← Book details Huriyya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 143

Sashe 61

Huriyya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

karbi ruwan ya sha ya mika mata Empty cup. Dama ace... Ke ce..., da raina ba zai ba ce ba, kuma zuciya ba zata ki yarda ba A ransa yake maganar yana binta da kallo bayan ta isa kofar falon surukarsa Hajiya Kaltume. A dinning ta aje cup din da bottle water ta nufi upstairs gabanta na faduwa domin yanzu ta san abu ne mai wahala Appa ya kirata akan wani abun alheri balle kuma a bangaren Hajiya Kaltume, waya sani ko wani sherin suka kulla mata. Cikin tsoro da fargaba ta tura kofar dakin ta shiga. After Hurriya ta wuce, Fadeel ya sauke ajiyar zuciya ya kalli Khairy dake tsaye kamar an sassaka itace ya ce Ni zan koma Toh a gaishe da gida Ta fara tafiya sai ya tsayar da ita, ya bude Motarsa ya dauko leda ya mika mata. Thank You Ta furta sannan ta wuce ta yi gaba, shi kuma ya shuga motarsa ya zauna, har sai da ta shige ciki sannan ya yi ma motar key ya juya. Har ya isa gidan Hajiya Fatee be daina tunanin yadda za'ayi su yi rayuwa haka da Khairy ba tun a waje balle kuma ace ya aureta, tun ba yau ba ya lura ita ma bata ra'ayinsa kamar yadda baya ra'ayinta. Domin wannan ne zuwa na biyar da yayi a gurinta idan suka gaisa baya sake cewa komai ko da ya gwada ma sai ya ji baya iyawa ita ma kuma bata cewa kuma bata sakewa, haka za su yi ta zama kamar wasu hotuna. Be kashe motar ba ya fita domin ba dadewa yake son yi a gidan ba so kawai yake yayi magana da Hajiyarsa. One step forward a falon Hajiya Fatee yayi arba da bako da ya fito daga dakinta sanye da shadda ruwan kasa, kana ganinsa ka ga bakauye, and instead of ya karasa fitowar sai ya juya da sauri ya koma cikin dakin na Hajiya. Fadeel yayi tsaye a falon yana kallon kofar dakinta with curious face, sai ga Hajiya Fatee ta fito tana ganin Fadeel ne ta saki fuska. Ashe ma Fadeel ne, yaya Malam fito ai danka ne Fadeel dai kallonta kawai yake. Waye wannan? Kawuka ne na kauye, zauna sai ya fito ku gaisawa, yau ya zo nan zai kwana yanzu haka ma zancenka muke sai gashi ka zo, Yaya Malam fito mana ku gaisa da Fadeel Fadeel ya zauna yana kallon kofar dakin da Yaya Malam ya ki fitowa. _____________________ Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku. Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660 Be taba zuwa nan ba sai yau, kakaninmu ne guda da shi, amman su a nijar suke, sai bana Allah ya kawo shi Hajiya Fatee ta fada tana ta yan kama kame. Fadeel ya motsa hannunsa sai kuma ya mike tsaye ba tare da tunanin komai a ransa ba ya ce. Maybe da safe zamu gaisa, ni ma gida zanje yanzu, daman na fito gurin Khairy ne na biyo nan saboda akwai maganar da na so mu yi, amman zamu yi da safe Hajiya Fatee ta kalleshi tana murmushi. Okay Allah ya maka albarka Sai da safe Hajiya Allah tashemu lafiya Ya nufi kofar fita ta bude ya fice, sai da Hajiya ta leka ta ga motarsa ta bar gurin sannan ta tashi a fusace ta shiga dakinta. Haba Malam haba na fada maka kwana gidan nan ba zai yiyu ba, ka ce dole sai an yi haka saboda Aljanin da dare zai zo, kuma na fada maka karka fita daga dakin nan idan kana neman wani abu ka fada min zan dauko maka, saboda gudun irin haka, kullum dana sai ya zo da safe ko dare ya gaishe ni, yanzu ba dan yana da zuciya mai kyau ba ai sai ya wani tunanin ya zo masa Malam yayi yar dariya mai cike da tsoro abun ka da bakauye. Hajiya ban san cewa danki zai zo ba, ni ma kawai na so na fita na dan zagaya ta can baya ne akwai abubuwan da zan karanta saboda kiran rauhanai Kuma ina ta kiranka ka fito mu gaisa baka fito ba, bayan na masa karyar cewa kai dan'uwana ne Akwai dalilin da ya saka, amman karki damu danki ai wata rana zai ganin