Sashe 57
Kura Da Fatar Akuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'a ki dai bari kiyi wanka wannan wari sai ka ce kin yi kashin kwance." Cewar Hajiya Baaba.
Zubewa a ƙasa ta yi tare da sakin wani irin zananen kuka tana faɗin,"Sun mutu ba ni da kowa kowa ya guje ni Hajiya Baaba."
Zare idanunsa suka yi cikin jimamin jin mutuwar su da suka zamo kamar 'yan'uwa a baya.
"Oh rai baƙon duniya Allah ya jiƙansu da rahma, hatsarin mota suka yi?." Cewar Hajiya Baaba cikin hawaye, wanda ta kasa ba ta amsa sai girgiza kanta da ta yi tana share hawaye.
Mom kuwa kuka ta fashe da shi tare da janta cikin ɗakinta, domin ta kasa cewa komai irin ƙauna da kular da suka yi mata yake dawo mata ƙwaƙwalwarta, wanda ba za ta taɓa manta hakan ba.
"Ki shiga ki yi wanka ga kaya ki shirya, ba ri na sanya a haÉ—a miki abinci."
A falo sun yi jugum-jugum dad kuwa tsananin mamakin yadda ta koma yake yi, tunawa da lokacin da suna Jami'a ita ce take ke amshe gasar wanka da É—aukar gayu, amma dubi yadda duniya ta yi mata É—aurin goro ta wuntsilar da ita cikin duniyar da ta yanke zumunta da su.
"Please mom, I can believe that, you brought that mad woman into our house. Haba you should have think, saboda ba zan iya cin abinci ba idan ina ganinta." Ta ƙarashe maganar tana yamutsa fuska.
"Jannah, ki iya bakinki ba zan lamunta rashin kunya a gareta ba, wanda in kika ƙi ji zan mummunar saɓa miki."
Wani irin kallo ta yi mata sai kuma ta kalli dad da ya kasa mata magana tun da ta fara maganar.
"Ki taimaka mata can kamar yadda kika saɓa, amma ba zan lamunta wata ta shigo mana cikin rayuwarmu ba. Don Allah dad ka ce ta bar mana gidammmu."
Shiru ya yi ba tare da ya ce komai ba. Mom ta juya za ta shiga kicin don ba da umurnin a shirya mata babinci, sai ganinta ta yi tsaye da brush a hannunta.
Turus ta tsaya tana kallonta cikin jin kunya wanda ta tabbatar wa kanta da ta ji duk abin da Jannah take cewa.
"Na kasa buÉ—e shower ne kuma na duba ban ga makilin ba." Ta faÉ—a cikin sanyin murya yayin da idanunta suka kawo ruwa tana jin babu daÉ—i akan abin da ta ce.
"Ok, mu je na nuna miki." Ta bi bayan ta ba tare da ta ƙara cewa komai ba.
Bayan ta gama wankan ta fito falo cikin rashin sakin jiki ganin kallon da Jannah da Jannah take mata wanda daga ƙarshe tsaki ta saki ta shige cikin ɗakinta.
Zama ta yi a takure tana cin abincin wanda ganin hakan ya sanya mom ta sa aka kai mata kayan abincin É—aki daban wanda ta ware mata akan ta zauna acan.
Abinci sosai ta ci sannan ta yi sallah ko da ta buƙaci ta sanar da mom labarinta, amma sai ta kalle ta tare da riƙe hannunta ta ce,"Kar ki damu ki kwanta ki huta da safe za mu yi maganar."
Jannah a ɗakinta tana zaune da laptop ɗinta tana buga game gefenta Ummu riƙe da wayarta assignment da aka basu take yi wanda ita ma ba ta daɗe da gama wa ba.
Bayan ta gama ta gama ta ije a drower sannan ta koma inda take zaune tare da buÉ—e data.
"Subuhanallahi! Yanzu maganar strike ɗin nan ya tabbata!" Ta ce cikin jimami tana nuna wa Jannah abin da aka rubuta a wayarta cikin ɓacin rai.
"Kai! WaÉ—annan mutanen fa ba su damu da future na mu ba, domin they are after money. Yanzu in suna yin strike how many years they want us to obtain degree, they should consider us as their youngers."
"Kin san Allah ba haushin da na ji muna gab da fara exam fa, ya kamata su bari mu gama exam bayan mun sha karatu."
"I'm hoping that they should call off the strike if not, zan gaya wa dad kawai na koma outside Country na ci gaba da karatuna."
