← Book details Kura Da Fatar Akuya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 5 OF 79

Sashe 5

Kura Da Fatar Akuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

Figigiyar rigar baccin dake jikin ta, ta cire sannan ta faɗa toilet ta ɓata lokaci tana wanka kafin ta fito ɗaure da sky blue tawu, kanta a jiƙe ya yin da ta ɗora ɗan ƙaramin towel tana tsane kanta.
Hand dryer ta ɗauka sannan ta kunna socket ta kunna tana busar da kanta, zuciyar ta ke ɗauke da tsananin damuwa wanda kana kallon face ɗin ta you can tell she’s moody.
Bayan ta kammala shiryawa cikin wata rigar pink mai kyau, ta ɗauki ribon tare da ɗaure kanta. Wayarta ta ɗauka tare da janyo ƙofar ta ta rufe.
A falo ta zauna kan doguwar kujera tare ta kunna kallo ta É—auki remote ta koma ta zauna. Ganin labaren ake yi sai ba ta canza tasha ba ta ije remote É—in a kan stool ta fara danna wayarta.
Mom ce ta fito sanye da wata fitinannniyar doguwar riga wace tasha ado sai. Siririn É—ankwalin rigar ta yi rolling É—in sa a kanta, sannan ga jakarta da takalmin ta mai azababben kyau.
Jannah ta yi mata kallon uku tara duk da ta yi mata kyau sosa, domin ita kanta ta san she’s so beautiful and dashing. She looked elegant and so charming. Ga shi tana sa masifar tsafta sam ta tsani ƙazanta.
Mace ce da ba ta kula da shekarunta ko ta haifi Jannah in tana abu sai ta ba ka mamaki don jin ta take tamkar 'yar shekaru sha takwas. So, she could categorize herself as mace classical wanda a dalilin hakan ta ɗauka take gara mahaifinta kamar ƙwallo duk da cewar shi ma ba baya ba.
Ƙarasowa ta yi cikin tafiyar taƙama tana waya, ta zauna a gefenta tare da ci gaba da wayar, wanda hakan, ta yi matuƙar tsana domin sai ta ɗauki kusan awaya tana yi.
Hakan ta faru, don ta ɗauki tsawon lokaci har ta gaji ta ɗan saki siririn tsaki, tare da janye hannun ta da ta rike za ta bar gurin, ganin hakan ya sa ta sallami mutum ba don ta gama ba bayan ta riƙe hannunta, yarda ba zata iya fisgewa ba.
"Morning, sweetheart. You look pretty." Ta ce tare da ware hannunta da nufin ta rungume ta, amma sai ta matsa gefe ta ƙi amsa gaisuwar. "Jannah na gaya miki."
"Mom you constantly nagging, no matter what you do. Please bana so, you are provoking me."
Ta ɗan murmusa jin abin da ta ce sai ta ƙara rungume ta duk da ba ta dake zuɓɓurawa ta ja leɓenta tare da kama hancin. "Shiryaya kawai! kina ba ni mamaki, ban taɓa ganin 'yar da take against ɗin mahaifiyarta ba, but you do..."
"You caused it. Kece kika sa nake miki hakan, amma kin san babu wacce na ke ƙauna da so kamar ke, but I don't know why you do that to me and me father."
Ta katse ta tana fadin haka. "See, your dad deserves it, and I'm tired of this whimsical attitude of yours sai na dawo. Watch your mouth."
Sai ta fusata ganin ba ta da ninyar canzawa daga munanan É—abi'un da take yi cikin muryar kuka ta furta bayan ta sha gabanta.
"I think you should go for a relationship therapy, you need that cos you have no idea ho…"
Wasu kyayawan mari ta sauke mata a fuskarta cikin ƙunar rai. "Ki san kalaman da za ki rinƙa gaya mini a matsayina ma mahaifiyarki, from now on I won't take your shit anymore."
Jannah ta fusata idanunta suka kawo ruwa sai ta sanya ƙara mai razanar ta tokare ƙofar da za ta wuce.
"Ba zan ƙara zama dake ba, ki mai da ni gurin Hajiya Baaba, na san za ta ba ni kulawa fiye dake. Mom, I can't stand your attitude much longer." Sai kuma ta yi shiru tare da jan majina tana ƙara sakin wan kukan ta ɗorawa da ce wa, "Idan kuma ki ka ƙi, kin ji na rantse miki, I will kill meself! I think suicide would be better for me than living in this hell you call a family."
Lamarin sai bata matuƙar mamaki, ta yi zuru tana kallon ta yadda take faɗin kalamai mara sa daɗin ji. Idanunta suka kawo ruwa, sai ta fara tunanin tarbiya ce ba ta iya ba, ko injiniya ya yi nasarar raba ta da 'yarta?
Ba tare da ta furta mata kalami ta É—auki jakarta ta ture ta tare da fita daga falon idanunta na zubar hawaye daidai lokacin da take cewa, "I will get a visa, I have money on me."
Da sauri Rose da take kicin tana sauraron hayaniyar da suke yi ta fito tare da rungume ta "Please, Jannah, take easy; it’s okay." Sai ta kara sakin kuka tare da ƙara rungume ta.
"Ba ta sona! Mace ce mai son dukiya da duniya. Shi ya sa ba ta barina na huta kullum cikin karatu, saboda na yi ilmi na tara dukiya. Tir da dukiya irin na ta, wacce ta sa muka kasa samun kulawarta sai da ta ba wa duniya."
"Sorry." Ta kara ce mata duk da ba fahimci mai ta faÉ—i ba tare da kamata suka shiga É—aki.
Da sauri Rose ta buɗe wardrobe nata ta ɗauko mata pills ta ɓalle tare da mika mata, amma sai ta karɓi na hannunta ta ƙara da guda uku ta watsa a bakinta.
Zare idanunta ta yi, sai juma ta kasa cewa komai, tana girgiza kanta kamar ƙadangaren kutu. Sosai take ganin sakarcin mom da ta kasa gane 'yarta tana shan maganin depression and anxiety. Koda yake she would not be surprised domin ba ta ba ta lokacinta ba balantana ta fahimci haka.
Ko da mom ta shiga mota kusan minti goma ta kifa kanta a sitiyarin motar hawaye ke zuba a fuskarta, bayan ta ba da umurnin kar a bar ta ta fita ko ƙofar gida.
"You are so insolent to me. Why?" Ta furta cikin tsananin ɓacin rai.
Da ta dawo aiki ko kofarta ba ta kalla ba, saboda haushin ta da take ji, amma tunaninta yana kanta, musamman da Rose ta gaya mata ta ƙi cin abinci.
Dad ne kawai zai iya shawo kanta, don haka ba ta damu kanta da ta je gurin ta ba ta yi kwanciyarta. Haka kuwa aka yi don sai da ya shafe kwana biyu yana rarrashi sannan ta haƙura ta saki kamar babu abin da ya faru, sai zaman na su ya dan yi daɗi babu laifi, duk da damar kowa harkar gaban shi ya ke yi.
Kasancewar Jannah suna lokacin hutu na first term inda za ta shiga e.s.s 3. Sai ya kasance gidan da ga ita sai Rose. Kullum tana cikin É—aki, daga kallo sai bacci da chatting, sai in ta gaji ta fito falo ko ta je gurin Rose, don ko mom ta dawo ba ta kanta take bi ba, dad ne wani lokacin yake dan samun kasancewar da ita. A haka sai suke rayuwarsu yau fari gobe tsumma.
Ranar kuma aka yi rashin sa'a bayan kwana biyar ciwon ta ya ƙara tashi. A lokacin duk ba sa nan, sai mai aikin su Kelen da take kicinn tana girki, kasancewar ranar ba duty ɗin Rose ba ne. Kelen yarinya ce domin da kaɗan ta girmi Jannah.
Tana bacci misalin shidda da yamma ta rinka jin sanyin na taso mata a hankali, tun tana controlling har ta ji this was more than she could take.
Wayarta ta ɗauka ta dialling number dad domin ta san shi ne kawai zai ba ta attention her more than mom. She might have been unlucky to call her phone and find it switched off; she could’ve been in a meeting.
Out of that temptation ta kira wayar dad, sai dai to her surprise, he wouldn't be coming due to a specific reason that he mentioned.
Jifa da wayar ta yi, tare da rufe fuskata da hannayenta, tana jin yadda sanyin ke ƙara tasowa.
Sai da aka kira mangariba ya shigo, cikin sauri ya nufi É—akinta, duk da cewar ya kira doctor ya duba ta, amma sam hankalinsa na kanta.
Tana ganin shi ta samu kuka mai karfi. Hanunsa ta kama sosai. "Please do something about this coldness; if not, it will kill me. Look, my body is shaking. Don Allah, dad, i'm tired.”
Sosai ya ji tausayin ta lokaci guda kuma ya zargi kansa, domin shi ne sanadin komai. Don haka ya zama dole ya tilasta wa mata, komawa gida, saboda ko ita was like isolating kan ta ta yi, she wasn't enjoying the environment at all. Given her body language, she was pretending.
