban ga amfanin zuwan iyayenka ba matuƙar kai za ka yi magana." Ta faɗa tana salati da tafa hannu sai ka ce wanda ya aikata mugun zunubi
Huzaifah sai ya cika da matuƙar mamaki, take ya gane ita ɗin kura ce da fara kauya, domin lokacin da ya je gidanta ba haka ta karɓe shi ba. Jikinsa a sanyaye ya koma ya zauna lokaci guda hawayen da yake ƙoƙarin mayarwa suka wanke masa fuska.
Ganin hakan, sai jikinsu ya ƙara matuƙar sanyi jin abin da ta ce, don ba su ga abin aibu ba mahaifinsa ne ya yi gyaran murya.
"Ki yi haƙuri kin san sha'anin yara da abin da suke so. Ki taimaka mana ki bamu auren Jannah za ki yi alfahari da hakan."
"Haka ne, ai dama ban ce ba zan yi ba, amma gida bai ƙoshi ba ina za a bawa dawa? Adamun da zan haɗa shi aure da ita shine kawai zai iya zama da ita domin kura ce da fatar akuya. Kuma tunani juya Adamun ya aura in har ba aure na yi masa ba, yadda matarsa ta mallake shi ba zai iya ƙara aure ba ni kuma ina son kafin na mutu na aurar da yarsa."
"Hajiya magamar da ya kawo shi daban da wanda kike masa. Yaran suna son junansu don Allah karki raba so.."
"Sannu Laila da Majnun! Na gaya maka Jabiruu in ima magana kana saka mini baki wallahi sai na yi maka tonon silili, saboda ba ka da ta ido har baki kake da shi."
"Allah ya ba ki haƙuri." Ya ce tare da kama bakinsa bai ƙara cewa komai ba yana kallon mom, da ta dafe kai tana dana-sanin kiranta, yayin da kunya ta kamata kamar za ta nitse, jin ta ɗauko magana daban.
"Da haƙurin ta mutu sadakar nawa ka bani?" Bai tanka mata ba ya yi shiru.
Juyawa ta yi ta kalli iyayen Huzaifah aure da na ƙulla babu uban da ya isa ya sa a fasa ko da iyayensu.
"Ɗanku ya je ya nema a waje ga matanan birjik sai wanda ya zaɓa, don ma bai san halinta bane har yake asarar hawayensa da kun san ita ɗin kura ce da fatar akuya ba za ku nema wa ɗanku ba. Ai Jannah sai Adamuu shine daidai da ita."
Jin abin da ta furta Jannah dake kuka abayan labule ba ta san lokacin da ta banko cikin falon da ƙarfi ba.
"Ina sonsa kuma shine wanda nake jin zan iya rayuwa da shi. Na rantse babu wanda ya isa ya raba ni da shi, in ba haka ba zan kashe kaina
"Shashasha! Wa ya damu don kon mutu. Kafin ke mutane nawa suka mutu akan soyayya kuma har yau ba a daina raba masoya. Ni da kaina iya siyo miki gubar kici ki mutu kuma ba zan fasa aura miki shi ba sai ku yi rayuwar auren a kiyama." Ta ce tare da juya ta kallo iyayensa ta ci gaba da cewa,
Kun ga ku tashi ku fice mini daga gidan 'ya kuka wani zauna É—ika-É—ika daku kun cika kujera."
Wani irin gigicecen ƙara ya saki ta nufi Huzaifah ta faɗa jikinsa.