Sashe 4
Sakatariya Ta Psrt 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Da sallama ta shigo tana ƙarewa cikin gidan kallo wanda ya sha sabon fenti da alama dai saboda bikin Hajara da Salima da za a yi ne.
Baaba Sabuwa ta fara gani wanda ihun yara ya sa ta fito daga kitchen. Duk cikin matan Baffa Musa ita Farida ke É—an gani da mutunci saboda itace uwargida kuma ba laifi tana da kirki.
"Oyoyo mutanen Jos. Sannu da zuwa"
Gyalenta ta saƙala ajikin igiyar shanya tana faɗin "fatan mun sameku lafiya"
"Lafiya lau, ya su Ummin na ku?"
Daga kitchen ta ke amsa ma ta da lafiya. Sai faman buÉ—e tukwane ta ke yi tana neman abin da za ta sa a baka.
"Baaba Sabuwa ni kam har yanzu ba ku bar baƙar al'adar ku ba, ace abincin rana sai ƙarfe uku"
"Lah yanzu na ke son É—aurawa ai"
Farida ta dubi wayar ta tana faɗin " a ƙarfe ɗayan!"...
Sai da dare Baffa ya sa aka kirata. A falon shi ta sameshi yana cin abincin dare. Bayan ya ma ta ya hanya sannan ya fara bayani " Aminah ta ce ba ki fara aiki ba dan haka zan sa Yakubu ya nema mi ki aiki a kamfanin da ya ke aiki ko za a dace kema ki samu. Kafin nan kuma ki cewa yaron da ke neman ki ya turo saboda mu san da gaske ya ke yi. Kin dai ga yanzu shirin auren ƙannen ki a ke yi, zuwa ƙarshen shekara ke ma ayi na ki"
"Ni dama na san dalilin cewa in dawo Kano kenan, ni Baffa ban san mi na tare ma ka ba. Kanata wani ƙannena-ƙannena, na ga su suka ƙi karatu su ka ce aure za su yi. Ni dana zaɓi karatu na yi kuma na gama ai sai a bar ni na ɗan sha iska kafin a fara maganar aure na"
Ya ma ta daƙuwa ya ce "Uban ki Farida, na ce kin ci ƙaniyar ki. Wato har yanzu ba ki bar rashin kunyar ki ba ko" .
"To Baffa ina zaman zamana a Jos, ka takura Ummi wai ta turoni Kano. Duk abinda na yi ai kai ka ji za ka iya..."
Marfin kwanon silver ya wurga ma ta ta kauce ba shiri. " ki kiyaye ni Farida wallahi zan mummunan saɓa mi ki. Tashi ki bani ware! Ja'ira kawai"
Sum-sum ta tashi ta fice a falon dan ta san ƙarshe zai iya marin ta ko ma ya daketa. Dan Baffa Musa akwai saurin hannu.
..........................
Ba ƙaramin kyau yai ba cikin shirin sa na riga da wando baƙi sai kuma blazer kalar navy blue. Ɗauke da briefcase ɗin sa ya sauko daga stairs ɗin cikin takunsa na girma da ƙasaita.
Ƙai tsaye wajen dining ya je inda iyalen gidan ke cin abinci. Ya sunkuya yaiwa wata budurwa peck a kumatu yana faɗin " good morning baby"
"Morning Big B" ta amsa tana ma sa murmushi
Itama Afrah da ke gefe ta ce " Good morning Yaya"
"Morning" ya faɗa a taƙaice.
Tea ɗin da ke gaban Baby ya ɗan ƙurɓa ya ce " sai na dawo ko"
Wata haÉ—aÉ—É—iyar mata da ke zaune opposite da Baby wanda tun saukowar shi idon ta ke kan sa ta ce "have breakfast with us, please"
A dararance ya kalleta ya ce "na gode Justice Nabilah"
Har ya bar falon ba ta dena kallon sa ba, zuciyar ta na ƙuna. Sai yaushe ne ɗan ta zai kira ta da sunan uwa? Sai yaushe alaƙar su zai dawo dai-dai kamar kowace uwa da ɗan ta? Shekaru sun ja amma har yau babu wata chanji tsakanin su.
Baby ta ce"Sorry Mom"
Justice Nabilah ta girgiza kai ta ce " kar ki damu Najdah" ta ƙaƙaro murmushin dole dan jaddada maganar da ta yi.
Ita dai Najdah jikin ta ne yai sanyi, har yau ta kasa gano dalilin ƙiyayyar Yaya Najeeb da Mom, wanda tun tasowar ta haka ta same su.
Tambayar duniyar nan ta yiwa Big B da Mom amma duka babu wanda ya bata gamsashshiyar amsa. Harta Daddy bai san dalilin wannan gabar ba. Tun yana faɗa akan wannan ƙiyayyar ta su har ya haƙura ya zuba mu su ido...
Tunda ya fita daga gidan kai tsaye wajen motar sa ya wuce. Wanda tuni aka fito ma sa da ita daga parking lot. Sau ɗari zai ɗau driver sau ɗari zai koresu. Shi ya sa yanzu kusan wata uku kenan rabon da ya sake ɗaukan driver. Shi ya ke tuƙa kan sa, ran da yake son yin aiki a cikin mota kafin ya ƙarasa office to zai sa drivern Daddy ya kai shi office.
*Najeeb Adam Jibo*
matashin da ya ke ji da kyau,kuÉ—i,ilimi da kuma gata. ÆŠa namiji guda ga tsohon Ambassador kuma Professor Adam Jibo da Justice Nabilah Al-Jabir.
Adam Usman Jibo ɗan asalin ƙaramar hukumar Kumo ne da ke jahar Gombe, sai dai kasancewar tun rasuwan mahaifinshi ya dawo wajen ƙanin Baban sa da ke Kano da zama ya saka zamansa ya koma Kano. Alhaji Mustafah Jibo babban ɗan kasuwa ne da ya ke da arziƙo tun a wancan lokacin.
lokacin da Adam ke da shekara bakwai a duniya mahaifin sa ya rasu, dan haka zaman sa da shi da ƙannen sa mata biyu su ka dawo hannun Alhaji Mustafah , lokacin Mustafah da matar sa shekarar su takwas da aure amma basu taɓa haihuwa ba. Sun riƙe Adam da ƙannen sa Ruƙayya da Fatima tamkar 'ya'yan da su ka haifa. Sai da su ka shekara goma sha biyar da aure ba haihuwa sannan Hajiya Mama wanda haka su Adam ke kiranta ta dage akan lallai Alhaji Mustafah ya ƙara aure ko za a dace.
Wata ƙanwar maƙocinsa kuma amininsa ya aura. Budurwace dan a lokacin da aka yi auren su shekararta shashida. Cikin ikon Allah watan Halima goma ta haifi ɗan ta namiji ya ci suna Sulaiman. Murna wajen Alhaji Mustafah ba a magana. Bayan Sulaiman ta haifi Abubakar sai da ta shekara huɗu kafin ta haifi Aisha wanda lokacin haihuwanta ta wahala sosai, tun lokacin haihuwar kuma ta ke jinya bayan sati uku ta rasu. Mutuwar da ta girgiza iyalen Alhaji Mustafah gaba ɗaya.
Hajiya Mama ba ta haifa ba amma ta ɗauki duka yaran tamkar ita ta haifesu, wanda ko kaɗan ba za ka taɓa ganin abu ɗaya da zai nuna ma ka ba ita ɗin ta haife su ba. Ba ma kamar Aisha wanda ita ta shayar da ita. Haka yaran su ka taso ba su da wata uwa da ta wuce Hajiya Mama. Kuma har lokacin da Alhaji da Hajiya Maman ba wanda ya banbanta tsakanin yaran marigayi Usman Jibo da kuma ainihin yaran Alhajin. Sai dai a hankali su ka fahimci Aisha ba ta magana, kurmiya ce. Anyita magani amma shiru, tana ji amma ba ta iya magana. Wannan lalura ta sa da Alhaji da Hajiya Mama su ka maida hankalin su wajen kula da Aisha sosai.
Da Adam ya gama primary school na shi Alhaji Mustafah ya kaishi Lagos karatu. Bayan kammala secondary school na shi a kings college da ke Lagos ya wuce Harvard yai degree ɗin sa a fannin International relation,daga nan ya wuce London Business school yai wani degree ɗin a fannin Business sannan yai masters na shi da Phd a Yale University. Ya fara koyarwa a Yale kafin Nigeria ta tura shi Canada a matsayin Ambassador daga nan aka maida shi USA daga USA sai Belgium daga nan sai South korea wanda daga south korea ɗin ne yai retire ya dawo Nigeria inda yai zaman shekara ɗaya yana hutawa, gomnati ta mi shi chaaa akan ya shigo siyasa a dama da shi sai dai shi ya fi son koyarwa saboda ya amfanar da mutane ilimin da ya tara. An awarding na shi professor kuma yana visitin lecturer a jami'o'i da dama a ƙasar, musamman ABU, BUK, UJ, UI da sauran su.
Adam Jibo ya haɗu da Nabilah Aljabir ne a Yale University lokacin yana masters na shi. 'Ya ce ga wani hamshaƙin mai kuɗi Aljabir Al Mukhtarr ɗan asalin ƙasar Bahrain. Soyayya ce mai ƙarfi ta shiga tsakanin su tun haɗuwar su a library. Ba ƙaramin sa'insa aka samu ba kafin aka amince da auren su musamman da ya ke tana balarabiya shi yana bafulatanin Nigeria. Sai dai Nabilah ita kaɗai ce 'ya mace a wajen mahaifinta kuma mahaifinta na son ta sosai.
Bayan auren su da shekara ɗaya ta haifi Najma wanda sunyi niyyar sawa yaransu sunayen da su ka fara da harafin N da A da J. Harafin N saboda Nabilah, harafin A da J kuma na Adam Jibo. Bayan shekara uku ta haifi Najeeb wanda daga shi sai da shekaru su ka ja kafin Najdah ta zo duniya, kusan shekara sha uku Najeeb ya bata. Dawowar su Nigeria Nabilah ta yi Pre Law school na wata shida kasancewar a ƙasar waje ta yi karatu kafin ta yi regular Law school. Ta yi aiki a kotuna da dama kafin daga bisani ta kai matsayin Justice.
Najma ɓangaren likitanci ta karanta tana aiki a National hospital Abuja a matsayin gyneacologist. Tana auren wani hamshaƙin mai kuɗi ɗan kasuwa kuma likita Dr Mujahid, yanzu haka yaran su uku.
Baaba Sabuwa ta fara gani wanda ihun yara ya sa ta fito daga kitchen. Duk cikin matan Baffa Musa ita Farida ke É—an gani da mutunci saboda itace uwargida kuma ba laifi tana da kirki.
"Oyoyo mutanen Jos. Sannu da zuwa"
Gyalenta ta saƙala ajikin igiyar shanya tana faɗin "fatan mun sameku lafiya"
"Lafiya lau, ya su Ummin na ku?"
Daga kitchen ta ke amsa ma ta da lafiya. Sai faman buÉ—e tukwane ta ke yi tana neman abin da za ta sa a baka.
"Baaba Sabuwa ni kam har yanzu ba ku bar baƙar al'adar ku ba, ace abincin rana sai ƙarfe uku"
"Lah yanzu na ke son É—aurawa ai"
Farida ta dubi wayar ta tana faɗin " a ƙarfe ɗayan!"...
Sai da dare Baffa ya sa aka kirata. A falon shi ta sameshi yana cin abincin dare. Bayan ya ma ta ya hanya sannan ya fara bayani " Aminah ta ce ba ki fara aiki ba dan haka zan sa Yakubu ya nema mi ki aiki a kamfanin da ya ke aiki ko za a dace kema ki samu. Kafin nan kuma ki cewa yaron da ke neman ki ya turo saboda mu san da gaske ya ke yi. Kin dai ga yanzu shirin auren ƙannen ki a ke yi, zuwa ƙarshen shekara ke ma ayi na ki"
"Ni dama na san dalilin cewa in dawo Kano kenan, ni Baffa ban san mi na tare ma ka ba. Kanata wani ƙannena-ƙannena, na ga su suka ƙi karatu su ka ce aure za su yi. Ni dana zaɓi karatu na yi kuma na gama ai sai a bar ni na ɗan sha iska kafin a fara maganar aure na"
Ya ma ta daƙuwa ya ce "Uban ki Farida, na ce kin ci ƙaniyar ki. Wato har yanzu ba ki bar rashin kunyar ki ba ko" .
"To Baffa ina zaman zamana a Jos, ka takura Ummi wai ta turoni Kano. Duk abinda na yi ai kai ka ji za ka iya..."
Marfin kwanon silver ya wurga ma ta ta kauce ba shiri. " ki kiyaye ni Farida wallahi zan mummunan saɓa mi ki. Tashi ki bani ware! Ja'ira kawai"
Sum-sum ta tashi ta fice a falon dan ta san ƙarshe zai iya marin ta ko ma ya daketa. Dan Baffa Musa akwai saurin hannu.
..........................
Ba ƙaramin kyau yai ba cikin shirin sa na riga da wando baƙi sai kuma blazer kalar navy blue. Ɗauke da briefcase ɗin sa ya sauko daga stairs ɗin cikin takunsa na girma da ƙasaita.
Ƙai tsaye wajen dining ya je inda iyalen gidan ke cin abinci. Ya sunkuya yaiwa wata budurwa peck a kumatu yana faɗin " good morning baby"
"Morning Big B" ta amsa tana ma sa murmushi
Itama Afrah da ke gefe ta ce " Good morning Yaya"
"Morning" ya faɗa a taƙaice.
Tea ɗin da ke gaban Baby ya ɗan ƙurɓa ya ce " sai na dawo ko"
Wata haÉ—aÉ—É—iyar mata da ke zaune opposite da Baby wanda tun saukowar shi idon ta ke kan sa ta ce "have breakfast with us, please"
A dararance ya kalleta ya ce "na gode Justice Nabilah"
Har ya bar falon ba ta dena kallon sa ba, zuciyar ta na ƙuna. Sai yaushe ne ɗan ta zai kira ta da sunan uwa? Sai yaushe alaƙar su zai dawo dai-dai kamar kowace uwa da ɗan ta? Shekaru sun ja amma har yau babu wata chanji tsakanin su.
Baby ta ce"Sorry Mom"
Justice Nabilah ta girgiza kai ta ce " kar ki damu Najdah" ta ƙaƙaro murmushin dole dan jaddada maganar da ta yi.
Ita dai Najdah jikin ta ne yai sanyi, har yau ta kasa gano dalilin ƙiyayyar Yaya Najeeb da Mom, wanda tun tasowar ta haka ta same su.
Tambayar duniyar nan ta yiwa Big B da Mom amma duka babu wanda ya bata gamsashshiyar amsa. Harta Daddy bai san dalilin wannan gabar ba. Tun yana faɗa akan wannan ƙiyayyar ta su har ya haƙura ya zuba mu su ido...
Tunda ya fita daga gidan kai tsaye wajen motar sa ya wuce. Wanda tuni aka fito ma sa da ita daga parking lot. Sau ɗari zai ɗau driver sau ɗari zai koresu. Shi ya sa yanzu kusan wata uku kenan rabon da ya sake ɗaukan driver. Shi ya ke tuƙa kan sa, ran da yake son yin aiki a cikin mota kafin ya ƙarasa office to zai sa drivern Daddy ya kai shi office.
*Najeeb Adam Jibo*
matashin da ya ke ji da kyau,kuÉ—i,ilimi da kuma gata. ÆŠa namiji guda ga tsohon Ambassador kuma Professor Adam Jibo da Justice Nabilah Al-Jabir.
Adam Usman Jibo ɗan asalin ƙaramar hukumar Kumo ne da ke jahar Gombe, sai dai kasancewar tun rasuwan mahaifinshi ya dawo wajen ƙanin Baban sa da ke Kano da zama ya saka zamansa ya koma Kano. Alhaji Mustafah Jibo babban ɗan kasuwa ne da ya ke da arziƙo tun a wancan lokacin.
lokacin da Adam ke da shekara bakwai a duniya mahaifin sa ya rasu, dan haka zaman sa da shi da ƙannen sa mata biyu su ka dawo hannun Alhaji Mustafah , lokacin Mustafah da matar sa shekarar su takwas da aure amma basu taɓa haihuwa ba. Sun riƙe Adam da ƙannen sa Ruƙayya da Fatima tamkar 'ya'yan da su ka haifa. Sai da su ka shekara goma sha biyar da aure ba haihuwa sannan Hajiya Mama wanda haka su Adam ke kiranta ta dage akan lallai Alhaji Mustafah ya ƙara aure ko za a dace.
Wata ƙanwar maƙocinsa kuma amininsa ya aura. Budurwace dan a lokacin da aka yi auren su shekararta shashida. Cikin ikon Allah watan Halima goma ta haifi ɗan ta namiji ya ci suna Sulaiman. Murna wajen Alhaji Mustafah ba a magana. Bayan Sulaiman ta haifi Abubakar sai da ta shekara huɗu kafin ta haifi Aisha wanda lokacin haihuwanta ta wahala sosai, tun lokacin haihuwar kuma ta ke jinya bayan sati uku ta rasu. Mutuwar da ta girgiza iyalen Alhaji Mustafah gaba ɗaya.
Hajiya Mama ba ta haifa ba amma ta ɗauki duka yaran tamkar ita ta haifesu, wanda ko kaɗan ba za ka taɓa ganin abu ɗaya da zai nuna ma ka ba ita ɗin ta haife su ba. Ba ma kamar Aisha wanda ita ta shayar da ita. Haka yaran su ka taso ba su da wata uwa da ta wuce Hajiya Mama. Kuma har lokacin da Alhaji da Hajiya Maman ba wanda ya banbanta tsakanin yaran marigayi Usman Jibo da kuma ainihin yaran Alhajin. Sai dai a hankali su ka fahimci Aisha ba ta magana, kurmiya ce. Anyita magani amma shiru, tana ji amma ba ta iya magana. Wannan lalura ta sa da Alhaji da Hajiya Mama su ka maida hankalin su wajen kula da Aisha sosai.
Da Adam ya gama primary school na shi Alhaji Mustafah ya kaishi Lagos karatu. Bayan kammala secondary school na shi a kings college da ke Lagos ya wuce Harvard yai degree ɗin sa a fannin International relation,daga nan ya wuce London Business school yai wani degree ɗin a fannin Business sannan yai masters na shi da Phd a Yale University. Ya fara koyarwa a Yale kafin Nigeria ta tura shi Canada a matsayin Ambassador daga nan aka maida shi USA daga USA sai Belgium daga nan sai South korea wanda daga south korea ɗin ne yai retire ya dawo Nigeria inda yai zaman shekara ɗaya yana hutawa, gomnati ta mi shi chaaa akan ya shigo siyasa a dama da shi sai dai shi ya fi son koyarwa saboda ya amfanar da mutane ilimin da ya tara. An awarding na shi professor kuma yana visitin lecturer a jami'o'i da dama a ƙasar, musamman ABU, BUK, UJ, UI da sauran su.
Adam Jibo ya haɗu da Nabilah Aljabir ne a Yale University lokacin yana masters na shi. 'Ya ce ga wani hamshaƙin mai kuɗi Aljabir Al Mukhtarr ɗan asalin ƙasar Bahrain. Soyayya ce mai ƙarfi ta shiga tsakanin su tun haɗuwar su a library. Ba ƙaramin sa'insa aka samu ba kafin aka amince da auren su musamman da ya ke tana balarabiya shi yana bafulatanin Nigeria. Sai dai Nabilah ita kaɗai ce 'ya mace a wajen mahaifinta kuma mahaifinta na son ta sosai.
Bayan auren su da shekara ɗaya ta haifi Najma wanda sunyi niyyar sawa yaransu sunayen da su ka fara da harafin N da A da J. Harafin N saboda Nabilah, harafin A da J kuma na Adam Jibo. Bayan shekara uku ta haifi Najeeb wanda daga shi sai da shekaru su ka ja kafin Najdah ta zo duniya, kusan shekara sha uku Najeeb ya bata. Dawowar su Nigeria Nabilah ta yi Pre Law school na wata shida kasancewar a ƙasar waje ta yi karatu kafin ta yi regular Law school. Ta yi aiki a kotuna da dama kafin daga bisani ta kai matsayin Justice.
Najma ɓangaren likitanci ta karanta tana aiki a National hospital Abuja a matsayin gyneacologist. Tana auren wani hamshaƙin mai kuɗi ɗan kasuwa kuma likita Dr Mujahid, yanzu haka yaran su uku.