Sashe 50
Kura Da Fatar Akuya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHEEM
"Ina ga we have to sleep on it. Kin san ta don haka mu yi gaggawar komaw.."
Bai ƙarashe maganar ba kiran Jannah ya shigo wayarsa, sai suka kalli juna a tare. Zuciyar mom cike da jin daɗin ba ita ta kira ba, domin ta san sai ta gaya mata maganar da za ta kasa bacci da kuka.
"Hajiya Baaba ta kira mana ruwa fa." Ya faÉ—i daidai lokacin da mom ta yi hanyar É—akinta da sauri tana faÉ—in,
"Ba ri na shiga ɗakina sai ku ƙarata can ba zan iya da rigimarta ba."
Cikin sanyin jiki ya sanya wayar a kunninsa bayan ya yi sallama. wanda ko sallamar ba ta amsa ba ta fara faÉ—in,
"Dad, could you imagined wai ni Hajiya Baaba, said that she will gonna give my hand in marriage to Ya Ajmal, as young as I'm, wallahi I really hate him cus he is not civilized at all." Ta ƙarasa maganar tana ƙuta.
Shiru ya yi don ya rasa me ze ce mata sai ya tsinci kansa da faɗin,"Never and impossible! Sam ba zan taɓa miki auren dole ba, kuma ba za ki yi aure yanzu ba sai kin cika burinki."
"Haba! I wander, ai dama na san wasa take yi mini domin ba za ka taɓa yadda ba, amma sai ta ce mini wai you are so greedy you most agreed." Ta katse shi tana faɗin haka.
Maganar ta soke shi har sai da ya rintse idanunsa, yana jin zafi a ransa ba tun yau ba ya san ta tsane shi ba ta son shi, musamman lokacin da lamarin ya faru abubuwa suka rikice."
"Kar ki damu ki kwantar da hankali ki saurari dawowarmu, muna dawowa za mu koma gidammu."
"Ai dama ban damu ba, kawai she is pestering me, shi ya sa na ga I have to give you a call, duk da na san shi doesn't has authority on me. Please dad take care you of youself I love you." Ta kashe wayar tana murmushi.
Kalmar da ta faɗi suka rinƙa masa kuwwa a kunninsa sai ya dafe kansa cikin jin tausayinta.
"Ba ki san wace ce Hajiya Baaba ba, domin ba ki da mafita da ya wuce auren nan."
Jannah ta sauke wayar tare da ajiyar zuciya mai ƙarfi ta kalli Nahlin da Ummu da suka yi zugum ta ce,"Da ma na gaya muku wallahi ba ta isa ba. Haba ita ɗin wa, don kawai ta haifi mom sai ta ce za ta juya kowa."
Miƙewa suka yi suka kalli junansu sannan suka shige ɗaki ba su ce mata komai ba, wanda ganin haka ya sa ta taɓe bakinta ta nufi sashin Hajiya Baba fuskarta a ɗaure babu ko walwala.
A falo tana ƙoƙarin shiga cikin ɗakinta daidai lokacin da ta fito daga bayin falon da abu ƙulle a baƙin leda da ƙatuwar roba a hannunta.
"Yauwa Jannahtu zo nan, dama yanzu zan sanya a yi mini kiranki, saboda tun yau zan fara miki wankan lalli saboda babu lokacin, don zamaninmu biki tun yana kusan wata bakwai ake farawa wa, ga shi ke duka ba za a sanya da nisa ba don ba zai wuce wata uku ba, don haka gara mu fara tun yanzu."
Har ta murɗa ƙofa za ta shige ɗakinta duk da ta ji kiran amma kuma sai ta fasa jin abin da ta ce.
Idanunta ta waro mata cikin ɓacin rai daidai lokacin da ta ƙaraso gabanta tana juya ruwan lallin da hannunta.
"Kin ganshi lalli ne mai kyau daga barno aka kawo mini shi ina ƙunsawa, yanzu dole na yi waya a kawo mini buhu don sai ya ƙare kafin bikin." Ta sa aya tare da ibo ruwan lallin za ta goga mata a fuska, wanda ya sanya ta matsa da sauri tana kallon shi kamar kashi tare da toshe hanci.
"Kin san Allah Hajiya Baaba, kar ki kuskura ki watsa mini wannnan abu mai kama da kashi a jikina, kuma ki bar maganar auren nan you are hurting my feelings, bana so."
"Dukana za ki yi? Ke fa daÉ—ina dake ba a miki abin arziki kina sane da gidan kishiya za ki sai kin sha gyara kar kije ki zama mowa."