Da taimakonsa sanyin ya fara raguwa bayan ya haɗa mata tea mai zafi ta sha har yana kona mata Baki, sannan ta yi wanka da ruwan zafi sosai, ya kunna mata room heater, sai ta samu sauki duk da cewar har zuwa lokacin haƙoran ta na kaɗuwa.
Ganin ta samu bacci ya kashe mata wuya ya fito falo yana zaune har aka kira sallah, daidai lokacin da ta shigo tana rike da jakarta. Kasancewar ba ta san ciwon ya tashi ba, sai ta wuce É—akin ta don gabatar da farali, sosai ta dawo da yunwa. Dad ya rufa mata baya.
A É—aki bayan sun idar da sallah suka sakko kasa don cin lunch, sannan ya ke sanar da ita. Abincin ta bari na nufi dakinta, sai dai har zuwa lokacin bacci take yi, duk da alamu ya nuna ba ta enjoying É—in sa, duba ga yadda ta tsakure kamar mage.
Kofa ta kama tare da juyowa ta da dawo wa falo ta zauna hannu biyu ta zuba tagumi.
"Mu koma gida Halee, don Allah. Our daughter needs that."
Kamar mai tunanin she couldn't say a word. She adjusted and hesitated for a moment. "In har muka koma gida ba zan taɓa manta wa ba duk da cewar na yi maka alƙawarin hakan, sai dai ya zama tabo mara guguwa wanda ya zama silar rashin nagartuwar raguwarmu." Ta karashe maganar cikin sautin kuka tare da juya bayanta.
A hankali ya taka har gabanta ya tsaya lokaci guda idanunsa suka canza. Gwiwowinsa a ƙasa ya kama hannunta a sauri ta janye, ba tare da ya damu ba ya fara magana. "Don Allah ki manta komai na roƙe ki a karo na ba adadi, ki taimake ni ba don halina ba. Kin san yadda abubuwa suka kasance, amma na yi miki alƙawarin hakan ba zai taɓa garuwa ba in sha Allahu kuma zan tsaya tsayin daka, domin na ga na kare ki da ƙarfina.”
Sosai take kuka ba tare da ta saurare shi ba, wanda dalilin kukan yake ƙoƙarin ɗauke numfashinta, ganin hakan ya sanya shi miƙe wa da sauri ya fice daga gidan domin ya san a wannan lokacin babu wanda zai iya rarrashinta. Shi kansa a zaman auren su ya san yana fama da wasu personlity ɗinta wanda suke unlike to his tunaninsa da hankalinsa. Kai tsaye harabar gidan ya fice yare da buɗe murfin motarsa ya shige tare da bata wuta ya fice daga harabar gidan zuciyarsa na tafasa tamkar garwashin wuta.
A hankali ya gangara motarsa zuwa gefen titi tare da kashe motar ya buga kansa da sitiyarin mota a hankali yace. "Prideful woman! Yes absolutely she is." Ya furta yana share fuskarsa da zufar da ta tsatsafo masa.
"Why, Halima, mai ya zuciyarki take kamar ta kafuran farko, Allah mun masa laifi ya yafe mana, amma sam ba kya yafiya."
Idanunsa suka kaɗa jajur har wani turiri kansa yake yi. Kifa kansa ya yi yana jin ina ma ana mai da hannun agogo baya, da ya gyara lamuran da suka faru a baya waɗanda suka zama mara guguwa suka canza alaƙar dake tsakaninsa da iyalinsa, amma sai sai kash! Bakin alƙalami ya bushe kaddara ta riga fata.
Tsawon lokaci ta ɗauka tana durƙushe a gurin zuciyarta tana tafasa ji take tamkar ta mutu ta bar duniya duk da cewar Allah ya wadata da komai na jin daɗin duniya, domin tana cikin matan da suka amsa sunansu kuma suke fantamawa da kuɗaɗensu. Kasacewa mace ce jaruma mai kamar maza a tsaye take. Shahararriyar yar kasuwa wacce ta aje aikin gwannnati domin zagaya ƙasashe don kasuwancinta, don zata iya shiga cikin jerin matan da za'a iya irga kuɗinsu a matan Nigeria. Sai dai duk da irin arzikin da Allah ya yi mata amma akwai tabon da ya raunana zuciyarta wanda take jin tamkar gara ta yi bankwana da rayuwar a take ciki, amma sai dai mutum bai da ikon canza kaddarar rayuwarsa.
COMMENT,READ FOLLOW AND SHARE.
Chapter 5 · 0% Book details