har sai ya gaji da gani na Kallon rashin fahimta ta yi masa. Kamar ya? Ai bana fatar haka, Malam bayan wannan za su sake neman wani abu ne? Aa ba za su sake neman komai ba, yanzu din ma, ai shegen kwadayi ne da son mata irin na manyan aljannu, kin san yadda farar mace take da daukar ido ko tsohuwa ce balle ke da ba za ace kin yi shekarunki ba, shiyasa kullum ake fada muku ku rika rufe jikinku amman baku ji Ta sauke ajiyar zuciya, ranta bakikirin kamar an mata bushara da mutuwa. Abubuwan sun yi yawa Malam, bana fatan sake aikata komai bayan wannan, tun bayan rabuwata da miji wani abu be sake shiga tsakanina da kowa ba, sai da kaddara nan ta fada min yara kanana suka ci mutunci, duk shi ne silar wannan bakincikin Karki damu Hajiya, daman tuntuna saboda kin dauki lokaci ne da tuni ma an wuce gurin, gashi har cikin ya kara satika, amman har yanzu ba mu makara ba. Amman Hajiya na yi miki wata tambaya mana, miye sa ba zaki yi aure ba, wato a lokacin da ina zurfafa bincike a kanki sai na hango maza da yawa da suke kaunarki, kina da wannan kwarjin na hallita A kaikaice ta kalleshi kallon da ya fi kama da harara. Miya kawo wannan maganar Malam? Ina ruwanka da rayuwata ko aurena? Samun gurin har ya kai haka? Karki manta dai da Malam kike magana, kuma ina son na fada miki babu mai iya miki irin aikin da zan miki duk garin nan, ki ga aiki kamar yankan wuka, ai kin yi ta sake sake shi ya dauke ki lokaci, da kika ga babu mafita ne kika kirana kika ce kin amince, ina bibiyar duk wanda nake yi ma aiki, ina ganin duk halin da suke ciki Ta rufe zancen da rufe kwalbar turare mai tsananin karfi, irin mai hawan kanka ya tashi mai aljannu. Hajiya Fatee ta mike tsaye daga kan gadonta da take zaune ta kalli Malam dake zaune a kasa ta ce. Malam ina ganin kamata yayi ka koma dakin baki dake waje, idan dare ya kara yi zan zo da kaina, daman saboda gudun dana ko masu aikin gidan su ganka ne, kuma yanzu na samu mafitar hakan tun da har na yi ma dana karyar kai dan'uwana ne Hajiya ai duk yadda kika ce haka za'ayi, rufin asirin na ki ne ba nawa ba Ya mike tsaye. Sai ki min jagora zuwa dakin bakin, ni ma hankalina zai fi kwanciya da haka Komawa ta yi ta zauna yayinda yake tsaye yana jiran ta wuce gaba ta nuna masa dakin, sai ta dafe kanta tana jin kamar ta fashe da kuka, abun duniya duk ua isheta, idan tace zata bar cikin,tonuwar asirinta ne gashi har ya fara tasowa dan lokacin data dauka bata mayar masa da amsar ta aminci ko akasin haka ba. HURRIYA POV. Kallo daya ta yi ma Appa ta san ba lafiya ba, domin fuskarsa a hade take kamar be taba dariya ba. Appa barka da dare Appa ya duba duban dake kara bayyana bacin ransa. Karata kika kao Hurriya? Ta nuna kamta. Ni... Hajiya Kaltume ta yi karaf ta ce. Aa ba ke ba shi.. Tun da kin raina mutane Hurriya ta kalli Hajiya Kaltume da sauri domin kalamanta suna kara rudata ne kawai. Tafiya kike gida gida kina fadar na ki na saka ki makaranta? Ta fiddo ido kamar za su fasa gilashin dake fuskarta su fito. Ni Appa Wallahi ban yi haka ba, ya za'ayi na yi haka? Toh waya je ya fada? Da Magariba nan Alhaji Garba ya same ni da zancen yana neman izini yana son ya nema miki makaranta, na gaza ne Hurriya? Tana jin Alhaji Garba ta san makocinsu ne kuma mahaifin kawarta Husna. A take idonta ya cika da kwalla. Wallahi Appa, ban ce ka gaza ba, ban fada mata cewar ka ce ba zaka saka ni makaranta ba, ni ban yi magana da Babanta ko mamanta ba, Appa Wallahi ban kai kararka gurin kowa ba Appa ya zaburo mata kamar zai kai mata duka. Idan baki fada ta ina suka ji cewar baki zuwa makaranta? Har zai same ni da zancen wai yana son ya sakaki makaranta baya bukatar sisina umarni kawai yake so, idan ba kin je ki fadi
Chapter 61 · 0% Book details