"Na ga alama kin taɓu sai an kai ki gidan mahaukata, ƙila kuma aure kike son yi sai ki samo bazawari tsoho, na san su mom ba za su hana ki ba."
"Kiji mini tsiya ni kike faɗin ma haka? Aure ko a lahira na haƙura da shi in dai ba Aminu masoyina za a ba ni. Ki kalli tsabar idona kice mini na taɓu, bari na nuna miki haukar."
Kawai ta ibo ruwan lallin mai yawa ta watsa mata a jiki har da fuska, wanda sanyin ruwan lallin ya shigeta sai ta ƙwala ƙara da ƙarfinta har sai da gidan ya ɗauka, wanda ya sa duka mutanen gidan suka sheƙo.
"Mutane za ki tara mini don ubanki daga miki abin arziki?"Ta tambayeta tare da toshe kunninta domin ƙarar ya shige har ƙwaƙwalwarta.
"Wallahi sai Allah ya saka mini da kika ɓata mini rigar da Huzaifah ya ce tafi kowane kaya yi mini kyau." Ta ce daidai lokacin da mutanen gidan suka ƙaraso a guje.
Lafiya Hajiya Baaba, mai ya faru?" Aby ya tambayeta cikin tsananin razana yana kalon Jannah da ke kuka shaɓe-shaɓe.
Ba ta ba shi amsar tambayarsa ba ta buge mata baki tana faÉ—in,
"Da maganar wani a kanki kike kiran wani gardi? To me ya rage tun da na riga na tambaya masa kawai auren ya rage, ga sadaki a hannuna yanzu ma zan iya bayarwa"
Sai kuma ta kalle su da suka yi jugum-jugum suna kallonta.
"Au kuji mini ja'ira dama kin yi ne da biyu don ki tara mini mutane?" Sai ƙara kallon Aby da yake jin damuwar zuciyarsa ta fi ƙarfin ƙwaƙwalwarsa ta ce,
"Ni da wannan da ba a mata abun kirki don kawai zan fara mata wankan lalli, shi ne take ci mini mutunci har tana kirana da mahaukaciya shi ya sa na nuna mata ƙarshen haukar. Da yake ita shashasha ce, ba ta san inda ke mata ciwo ba, ai ban gyarata a kwai matsala, tunna gidan kishiya za ta amma tana mini rashin mutunci, ai dole na fara gyarata ta zama mowa ko?"
Ta ƙarashe maganar da sigar tambaya tana kallonsa wanda takaici ya hana shi cewa komai sai dai ya ɗaga mata kansa kawai ya fice yayin da sauran suka rufa masa baya.
Jannah ta galla mata harara za ta bi bayansu wanda da sauri ta janyo rigarta ta dawo da gabanta tana faÉ—in," Da wo nan babu inda za ki aini da ke mutu ka raba don ko auren aka yi, mutane na watsewa zan tattara inawa-inawa na dawo gidan.
Hannunta ta fisge ta gallah mata harara ta yi cikin ɗakinta tare da bugo ƙofar kamar za ta ɓalla.
"Allah Sarki kofa, ba ita ta kar zomon ba rataya aka ba ta." Ta juya ta shige É—akinta tana mita.
Cikin sanyin jiki yake tuƙa motar tamkar wanda aka zarewa lakka har y isa gida ya yi hon.
Maigadi ya taso ya buɗe masa yana jiran ya shigo da motar, amma sai ya fahimci ya yi nisan kiwo, domin bai san ya buɗe ba. Tunani ne barkatai a ranshi wanda ba shi da hanyar ɓullo musu.
Rintse idanunsa ya yi yana jin tsananin tsanarta yana ƙara samun matsuguni a jikinsa, don sai yanzu ya gane dalilin tsanarta da ya yi matuƙa, saboda tun da ta zo ya kalle ta kwata-kwata ba ta yi masa ba.
Ganin ya yi nisan kiwo ya sanya maigadi ya bubbuga gilashin motar wanda ya sanya ya yi firgigif kamar mai bacci.
A hankali ya shigo da motar kamar baya son shiga gidan daidai lokacin da Mushiirat ta fito da dogon hijabinta har ƙasa da carbi a hannunta tana ja.
Jim ta ɗan yi tana kallon yanayin fuskarsa kafin ta ƙarasa gurinsa.
Kamar yadda suka saba duk lokacin da ya dawo sai ya miƙo mata hannu sun yi sallama suna sakar ma junansu murmushi sannan ya yi hugging ɗinsa. Sai dai, yau ita ta fara miƙa masa tare da kwanciya a jikinsa.