Tsaki Ummu ta yi ta kashe datar ta ije wayar domin ganin strike ɗin ya ɓata mata mood ɗinta gabaki ɗaya.
Wayar Jannah ya yi ƙara wanda ta ɗauka da sauri ta kanga a kunninta tana sakin wani irin murmushi bayan ta kashe mata ido.
"Umh, bari kika na tashi kar ku ƙone ya shafe ni." Ta ce tana kai mata dukan wasa a bayanta.
Ba ta ce mata komai ba sai murmushi da ta yi.
"Hello, my angel kina lafiya?" Ya furta da salon muryarsa na jan hankali lokacin da ya ƙaraso kan gadonsa ya faɗa yana shafa kansa.
"Am good bab and you?" Ta ce murya a hankali.
"Ina lafiya lau in dai babbar mace tana lafiya."
Murmushi ya yi har sai da sautin murmushin ya bayyana."Ina lafiya sosai, musamman yanzu da na ji muryarka sai na ji wani irin annashuwa bab."
Dariya sosai ya yi."Ina sonki Jannah, amma yau na yi mafarkin da bai yi mini daɗi ba, domin wani na gani ya riƙe hannunki zai ƙwace ki daga gare..."
"Bab, me ka yi mishi, ina fata ka sare kanshi da takobi?" Ta ce da muryarta da ya bayyana razana da firgici.
"A'a, ban samu na yi hakan ba a mafarki, amma na É—auki ninyar haka a zahirce ga duk wanda ya É—auki É—amarar yin hakan."
"Hakan ma ba zai faru ba bab." Ta ce mishi cikin taushin murya.
"Ki ba ni dama na bayyana kaina a gurin magabatanki Jannah, ina sonki wanda in ban aureki ba zan iya rasa rayuwata. Kin ga tafiya waje zan yi in ya so ayi maganar auren, da na dawo sai aure, kuma auren za a ɗaura muje can muyi karatunmu is ok Jannah, duk abin da iyayenki suka ce daidai ne matuƙar ba za su raba ni da ke ba."
"I will bab, in dai hakan zai faranta maka ko da ace gobe za a É—aura mana aure."
Wani irin ihu ya saka tare da rungume wayarsa." Da gaske kike Aljannata, da gaske kin sauko da burinki mu yi aure da da wuri ba sai kin kai matakin da kika da kike so ba."
Dariyar jin ce mata da ya yi aljannarsa domin wani lokacin haka yake ce mata wanda yake sanya ta nishiÉ—ani.
"Eh, na amince in har hakan zai saka nishaÉ—i." Ta furta a bayyane a ranta kuwa cewa ta yi,
"Ba ka san tashin hankalin da nake ciki ba wanda ya sa na sauke duk wani burina, domin wancan kinibabbiyar tsohuwar na neman kashe ni da raina.
"Yaushe za ki ba ni dama na yi intruducing ki gurin iyayena? ba su da matsala kuma duk sun sanki na nuna musu hotonki."
"Ni ma zan so haka, amma kafin nan ka shirya haÉ—uwa da dad É—ina sun dawo Nigeria."
"Wow, masha Allah. Na yi miki murna sosai I would like to come to see my dad and mom."
Murmushi ta yi suka ci gaba da waya, wanda sai da aka kira sallah sannan suka yi sallama, shi ma ba don sun so ba sai dai don su yi sallah.
A ranar mom ba ta samu damar ganawa da Mujee ba, domin tun da ta fita da safe ba ta dawoba sai cikin dare wanda tana dawowa ta shige ɗakinta, ta kulle ƙofa ta fara aiki a laptop ɗinta daga nan bacci ya kwasheta.
Da safe misalin goma da rabi Ummu ce da Jannah a dining suna karyawa, sai Hajiya Baaba da ke kallo Ammy da Nahlin suna É—aki tana haÉ—a kayansu, domin gobe da safe za su tafi.
Mujee ta fito daga É—akin da ya zama mallakinta, ta yi wanka cikin doguwar rigar da mom ta ba da umurnin aka siyo mata da hijabai har da gyaluluwa, domin kusan akwati guda aka yi mata.
Babu laifi ta yi kyau don har yanzu tabonnin fuskarta ba su gama washewa ba, amma ta ɗan ciko ba kamar lokacin da ta zo ba sai ƙamshi take bugawa.
Ture abincin da take ci ta yi tare da ɓata fuska.
"Kai wannan bagidajiyar mata ta sa na rasa appetite na, saboda am not more interesting. Bayan talauci ma har da mai da ta shafa suka ɓata mata fuska, ni wallahi in na ganta I fell like vomiting." Ta ce tana hararta.
"Please Jannah, stop is not good and is disrespectable. She is your mom's friend and old enough to be you mom."
"Tir! Never over my dead body, wannan kucakar ta zama mahaifiyata."
Mom da ta fito daga ɗakinta ta ji duk abin da take cewa, wanda tsabar baƙinciki ya sanya ta tsaya ta kasa magana domin ta rasa mai za ta ce mata, saboda lamarinta yana ba ta tsoro.
Ƙarasowa ta yi da nufin ta tsawatar ma ta daidai lokacin da Mujee, ta ƙarasa kan dining ɗin za ta zauna.
"Ke dalla can ki je ƙasa ki ci abinci, ko ba ki ga masu gidan suna karyawa ba ne." Ta daka mata tsawa tana faɗin haka wanda har sai da ta firgita Ummu ta miƙe a razane tana kallonta.
Da sauri Mujee ta matsa gefe hawaye na bin fuskarta ba tare da ta ce komai ba.
"Ke fa ba ki da kunya uban kowa sai kin tozarta har da ƙawar uwarki ba za ki raga mata ba." Cewar Hajiya Baaba.
Tsaki ta yi ta tura bakinta ta miƙe za ta bar gurin wanda daidai lokacin da mom ta ƙaraso gurin ba ta yi wata-wata ba ta ɗauke ta da mari.
Wani irin ihu ta sa har sai da gidan ya amsa ta yi watsi da lafiyayyen abincin da aka shirya akan dining É—in.
"Wayyo Allah! Na shiga uku! Wataƙila sai kin kurmantar da ni da wannan ƙarar naki kamar gyare." Cewar Hajiya Baaba tare da toshe kunninta.
"Kika mare ni akan wannan matar?"Ta tambayeta tana kallonta ido cikin ido
"Na mare ki nan gaba duka zan yi miki matuƙar kika ƙara mata rashin kunya."
"Daadd! Ka ga mom ta buge ni akan wannnan matar da na tsane ta haka kawai nake jin kamar na kashe ta, kuma ba zan ɓoye ba dole sai ta bar gidan nan."
Zubewa a ƙasa ta yi tare da sakin wani irin zananen kuka tana faɗin,"Sun mutu ba ni da kowa kowa ya guje ni Hajiya Baaba."
Zare idanunsa suka yi cikin jimamin jin mutuwar su da suka zamo kamar 'yan'uwa a baya.
"Oh rai baƙon duniya Allah ya jiƙansu da rahma, hatsarin mota suka yi?." Cewar Hajiya Baaba cikin hawaye, wanda ta kasa ba ta amsa sai girgiza kanta da ta yi tana share hawaye.
Mom kuwa kuka ta fashe da shi tare da janta cikin ɗakinta, domin ta kasa cewa komai irin ƙauna da kular da suka yi mata yake dawo mata ƙwaƙwalwarta, wanda ba za ta taɓa manta hakan ba.
"Ki shiga ki yi wanka ga kaya ki shirya, ba ri na sanya a haÉ—a miki abinci."
A falo sun yi jugum-jugum dad kuwa tsananin mamakin yadda ta koma yake yi, tunawa da lokacin da suna Jami'a ita ce take ke amshe gasar wanka da É—aukar gayu, amma dubi yadda duniya ta yi mata É—aurin goro ta wuntsilar da ita cikin duniyar da ta yanke zumunta da su.
"Please mom, I can believe that, you brought that mad woman into our house. Haba you should have think, saboda ba zan iya cin abinci ba idan ina ganinta." Ta ƙarashe maganar tana yamutsa fuska.
"Jannah, ki iya bakinki ba zan lamunta rashin kunya a gareta ba, wanda in kika ƙi ji zan mummunar saɓa miki."
Wani irin kallo ta yi mata sai kuma ta kalli dad da ya kasa mata magana tun da ta fara maganar.
"Ki taimaka mata can kamar yadda kika saɓa, amma ba zan lamunta wata ta shigo mana cikin rayuwarmu ba. Don Allah dad ka ce ta bar mana gidammmu."
Shiru ya yi ba tare da ya ce komai ba. Mom ta juya za ta shiga kicin don ba da umurnin a shirya mata babinci, sai ganinta ta yi tsaye da brush a hannunta.
