← Book details Huriyya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 143

Sashe 58

Huriyya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ga Allah ba kin ga ko waye zai bayyana kansa, ki daina damuwa tashi muje mu ci abincin dare Hurriya ta sauko ganin Namra ta mike tsaye suka fita tare, suka sauka kasa a plate daya Namra ta saka musu tuwon semu da miyar yauki ta saka manshanu sosai, ta dauko ruwa ta zauna a kasa. Sauko mu ci Hurriya ta tashi ta shiga Kitchen ta wanke hannunta ta fito ta zauna kusa da Namra, a madadin ta ci abincin kai tsaye sai ta kwantar da kanta jikin Namra. Yaya Namra na gode, ke da Yayana kawai kuke so na a gidan nan Namra ta yi murmushi. Ba komai yar kanwata, ni wannan abun da ake cewa yan ubanci bana miki kallon haka, ina kallonki ne kamar uwa daya uba daya muke, tashi ki ci abinci Ta tashi ta gyara zamanta sai dai kamin ta kai hannunta cikin abinci Khairy ta shigo sanye da karamin mayafinta wayarta a hannunta, is like kamar an mata dole haka ta tsaya bakin kofar falon babu ko sallama. Hurriya taso muje Hurriya ta kalleta. Ina? Ki taso idan zaki taso Malama Namra ta daga kai ta kalli Khairy da duba na wulakancin. Ba zata tashi ba abinci zata ci Okay sannu uwarta, bari naje na fadawa Yaya uwarta ta hanata zuwa, ita ma kuma ta ce ba zata je ba Hurriya na jin kiran na Yayanta ta tashi tsaye da sauri zata nufi kofar. Dauko mayafinki Hajiya Ta juya ta dauko mayafin kamar yadda Khairy ta bukata, sannan ta bi bayanta suka fice, at first ta yi zaton bangaren Hajiya Kaltume za su nufa sai kuma ta ga ta nufi gate. Ba yaya kika ce yana kirana ba? Yana waje Huriyya ta bi bayanta suka fita gate, close to gate din wata mota ce fake da ba ta gidan ba. Gurin motar suka nufa ta bude ma Hurriya baya. Shiga Amman wannan ba motar Yayana ba ce... Zaki shiga ko sai ya fito ya mareki? Ba shi ya ce mu jira shi a mota ba Hurriya ta shiga da sauri, Khairy ta rufe bayan sannan ta bude front seat ta shiga ta zauna tana taba wayarta. After like five minutes aka bude motar ta Driver seat aka shigo, tana leken fuskarsa yana juyo ya kalleta wa zata gani ba Adam ba. Thank you Khary This should be the last time sa zaka cilasta min fitowa da yarinyar nan Ta fada a kufule. Hurriya ta kalleta fuska kamar zata fashe da kuka, murya kamar a shagwabe ta ce. Amman yaya Khairy kin san me Appa yace ko kuma kin san Yayana zai yi fada idan ya sani Adam yayi saurin tarar numfashinta. Ba dadewa zamu yi ba Hurriya, kawai ina son na ganki ne kuma na baki hakuri abun da ya faru, and na aiko da box an baki? Khairy ta watsa masa wani kallo. Okay ni zan hana mata box din kenan? Waya sani, tun da har kika iya bata ni a gurinta ai zaki iya hana ta ganin box din Ni ban bata ka ba And why take min kallon mutumen banza? Ni ba iskanci ne ya kawo ni gurinta ba, ki daina fada mata bad things about me, na ga ai natsantsiya ce not like you that's why i like her With shock Khairy take kallonsa. Adam what's the meaning of all this? Sonta nake yi, and I'm ready to prove it, i want to talk to her parents da duk wani mai son hana alakata da ita tafiya I'm serious Khairy ta tsaya kallonsa for some seconds kamin ta dauke kai ta bude motar, Hurriya ma ta bude motar zata fita. Fita zata yi idan kika fita, ki zauna sai na gama magana da ita Ya fada da kamar fada yana kallon Khairy da bata fita motar ba, jin haka ya saka ta fasa fitar ta rufe motar, Hurriya kam bata tsaya ba ta fice ta tana ganin Adam ya bude motar ta ranta a na kare ta shige gida da sauri, a fusace ya dawo motar ya rufe Khairy da fada Kin ga abun da kike ja ko? Kin dauki tsanata kin sakawa yarinyar har guduna take Toh wai kai Adam duk yan matan duniya ka rasa wa zaka so sai Hurriya? Yarinyar da ko jami'a bata fara ba Ba ruwanki Ya bude gurin da yake ajiyar kudi ya dauko rafar dubu daya ya mika mata Je ki gyara abun da kika bata ina son yarinyar nan ta so ni Khairy ta kalli kudin ta kalleshi, kamar ta yi magana sai kuma ta saka hannu ta karba ta bude motar ta fita. Why Adam why... Ta fada cikin yanayin damuwa da gajiyawa tana tafiya ba tare da ta juyo ba. _____________________ Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku. Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... Littafin nan na kudi ne, ba free ba, idan kika karanta ba tare da biya ba kin daukarwa kanki nauyi domin hakkina ne kika rataya a wuyanki. Biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence of payment to 08036126660 Sai da Hurriya ta shigo gidan sannan ta daina gudu, sai dai hango Hajiya Kaltume tsaye a karamin gate din part dinta ya kara daga mata hankali sosai domin irin tsayin da Hajiya ta yi ya nuna kamar ita take jira. Rage tafiyar da take ta yi gabanta na faduwa tana ta sake sake domin ta san halin Hajiya Kaltume da ma Khairy din za su iya wanke kansu ita su jefata a ruwa. Tana daf da shigewa bangaren Momy Hajiya Kaltume ta yi kiranta da hannu, a lokacin ne tsoro ya kara cika zuciyar Hurriya, haka dai ta daure ta karasa gurin da take tsaye. Hajiya gani Ina kika fito? Yaya Khairy na raka waje gurin Saurayinta Hajiya Kaltume ta yi fuskar mamaki. Saurayinta kuma? Waye? Ban san shi ba ni ma Okay. Je ki BQ din Nafisa ki kira min Kulu, kuma ban ce ki fadawa Nafisa ba, sannan ki fada mata ta same ni bangarena magana ce mai muhimmanci ki kirata dabam ki fada mata ba a cikin mutane ba To Hajiya Ta mike tsaye tana jin sanyi a ranta, na rashin zafafa bincike ko binta da zagi da Hajiya Kaltume bata yi a yau. Tana shiga gate din da nufi BQ din Momy har karamar kofar bangaren masu aikin ta fara budewa ta shiga ciki, dukansu suna waje suna hira har da dare dare. Mama Kulu ina wuninku Ta gaishesu, duk suka amsa mata har Kulu, sannan Hurriya ta ce. Mama Kulu wai ki zo Ta nuna kanta. In ji wa? Dayar dake zaune kusa da ita ta saka dariya. Ke ma dai da neman tsawaita zance kike, waye zai kiraki duk gidan nan ban da Momy? Kuma tun da kika ga Hurriya a kin san ita take nemanki Hurriya dai bata ce komai ba ta juyo ta fara tafiya, a bakin kofar ta tsaya har sai da Kulu ta fito sannan ta tare tace. Ba Momy ke nemanki ba, Hajiya Hajiya kuma? She asked with shock. Eh nima na dawo daga waje na ganta tsaye tace na kiraki kuma kar na bari kowa ya ji, ta ce ki same ta bangarenta magana ce mai muhimmanci Toh... Allah yasa dai lafiya Hurriya dai ban da kallonta babu abun da ta yi, domin ita ma bata san dalilin kiran ba balle ta fada mata ita kuma bata daina faduwar gaba ba har ta isa bangaren na Hajiya Kaltume. Daman Hurriya tana isar mata da sako ta shiga bangaren Momy ta bar a guri.. Cikin tsoro ta shiga falon da Momy tana sallama. Ruma ce kadai zaune a falon tana cin abinci, hannu ta sauke ta aje plate a kasa bayan ta amsa sallamar Kulu, ita kanta mamakin ganinta a bangaren take. Hajiya na ciki ta ce tana son ganin Eh tana ciki bari na kirata Ta mike tsaye tana tsude hannu ta nufi stairs, slowly ta tura kofar dakin Hajiya ta lake. Hajiya ga Kulu mai aikin Momy a kasa tana nemanki Je ki ce mata ta shigo Nan eh? Ta juya ta koma, tun kamin ta karasa saukowa ta fadawa Kulu sakon Hajiya Kaltume. Ta ce ki shigo Na shigo kuma? Ruma ta daga mata kai, Kulu ta daga kai ta kalli stairs din da bata taba hawa ba, tun zuwanta gidan, shigarta bangaren Hajiya Kaltume ma za a iya kidayashi domin bata zuwa sai idan Momy ta aikota, kuma ba kasafai Momy take haka ba. Da tsoro Kulu ta taka ta hau stairs sai ta rasa wane daki zata shiga domin duka dakunan a rufe suke kuma bata taba kaiwa gun ba balle ta gane wanene dakin Hajiya Kaltume. Kwatantawa ta yi da dakin Momy sai ta isa bakin kofar dakin ta yi sallama ta kwankwasa. Shigo Ta murda kofar ta shiga
Chapter 58 · 0% Book details