"Barka habibina, you took more than the time you said." Ta ce cikin shagwaɓa tana shafa gefensa da ya sha gyara sai ɗaukar ido yake.
"Am sorry." Kalmar da ya iya furtawa kenan sai ya matsar da ita daga jikinsa zai shige cikin falon cikin rashin ƙwarin gwuiwa, saboda wani irin tausayi da ta ba shi.
Ta bishi da kallo har ya shige wanda hankalinta ya yi matuƙar tashi sosai take ta fara tambayar kanta lafiya, amma rashin masa ya sanya tabi bayansa lokacin da ya shige ɗakinsa.
"Bab, what's wrong, are you alright?" Ta tambaye shi lokacin da ta rufe ƙofar tana ƙarasowa gurinsa.
"Yes I'm, kamar kaina yake son ya yi ciwo bari na watsa ruwa. May be I will better." Ya ce tare da miƙewa zai shiga bayi ba tare da ya kalle ta.
"Oh no please, yaushe muka fara ɓoye abin da ke damunmu a tsakaninmu? Don Allah ka gaya mini na shiga damuwa." Ta ce tare da riƙe hannunsa.
"Na ce miki kaina yake ciwo." Ya faɗa murya a kausashe yana ƙoƙarin shigewa.
Da sauri ta tari gabansa tana kallon idanunsa."Gaskiya ni ba zan yafe wa kaina ba, matuƙar ban ɗauke maka damu.."
"Ke!" Ya daka mata tsawar da ta firgita ta, wanda ya sa ta saki hannunsa da sauri ta matsa gefe tana zare ido don har hawaye ya fara sauka fuskarta, saboda za ta iya rantse wa yau ne farko da ta ji ya daka mata tsawa.
"Haba na gaya miki babu komai, amma you keep asking let me be." Ya ce tare da ƙarasa shiga cikin bayin.
Sharaf ta zauna a gefen gadon tare da saka kuka, dama tun da take kiran wayarsa bai ɗaga ba ta san akwai abin da ke faruwa. Lokaci guda ta fara tunanin abin da zai iya ɓata masa rai haka ya kauda ɗoki da zaƙuwar da yake ta yi ya dawo sun kasance a tare.
"Ina ga we have to sleep on it. Kin san ta don haka mu yi gaggawar komaw.."
Bai ƙarashe maganar ba kiran Jannah ya shigo wayarsa, sai suka kalli juna a tare. Zuciyar mom cike da jin daɗin ba ita ta kira ba, domin ta san sai ta gaya mata maganar da za ta kasa bacci da kuka.
"Hajiya Baaba ta kira mana ruwa fa." Ya faÉ—i daidai lokacin da mom ta yi hanyar É—akinta da sauri tana faÉ—in,
"Ba ri na shiga ɗakina sai ku ƙarata can ba zan iya da rigimarta ba."
Cikin sanyin jiki ya sanya wayar a kunninsa bayan ya yi sallama. wanda ko sallamar ba ta amsa ba ta fara faÉ—in,
"Dad, could you imagined wai ni Hajiya Baaba, said that she will gonna give my hand in marriage to Ya Ajmal, as young as I'm, wallahi I really hate him cus he is not civilized at all." Ta ƙarasa maganar tana ƙuta.
Shiru ya yi don ya rasa me ze ce mata sai ya tsinci kansa da faɗin,"Never and impossible! Sam ba zan taɓa miki auren dole ba, kuma ba za ki yi aure yanzu ba sai kin cika burinki."
"Haba! I wander, ai dama na san wasa take yi mini domin ba za ka taɓa yadda ba, amma sai ta ce mini wai you are so greedy you most agreed." Ta katse shi tana faɗin haka.
Maganar ta soke shi har sai da ya rintse idanunsa, yana jin zafi a ransa ba tun yau ba ya san ta tsane shi ba ta son shi, musamman lokacin da lamarin ya faru abubuwa suka rikice."
"Kar ki damu ki kwantar da hankali ki saurari dawowarmu, muna dawowa za mu koma gidammu."
"Ai dama ban damu ba, kawai she is pestering me, shi ya sa na ga I have to give you a call, duk da na san shi doesn't has authority on me. Please dad take care you of youself I love you." Ta kashe wayar tana murmushi.
Kalmar da ta faɗi suka rinƙa masa kuwwa a kunninsa sai ya dafe kansa cikin jin tausayinta.