Turus ta tsaya tana kallonta cikin jin kunya wanda ta tabbatar wa kanta da ta ji duk abin da Jannah take cewa.
"Na kasa buÉ—e shower ne kuma na duba ban ga makilin ba." Ta faÉ—a cikin sanyin murya yayin da idanunta suka kawo ruwa tana jin babu daÉ—i akan abin da ta ce.
"Ok, mu je na nuna miki." Ta bi bayan ta ba tare da ta ƙara cewa komai ba.
Bayan ta gama wankan ta fito falo cikin rashin sakin jiki ganin kallon da Jannah da Jannah take mata wanda daga ƙarshe tsaki ta saki ta shige cikin ɗakinta.
Zama ta yi a takure tana cin abincin wanda ganin hakan ya sanya mom ta sa aka kai mata kayan abincin É—aki daban wanda ta ware mata akan ta zauna acan.
Abinci sosai ta ci sannan ta yi sallah ko da ta buƙaci ta sanar da mom labarinta, amma sai ta kalle ta tare da riƙe hannunta ta ce,"Kar ki damu ki kwanta ki huta da safe za mu yi maganar."
Jannah a ɗakinta tana zaune da laptop ɗinta tana buga game gefenta Ummu riƙe da wayarta assignment da aka basu take yi wanda ita ma ba ta daɗe da gama wa ba.
Bayan ta gama ta gama ta ije a drower sannan ta koma inda take zaune tare da buÉ—e data.
"Subuhanallahi! Yanzu maganar strike ɗin nan ya tabbata!" Ta ce cikin jimami tana nuna wa Jannah abin da aka rubuta a wayarta cikin ɓacin rai.
"Kai! WaÉ—annan mutanen fa ba su damu da future na mu ba, domin they are after money. Yanzu in suna yin strike how many years they want us to obtain degree, they should consider us as their youngers."
"Kin san Allah ba haushin da na ji muna gab da fara exam fa, ya kamata su bari mu gama exam bayan mun sha karatu."
"I'm hoping that they should call off the strike if not, zan gaya wa dad kawai na koma outside Country na ci gaba da karatuna."
Tsaki Ummu ta yi ta kashe datar ta ije wayar domin ganin strike ɗin ya ɓata mata mood ɗinta gabaki ɗaya.
Wayar Jannah ya yi ƙara wanda ta ɗauka da sauri ta kanga a kunninta tana sakin wani irin murmushi bayan ta kashe mata ido.
"Umh, bari kika na tashi kar ku ƙone ya shafe ni." Ta ce tana kai mata dukan wasa a bayanta.
Ba ta ce mata komai ba sai murmushi da ta yi.
"Hello, my angel kina lafiya?" Ya furta da salon muryarsa na jan hankali lokacin da ya ƙaraso kan gadonsa ya faɗa yana shafa kansa.
"Am good bab and you?" Ta ce murya a hankali.
"Ina lafiya lau in dai babbar mace tana lafiya."
Murmushi ya yi har sai da sautin murmushin ya bayyana."Ina lafiya sosai, musamman yanzu da na ji muryarka sai na ji wani irin annashuwa bab."
Dariya sosai ya yi."Ina sonki Jannah, amma yau na yi mafarkin da bai yi mini daɗi ba, domin wani na gani ya riƙe hannunki zai ƙwace ki daga gare..."
"Bab, me ka yi mishi, ina fata ka sare kanshi da takobi?" Ta ce da muryarta da ya bayyana razana da firgici.
"A'a, ban samu na yi hakan ba a mafarki, amma na É—auki ninyar haka a zahirce ga duk wanda ya É—auki É—amarar yin hakan."
"Hakan ma ba zai faru ba bab." Ta ce mishi cikin taushin murya.
"Ki ba ni dama na bayyana kaina a gurin magabatanki Jannah, ina sonki wanda in ban aureki ba zan iya rasa rayuwata. Kin ga tafiya waje zan yi in ya so ayi maganar auren, da na dawo sai aure, kuma auren za a ɗaura muje can muyi karatunmu is ok Jannah, duk abin da iyayenki suka ce daidai ne matuƙar ba za su raba ni da ke ba."
"I will bab, in dai hakan zai faranta maka ko da ace gobe za a É—aura mana aure."
Wani irin ihu ya saka tare da rungume wayarsa." Da gaske kike Aljannata, da gaske kin sauko da burinki mu yi aure da da wuri ba sai kin kai matakin da kika da kike so ba."
Dariyar jin ce mata da ya yi aljannarsa domin wani lokacin haka yake ce mata wanda yake sanya ta nishiÉ—ani.
"Eh, na amince in har hakan zai saka nishaÉ—i." Ta furta a bayyane a ranta kuwa cewa ta yi,
"Ba ka san tashin hankalin da nake ciki ba wanda ya sa na sauke duk wani burina, domin wancan kinibabbiyar tsohuwar na neman kashe ni da raina.
"Yaushe za ki ba ni dama na yi intruducing ki gurin iyayena? ba su da matsala kuma duk sun sanki na nuna musu hotonki."
"Ni ma zan so haka, amma kafin nan ka shirya haÉ—uwa da dad É—ina sun dawo Nigeria."
"Wow, masha Allah. Na yi miki murna sosai I would like to come to see my dad and mom."
Murmushi ta yi suka ci gaba da waya, wanda sai da aka kira sallah sannan suka yi sallama, shi ma ba don sun so ba sai dai don su yi sallah.
A ranar mom ba ta samu damar ganawa da Mujee ba, domin tun da ta fita da safe ba ta dawoba sai cikin dare wanda tana dawowa ta shige ɗakinta, ta kulle ƙofa ta fara aiki a laptop ɗinta daga nan bacci ya kwasheta.
Da safe misalin goma da rabi Ummu ce da Jannah a dining suna karyawa, sai Hajiya Baaba da ke kallo Ammy da Nahlin suna É—aki tana haÉ—a kayansu, domin gobe da safe za su tafi.
Mujee ta fito daga É—akin da ya zama mallakinta, ta yi wanka cikin doguwar rigar da mom ta ba da umurnin aka siyo mata da hijabai har da gyaluluwa, domin kusan akwati guda aka yi mata.
Babu laifi ta yi kyau don har yanzu tabonnin fuskarta ba su gama washewa ba, amma ta ɗan ciko ba kamar lokacin da ta zo ba sai ƙamshi take bugawa.
Ture abincin da take ci ta yi tare da ɓata fuska.
"Kai wannan bagidajiyar mata ta sa na rasa appetite na, saboda am not more interesting. Bayan talauci ma har da mai da ta shafa suka ɓata mata fuska, ni wallahi in na ganta I fell like vomiting." Ta ce tana hararta.
"Please Jannah, stop is not good and is disrespectable. She is your mom's friend and old enough to be you mom."
"Tir! Never over my dead body, wannan kucakar ta zama mahaifiyata."
Mom da ta fito daga ɗakinta ta ji duk abin da take cewa, wanda tsabar baƙinciki ya sanya ta tsaya ta kasa magana domin ta rasa mai za ta ce mata, saboda lamarinta yana ba ta tsoro.
Ƙarasowa ta yi da nufin ta tsawatar ma ta daidai lokacin da Mujee, ta ƙarasa kan dining ɗin za ta zauna.
"Ke dalla can ki je ƙasa ki ci abinci, ko ba ki ga masu gidan suna karyawa ba ne." Ta daka mata tsawa tana faɗin haka wanda har sai da ta firgita Ummu ta miƙe a razane tana kallonta.
Da sauri Mujee ta matsa gefe hawaye na bin fuskarta ba tare da ta ce komai ba.
"Ke fa ba ki da kunya uban kowa sai kin tozarta har da ƙawar uwarki ba za ki raga mata ba." Cewar Hajiya Baaba.
Tsaki ta yi ta tura bakinta ta miƙe za ta bar gurin wanda daidai lokacin da mom ta ƙaraso gurin ba ta yi wata-wata ba ta ɗauke ta da mari.
Wani irin ihu ta sa har sai da gidan ya amsa ta yi watsi da lafiyayyen abincin da aka shirya akan dining É—in.
"Wayyo Allah! Na shiga uku! Wataƙila sai kin kurmantar da ni da wannan ƙarar naki kamar gyare." Cewar Hajiya Baaba tare da toshe kunninta.
"Kika mare ni akan wannan matar?"Ta tambayeta tana kallonta ido cikin ido
"Na mare ki nan gaba duka zan yi miki matuƙar kika ƙara mata rashin kunya."
"Daadd! Ka ga mom ta buge ni akan wannnan matar da na tsane ta haka kawai nake jin kamar na kashe ta, kuma ba zan ɓoye ba dole sai ta bar gidan nan."