← Book details Bin Abinda Zuciya Ke So Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 100 OF 119

Sashe 100

Bin Abinda Zuciya Ke So Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

dake kara bayyanar da kamanninta da Rahima tana kallon Ummi da mahaifiyarta kafin ta matso kusada su ashagwabe tace "Ummi na nifa nikisaki Momma and hug me koyar uwarki kadai kikai missing?" ahankali Ummi tasaki yayarta tana kallon fuskan wacce tai maganan, cupping face dinta tayi tana kallonta murya chan kasa kaman zatai kuka tace "Safa" cikedaso matar tafada jikin Ummi tace "Ummi am sorry dan Allah kada kiyi fushi dani" rungumeta tight tayi sosai gabaki daya su Noor da Sameer duk sun tsaya suna kallonsu, Baffa kuma na gaisawa da magidanci, Baffa yace "kaga matan nan babu alamun zasu gama wanan gaishe gaishen yanzu anbarmu a tsaye muje ciki kahuta Alhaji" dariya akayi Safa ta dago kanta daga jikin Ummi ta kalli Sameer dahar lokacin ita yake kallo cikeda mamaki takama bakinta tace "Ummi haka Ya Sameer yadawo wani lutete kana ganinshi no body needs to tell you soja ne, rabon danaga Ya Sameer ina ganin yafi shekara goma sha biyar wlh duk bamu da zumunci jibi Noor da Muhammad duksun zankale an ijiye iyali, jibidai Mu'az da aka haifa agabana Ummi yaron dayasha fesomin zawon hakori duk innazo gaidaki" dariya duk akayi banda Mu'az daya zumburo baki, Momma tace "kibarni autana yasha iska, kumuje ciki" da sauri Safa tai wajen Sameer dan hararanshi tayi tace "kana wani feeling kanka danna cemaka Ya Sameer ganin su Ummi ne fa yasa nadaura Yaya akan sunan dududu da wata uku kacal fa ka girmen mara zumunci kawai" dan murmushi yamata yama kasa magana dan many things are running in his mind right now gawani anger dayaji yanaji yadai daure yacigaba da tafiya, har sukakai falo, zubewa akayi afalon aka shiga hira Safa ta janye gyalen lafayan daga kanta hakan yabama uban tulin gashinta daman fitowa dayasha gyara sai murmushi take she is so happy rabon ta dataga su Ummi ta manta saidai awaya, daman yaran duka ta manta rabon data gansu, lokacin datake Abuja tana yawan zuwa Sameer bayama kasan dan lokacin yatafi wani course a China, 3 and half years course ne saisa basu cika haduwa ba, su Noor kam lokacin duk suna University chan zaria. Ganin filter da Rahima ta rike tana tache citta ya fadi d aga hannunta hannunta narawa sosai yasa da sauri Fadila takama hannunta cikeda damuwa tace "sannu bar aikin bakida lpy, zauna" tajawo kujera ta daurata akai sanan tasakin mata murmushi tadau filter ta cigaba da aikin, Ummi ne tabude kofar kitchen din ta shigo tana kallonsu tace "sannunku da aiki" Fadila ce ta amsa tace "Ummi yanzu zamu kawo musu abincin naji sun iso, Ummi Rahima taje ta kwanta batada lpy jikinta rawa yake" dan murmushi Ummi tayi tashafa kan Rahima ahankali tace "akwai dalilin rawan, jini jini ne, sannu Rahima kihuta in kingama hutawa saiki fito ku gaisa, kufara gabatar musu da abinci da abubuwan sha Fadila" cikeda girmamawa sukace to Ummi sanan Ummi tajuya tafita sukuma suka fara jera abinci a tray suna fita da shi Rahima na zaune tana kallonsu harsuka fita da komi, Nabila tadawo kitchen din ta kalli Rahima dake zaune duktai wata kala tace "tashi muje falon mun gama fitar da abincin" gyadamata kai tayi tamike tsaye ahankali, sake faduwa gabanta yayi hakan yasa tadaura hannunta kan kirji da sauri Nabila tace "menene?" kaman zata fasheda kuka tace "gabana