Sashe 131
Huriyya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
za'a nema, sai dai Hajiya tace min mu daga kafa zuwa nan da kwana biyu zata tafi ita da Hajiyar Maru sai su yi maganar tarewar domin abun ne da ya danganci mata, kuma na bata sako ta fadawa iyayenta mu dai yarinya muka aura ita muke so, ba dan mun raina arzikin ubanta ba, amman ba ma bukatar komai daga garesu zamu zuba komai daga nan garin da zata zauna har zuwa inda aiki zai kaika You're best Dad ever samun irinka Daddy sai an tona, Hurriya ta yi sa'ar samunka a matsayin suruki Akan kawo mana neman taimakon auren wasu ma mu yi balle kuma naka? Jamal ba dan kana son yarinyar nan ba no a kashin kaina yarinyar ta ba ni tausayi na halin rayuwar data samu kanta, ina tunanin idan da ace yata ce ya zan ji, yarinya karama an bata mata rayuwa da suna akan abun da bata aikata ba Akwai matukar tausayi Daddy, amman Ammy ta kasa gane haka Zata gane Son.. Zata gane.. Matsalar da aka samu Ammynka mace ce mai matukar son riya da alfahari ba irin wannan auren take son ayi ba, kuma su mata suna da wannan dabi'ar da rike abu balle kuma bata son yarinyar, dole sai ka yi hakuri with time zata fahimceka.. Ina fatan haka Bari na barka ka huta, zan aikawa mahaifinta da video yanzu, na san ba zai masa dadin kallo ba, amman ya kamata ya san gaskiya kuma ya san matakin da zai dauka ko dan nan gaba, amman da zaka hakura da yadawar wata kila zai fi, ya zai ji idan aka ce yarsa ce ta aikatawa yarsa haka? Daddy idan video be fita ba taya za a wanke Hurriya? Cikin alkawarin da na yi mata na fada mata cewar sai na yada wanda yayi mata wannan abun fiye da yadda aka yada hotunanta All the best... Get well soon Thank you Daddy Ya fita daga video call din ya sauke video da Salim ya turo masa yana kalla, a take ya ji kamar an yaye masa ciwon dake damunsa saboda farincikin yadda Adam ya bada labarin komai a video kamar yadda ya fadawa Captain da iyayensa banbancin wacan video da wannan, wannan video shi ya dora shi da kansa a shafinsa na tiktok kuma yana sanye da tufafi na kamala har da hula kamar mutumen arziki. Bayan ya gama kallo ya jira Ammy a wayar sai ta amsa tana shigo dakin domin tana daf da kofar dakin ne a lokacin da ya kira wayarta. Lafiya? Allah yasa ba jikin ba ne Ta karaso gurinsa da sauri. Captain dake jin kamar yau ce ranar angoncinsa ya mikawa Ammy wayar yana dariya. Ba shi ba ne, duba wannan ki gani Ta karbi wayar ta kunna video ta kalla, sai ta tabe baki ta zauna. Still dai ba zai goge hoton tsiraicin Hurriya da yake idanuwan mutane ba, kuma hakan ba zai hana ace kasan yarinyar nan da aka yada hotunan ta da wani saurayi ba? To Captain take auren yaron Engr A A Turaki ba Far'ar dake fuskar Captain sai ta soma disashewa, doman yayi tunanin hakan zai cire wani abu daga tsanar da Ammy take ma Hurriya. Tun farko kina kiyayya da ita ne saboda kina taya Momy kishi ne kawai saboda tana yar mijinta kuma Momy bata son Hurriya, Namra ma bata sonta, da kunnena na ji komai Ammy, kiyayyar da kike yi ma Hurriya ba na abun da ya faru ba ne kawai idan saboda shi ne ai kaddara ce da bata wuce kan kowa ba Haka ne, shiyasa mahaifinka zai yi mata komai ai, da yar wani mai arzikin ka aura kamar mahaifinka, ai ba zai yarda da wannan ba Shi ma ai be riga ya yarda ba, domin ba a taya masa ba kuma babu tabbacin zai amsa ko akasin haka shi ma yana son yarsa... Ya koma ya kwanta ya rufe idonsa... *** *** *** Cike da girmamawa Appa ya amsar wayar sukirinsa ta bangaren biyu, suka gaisa cikin mutunci da far'a Daddy ya tambaye shi rayuwa da kuma kasuwa suka ya amsa masa da hamdallar Allah. Daman na kira ne akan maganar Hurriya... Daddy ya dan yi shiru. Akan maganar tarewarta ne? Eh to...ba makasudin kenan ba, amman saboda ka fadi hakan bari na ce har da shi da na bar mata su yi wannan aikin ne Appa yayi murmushi. Daman ina da niyar na yi maka magana akan hakan, saboda ina neman Alfarmar ka daga mana kafa har zuwa ta samu lafiya, yanzu haka na fara shirye shiryen abun da ya dace ayi ne akan idonta, abun ba zai yi kyau ba amarya da makanta... Daddy yayi hanzarin tariyar numfashinsa. Ka kawar da wannan maganar, yanzu