"Ba ki san wace ce Hajiya Baaba ba, domin ba ki da mafita da ya wuce auren nan."
Jannah ta sauke wayar tare da ajiyar zuciya mai ƙarfi ta kalli Nahlin da Ummu da suka yi zugum ta ce,"Da ma na gaya muku wallahi ba ta isa ba. Haba ita ɗin wa, don kawai ta haifi mom sai ta ce za ta juya kowa."
Miƙewa suka yi suka kalli junansu sannan suka shige ɗaki ba su ce mata komai ba, wanda ganin haka ya sa ta taɓe bakinta ta nufi sashin Hajiya Baba fuskarta a ɗaure babu ko walwala.
A falo tana ƙoƙarin shiga cikin ɗakinta daidai lokacin da ta fito daga bayin falon da abu ƙulle a baƙin leda da ƙatuwar roba a hannunta.
"Yauwa Jannahtu zo nan, dama yanzu zan sanya a yi mini kiranki, saboda tun yau zan fara miki wankan lalli saboda babu lokacin, don zamaninmu biki tun yana kusan wata bakwai ake farawa wa, ga shi ke duka ba za a sanya da nisa ba don ba zai wuce wata uku ba, don haka gara mu fara tun yanzu."
Har ta murɗa ƙofa za ta shige ɗakinta duk da ta ji kiran amma kuma sai ta fasa jin abin da ta ce.
Idanunta ta waro mata cikin ɓacin rai daidai lokacin da ta ƙaraso gabanta tana juya ruwan lallin da hannunta.
"Kin ganshi lalli ne mai kyau daga barno aka kawo mini shi ina ƙunsawa, yanzu dole na yi waya a kawo mini buhu don sai ya ƙare kafin bikin." Ta sa aya tare da ibo ruwan lallin za ta goga mata a fuska, wanda ya sanya ta matsa da sauri tana kallon shi kamar kashi tare da toshe hanci.
"Kin san Allah Hajiya Baaba, kar ki kuskura ki watsa mini wannnan abu mai kama da kashi a jikina, kuma ki bar maganar auren nan you are hurting my feelings, bana so."
"Dukana za ki yi? Ke fa daÉ—ina dake ba a miki abin arziki kina sane da gidan kishiya za ki sai kin sha gyara kar kije ki zama mowa."
"Na ga alama kin taɓu sai an kai ki gidan mahaukata, ƙila kuma aure kike son yi sai ki samo bazawari tsoho, na san su mom ba za su hana ki ba."
"Kiji mini tsiya ni kike faɗin ma haka? Aure ko a lahira na haƙura da shi in dai ba Aminu masoyina za a ba ni. Ki kalli tsabar idona kice mini na taɓu, bari na nuna miki haukar."
Kawai ta ibo ruwan lallin mai yawa ta watsa mata a jiki har da fuska, wanda sanyin ruwan lallin ya shigeta sai ta ƙwala ƙara da ƙarfinta har sai da gidan ya ɗauka, wanda ya sa duka mutanen gidan suka sheƙo.
"Mutane za ki tara mini don ubanki daga miki abin arziki?"Ta tambayeta tare da toshe kunninta domin ƙarar ya shige har ƙwaƙwalwarta.
"Wallahi sai Allah ya saka mini da kika ɓata mini rigar da Huzaifah ya ce tafi kowane kaya yi mini kyau." Ta ce daidai lokacin da mutanen gidan suka ƙaraso a guje.
Lafiya Hajiya Baaba, mai ya faru?" Aby ya tambayeta cikin tsananin razana yana kalon Jannah da ke kuka shaɓe-shaɓe.
Ba ta ba shi amsar tambayarsa ba ta buge mata baki tana faÉ—in,
"Da maganar wani a kanki kike kiran wani gardi? To me ya rage tun da na riga na tambaya masa kawai auren ya rage, ga sadaki a hannuna yanzu ma zan iya bayarwa"
Sai kuma ta kalle su da suka yi jugum-jugum suna kallonta.
"Au kuji mini ja'ira dama kin yi ne da biyu don ki tara mini mutane?" Sai ƙara kallon Aby da yake jin damuwar zuciyarsa ta fi ƙarfin ƙwaƙwalwarsa ta ce,
"Ni da wannan da ba a mata abun kirki don kawai zan fara mata wankan lalli, shi ne take ci mini mutunci har tana kirana da mahaukaciya shi ya sa na nuna mata ƙarshen haukar. Da yake ita shashasha ce, ba ta san inda ke mata ciwo ba, ai ban gyarata a kwai matsala, tunna gidan kishiya za ta amma tana mini rashin mutunci, ai dole na fara gyarata ta zama mowa ko?"
Ta ƙarashe maganar da sigar tambaya tana kallonsa wanda takaici ya hana shi cewa komai sai dai ya ɗaga mata kansa kawai ya fice yayin da sauran suka rufa masa baya.
Jannah ta galla mata harara za ta bi bayansu wanda da sauri ta janyo rigarta ta dawo da gabanta tana faÉ—in," Da wo nan babu inda za ki aini da ke mutu ka raba don ko auren aka yi, mutane na watsewa zan tattara inawa-inawa na dawo gidan.
Hannunta ta fisge ta gallah mata harara ta yi cikin ɗakinta tare da bugo ƙofar kamar za ta ɓalla.
"Allah Sarki kofa, ba ita ta kar zomon ba rataya aka ba ta." Ta juya ta shige É—akinta tana mita.
Cikin sanyin jiki yake tuƙa motar tamkar wanda aka zarewa lakka har y isa gida ya yi hon.
Maigadi ya taso ya buɗe masa yana jiran ya shigo da motar, amma sai ya fahimci ya yi nisan kiwo, domin bai san ya buɗe ba. Tunani ne barkatai a ranshi wanda ba shi da hanyar ɓullo musu.
Rintse idanunsa ya yi yana jin tsananin tsanarta yana ƙara samun matsuguni a jikinsa, don sai yanzu ya gane dalilin tsanarta da ya yi matuƙa, saboda tun da ta zo ya kalle ta kwata-kwata ba ta yi masa ba.
Ganin ya yi nisan kiwo ya sanya maigadi ya bubbuga gilashin motar wanda ya sanya ya yi firgigif kamar mai bacci.
A hankali ya shigo da motar kamar baya son shiga gidan daidai lokacin da Mushiirat ta fito da dogon hijabinta har ƙasa da carbi a hannunta tana ja.
Jim ta ɗan yi tana kallon yanayin fuskarsa kafin ta ƙarasa gurinsa.
Kamar yadda suka saba duk lokacin da ya dawo sai ya miƙo mata hannu sun yi sallama suna sakar ma junansu murmushi sannan ya yi hugging ɗinsa. Sai dai, yau ita ta fara miƙa masa tare da kwanciya a jikinsa.
"Barka habibina, you took more than the time you said." Ta ce cikin shagwaɓa tana shafa gefensa da ya sha gyara sai ɗaukar ido yake.
"Am sorry." Kalmar da ya iya furtawa kenan sai ya matsar da ita daga jikinsa zai shige cikin falon cikin rashin ƙwarin gwuiwa, saboda wani irin tausayi da ta ba shi.
Ta bishi da kallo har ya shige wanda hankalinta ya yi matuƙar tashi sosai take ta fara tambayar kanta lafiya, amma rashin masa ya sanya tabi bayansa lokacin da ya shige ɗakinsa.
"Bab, what's wrong, are you alright?" Ta tambaye shi lokacin da ta rufe ƙofar tana ƙarasowa gurinsa.
"Yes I'm, kamar kaina yake son ya yi ciwo bari na watsa ruwa. May be I will better." Ya ce tare da miƙewa zai shiga bayi ba tare da ya kalle ta.
"Oh no please, yaushe muka fara ɓoye abin da ke damunmu a tsakaninmu? Don Allah ka gaya mini na shiga damuwa." Ta ce tare da riƙe hannunsa.
"Na ce miki kaina yake ciwo." Ya faɗa murya a kausashe yana ƙoƙarin shigewa.
Da sauri ta tari gabansa tana kallon idanunsa."Gaskiya ni ba zan yafe wa kaina ba, matuƙar ban ɗauke maka damu.."
"Ke!" Ya daka mata tsawar da ta firgita ta, wanda ya sa ta saki hannunsa da sauri ta matsa gefe tana zare ido don har hawaye ya fara sauka fuskarta, saboda za ta iya rantse wa yau ne farko da ta ji ya daka mata tsawa.
"Haba na gaya miki babu komai, amma you keep asking let me be." Ya ce tare da ƙarasa shiga cikin bayin.
Sharaf ta zauna a gefen gadon tare da saka kuka, dama tun da take kiran wayarsa bai ɗaga ba ta san akwai abin da ke faruwa. Lokaci guda ta fara tunanin abin da zai iya ɓata masa rai haka ya kauda ɗoki da zaƙuwar da yake ta yi ya dawo sun kasance a tare.