keta faduwa" wani irin mugun tausayinta Nabila taji gaskiya this small girl has been through so many things, kanta ta shafa tace "karki damu kidinga addu'a kinji" gyadamata kai tayi ahankali, Nabila tace "yauwa kokefa kinga yanda kayan nan suka miki kyau kuwa, gaskiya Ummi ta iya zabe, sun miki kyau sosai duk wanda ya ganki saiyaji kaman ya saceki Ya Sameer ya iya zabo mata" dan murmushi Rahima tayi Nabila tace "yauwa kokefa kinyi murmushi mutafi yanzu mune kawai bama falon anata cin abinci" gyadamata kai Rahima tayi Nabila ta bude kofa suka fita Rahima biyeda ita suka shigo dinning dan kana fitowa daga kitchen zaka shiga dining saika sauko daga stairs din dining ka shigo katoton falonsu. Wani irin faduwa da gaban Safa yadingayi tanajin step din tafiya azuciyarta yasa ta tsaya dacin abincin datakeyi chak, tana kallon spoon din da fried rice dinda ta debo keciki. "yauwa Ummi ga Rahiman nan" Nabila data fara fitowa daga dinning din tafadima Ummi datace mata takira Rahima, da sauri Safa tajuyo ta kalli dining din da babu wanda yabullo trying to see wanan matar Sameer din da acewanta takeda this special name. Ahankali Rahima da yanda gabanta ke faduwa sosai yasa tama kasa sauri tana tafiya kafafunta na hardewa babu ko kuzari daya tattare da ita tasa fararen hannunta dasuka sha lalle ta yaye labulen dinning din tafito tareda saukar da kafarta daya kan stairs din dining, dun! Dum!! Dudum!!! Gaban Rahima yawani irin fadi da tunda take aduniya bai taba fadi hakaba hada ido datayi da Safa da tunkafin ta bullo daga dinning din take kallon dining din longing to see who is coming out from this dinning, hada ido da sukayi da Rahima yasa numfashinta ya dauke gabaki daya na about 20sec sanan yadawo gabanta yamafi na Rahima faduwa, har abada, har abadan abidina bazata taba manta kamannin abinda ta tsugunna ta haifa ba, sanan ta raina for good 12yrs! Dakin kaman kowa naciki yamutu ko motsi bakaji sai sautin numfarfashi, yanda Safa ke kallon Rahima haka Momma da da Abu magidancin kusada ita ke kallonta, spoon din da Safa ta debo rice dashine ya subuce yafadi karan spoon din yadawo da koya hayyacin shi, cikin wani irin yanayi Momma ta taba Ummi dake kusada ita, cikin wata murya dazai nuna abubuwa daban daban na kunshe acikinta tace "Adda, Adda wani.....ke....g....ani haka?" tai maganan ararrabe, cikin zafin harshe Ummi tace "kin fini sani ai" dafa kujera Momma tayi tana kallon Rahima dahar lokacin kallonsu take one by one dudda she was small then but tsaf tagane mahaifiyar ta, sanan kakanta dan tana yawan zuwa gidan kakanninta da mahaifiyarta. Ahankali Momma ke tafiya tana dumfaro Rahima data janye idanunta dagakan Safa ta zubasu kan Momma Rahima tayi, idanun Momma sun kawo kwalla sosai tana tahowa da sauri zata rungume Rahima da sauri Rahima ta matsa gefe tareda saukowa daga kan stairs din tafara tafiya ahankali Momma kuma ta tsaya chak a inda Rahima tabarta awulakance, duk taku daya na Rahima sai Safa tajishi a zuciyarta har gaban Ummi Rahima tazo ta dage ta danne zuciyarta tahana kanta kuka ita karan kanta batasan she is this strong ba sai yau, murmushi ta kakalo ta sakinma Ummi tace "Ummi gani Anty Nabila tace kina kirana" murmushi itama Ummi tamata yauce rana ta farko datakeji kaman ta hadiye Rahima danso and she is ready to support Rahima akan kowani hukunci zata musu, cikeda so tace "eh jewel cewa nayi kufito kizo ki debi abincin ki kici" murmushi tasakeyi cikin yar siriruwan muryanta mai shegen dadi, tace "banjin yunwa yanzu Ummi, anjima zanci, kwanciya zanyi yanzu" gyadamata kai Ummi tayi tace "to shikenan yar albarka, jeki kwanta abinki" gyadama Ummi kai tayi kaman wata yar yarinya looking so adorable kaman ka kamota kacinye tai hanyar daki without giving anybody in the room another look, ahankali tabude kofa ta shige tareda maido kofan tarufe har cikin zuciyarta Safa taji karan buga kofan ta runtse ido da sauri wasu hawaye masu zafi sharrr suka zubomata. _I want to sold out yau bari kuga hotunan_ Da sauri Momma tazo wajen Ummi cikin wani irin yanayi tanuna kofar dakin da Rahima ta shiga tace "Adda Ra...Rahim.....a, jikana ne ta girma haka? Please kifadamin itace?" lumshe ido magidancin yayi yabudesu kafin ahankali ya ijiye kopin hannunshi kasa, Ummi dataji wani irin bala'in haushin su takeji tace "wanan tambayar kuma kezan mawa Saratu, keda jinin ki" hannu Momma tadaura kan fuskarta tafashe da kuka ahankali tace "innalillahi wa innailaihi raji'un, Allah natuba, Allah natuba, astagafurullah", ahankali Safa tasaka hannu ta share hawayen daya zubomata tass tadauki chokalin abincin ta daya fadi akasa tsabagen rashin sani meme zatayi tasashi cikin abincin ta debo abincin zatakai baki, cikin wani irin fushi da zafin rai Sameer yace "I swear if you dare take that food to your mouth I will choke you to death Safa!" tsabagen yanda ranshi ke tafarfasa yana kallonta dagakan kujeran dayake ance babba duk inda yake babba ne, Sameer feel at his age he can talk to kowa in his family koda agaban iyayensu ne, dago rinannun idanunta Safa tayi ta kalli Sameer ahankali, cikin fushi yace "bantaba sanin ajininmu akwai people dazan kalla naji dama ace ban hada komi dasuba sai akanku" yafada yana kallon Abu, Momma da itama Safan, yace "like how dare you Safa kikai abondoning abinda kika haifa da cikinki batare dakin kara waiwayanta daidai dasau daya ba bayan kin barta at the verge of death eh!?" yadaka mata tsawa daba ita kadaiba har saida sauran yan dakin suka girgiza, yace "wlh you are very very lucky, rabon dana hadu dake tun muna yara, harkikai aure in fact nibanma san kin haihuba, I knew nothing about haihuwan ki dako ina kike aduniyan nan dasaina nemoki and beat the stupidity out of your head nonsense!" yay shiru kirjinshi na tafarfasa yana kallonta Ummi bata hanashi magana ba ta tsaya tana kallonshi kawai with so much love and admiration tana kara godema Allah yanda ta tarbiyantar da mazajenta duk inta kalli Sameer tasan cewa she gave birth to a fearless leader anan wurin family coordinator, tasan kodayau zata fadi ta mutu, sanan Baffa yafadi ya mutu Sameer will coordinator this family yahada kan kowa and keep moving, Sameer is strong, bold, and fearless wanan ajininshi yake. Karkada kafa yayi yana kara tunano abubuwan da Rahima went through yace "kinsan wani abu?" yace "inhar baki roki yarinyar nan gafara tayafe miki ba kidena ganin ke mahaifiyar ta ce kenada hakkoki akanta, kidena ganin haka, wlh inhar this girl Rahima dakike gani dinan bata yafemiki ba Allah will punish you cus this girl went through hell, this are witness" yanuna su Noor da Ummi yace "Rahima has been through alot, alot kawai tanada rabone and Allah na kareta saisa but I truly feel disgusted over your act, what's the relationship between abinda mahaifinta yamuku da yarda
Chapter 100 · 0% Book details