neman lafiyarta da cinta da shanta a abu ne da ya rataya a wuyan mijinta, kusan shi ne makasudin da ya saka nake son ta tare ai, saboda ya zama tana hannunmu mu zamu yi mata komai, ba lafiyarta kadai ba Alhaji Haruna har wata hidima da zaka yi akan Hurriya tun daga kayan daki har koma mun dauke maka Aa aa aa sam ba zan karbi wannan ba, na san kan yi kokari amman wannan bangaren kan a bar min shi, yarinyar tana daya daga cikin yaran da nake alfahari da su, kuma idan ban sakawa Hurriya na yi mata hidima mai kyau ba da me zan saka mata? Ni zan yi ma yata komai idan ka yi min haka ai kamar ka raina nawa arzikin ne ko kuma na ganin zan gaza ni kuwa zan baka mamaki Daddy ya ce. Ba wannan ba ne duka na so na yi hakan ne saboda kyautatawa, amman ba zan hana ka Allah yasa hakan ne mafi alheri Ameen na gode sosai Allah ya bar zumunci Ameen Ameen. Akwai video da zan aje maka a whatsapp yanzu, video ne da Adam yayi yake ba da hakuri na abun da yayi kuma yake fadar gaskiyar abin da ya faru, wanke Hurriya sosai a video Maa Shaa Allahu Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah Allah na gode maka Alhamdulillah Appa yana ta maimaitawa cikin farinciki. Sai dai bana son Hurriya ta ji a yanzu, kuma ina rokon Alfarmar ka kai Hurriya a asibiti yanzu ta duba mijinta ba shi da lafiya yana can kwance an saka masa drip Subhanallahi, me yake damunsa Ba wani serious ciwo ba ne fever ce kawai Toh ranka ya dade zan yi hakan, kuma ni ma zan je na duba shi anjima Na gode Daddy ya yanke jiran, Appa kuma ya shiga whatsapp dinsa ya kama number Daddy yana ta jiran sakonsa. Dilll sakon ya fado a wayar video ya fara bude kansa, daga kasan video kuma address din asibitin da Captain yake ne. Natsuwa sosai Appa yayi yana kallon yadda Adam ya fara bada hakuri da neman yafiyar Hurriya hannunsa da dauri, kana ganinsa ka san baya cikin farinciki kuma ya sha wahala domin jikinsa ya nuna haka, daga bisani ya koro da bayanin yadda abubuwan suka faru. Appa na zaune a office dinsa sai gashi a tsaye yana kallon video cikin firgici da mamaki yana jin duniyar gaba daya kamar mafarki. Khairy... Umm Khairi... Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un Ya koma ya zauna, yana ta neman daukin Allah ta hanyar ambatonsa kamin ya sake mikewa tsaye ya maida video baya ya kalla, ya sake kalla ya sake kalla. La'ilaha Illallahu... Ya karasa a zuciyarsa domin bakinsa ya masa nauyi kirjinsa ya kau yaji, kansa yayi nauyi har ya rasa abun da zai fara tunani. Ya aje wayar a tebur ya zauna yayi shiru na wasu mintuna yana kallon wani gurin kamin ya soke kai kasa yana sauke ajiyar zuciyar da ta ki sauka a zuciyarsa. Tunanin yake ta ina ya gaza a matsayinsa na uba, ta ina ya kyautata ta ina ne be kyautata ba? Me ya kawo haka a cikin familynsa ga yaran da suka shi ya haife su? Ya kai hannu ya dauki wayarsa ya shiga contact dinsa ya nemo number da ya kwashe shekaru be ji daga gareta ya kira. Sai da jiran ya yanke ya sake yin wani shi ma ya yanke a uku aka daga. Assalamu Alaikum Appa baya iya amsa sallama a yanzu dan haka be amsa ba, maganar ma kamar wanda aka dannewa numfashi haka yake yinta. Zan aiko da mota yanzu, za a dauki Hurriya taje asibiti ta duba mijinta ba shi da lafiya Wane irin magana ne wannan? Tun da ace mana an daura auren nan yau kwana biyu mutunen be zo ya ganta ba, fari ne ba ki ne mu ba mu san kamaninsa ba, sai kuma yanzu ka ce zata je ta duba shi? Ya daga yatsansa yana nunawa kamar ance masa tana gabansa a zaune. Dan Allah Iyami karki musa min, karki kara min bakinciki da bacin da nake ciki a yanzu, baki san halin da nake ciki ba matukar ba so kuke na fadi na mutu ku huta... Jin wannan kalamin ya saka Amma bata sake cewa komai ba har Appa ya kashe wayar, Direbansa dake gida ya kira ya fada masa yaje ua dauki Hurriya ya kaita asibitin, sannan ya dayan direbansa ya fada masa ya kunna mota za su tafi gida yanzu nan. Yasir ne last mutumen da ya kira ya fada masa ya same shi gida yanzu nan, sannan ya mike tsaye cike da nauyin zuciya irin na uban da yake jin kamar ya gaza ta wani bangaren ya fice daga office din. Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu