Sashe 7
Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nasu da wata matsala Sai matsalar ciwon Usman da Ummul,
wasa-wasa ko wanne wota Ummul sai ta galabai ta abin yaci tsura tasha magunguna da allurai har tagaji a banza.
Abba kuwa ya matsala Nenne da tabbayarshin dama haka ko wacce mace take fuskantar wannan matsalar ne yayin yin al'adarta.
Nenne takan ce mishi .
"Insha Allah in tayi aure zai bari."
A haka suka bar maganar.
Sai yau kuwa tunda gari ya waye Ummul ta tashi da. ciwon ciki da matar ga sarawar da k'ugunta keyi.
Kasan cewa Hamma Umar baya gida yana cikin Damaturu yasa Abba ya d'auketa shida Nenne suka kaita jama'a clinic kasan cewa doctor abokin Hamma Umar ne.
Gwajin forko da doctor yayi ya gane matsalar ta,
cikin girmamawa doctor yayiwa Abba baya nin ciwon nata ya kuma k'ara da cewa.
"Abba dama akan samu wasu matan da irin wannan larurar,
maganar gaskiya duk magungunan da za'a bata ko allurai duk aikin banza ne mafita d'ayace wacce zata rabata da ciwon nan da izinin Allah muddin akayi mata aure ta mu'amalantu da zaman takewar aure toh insha Allah zata rabu da ciwon nan."
Cikin kad'uwa Abba yace toh,
"Doctor menene mafita?."
Ajiyan zuciya ya sauk'e tare da cewa .
"Mafitar dai itace ayi mata aure kawai."
Da wannan shawarar Abba ya koma gida tare da Nenne Ita kuwa Ummul bata san abinda ke wakana ba.
Sai fama da takeyi da ciwon ta.
Bayan kwana biyu Abba ya kira Hussain shi suka zauna a d'akin Hajjajo suka tattauna kan maganar Ummul su yasu suka gama maganarsu
ba and a yasan abinda suka zantar.
Yau jumma'a tun safe Ummul keta gyare-gyare da girkr-girke dan yau Habeebin ta Mustapha yana kan hanyarshi ta zuwa,
4:15 pm Mustapha ya iso,
yana isowa Abba da Hamma Umar suka shigowa,
da sauri Mustapha yayi parking ya fito ya nufi su Abba yana zuwa kusa dasu,yayi sauri ya....
By
*GARKUWAR FULANI*
ðŸ“ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
*RUBUTACCEN AL,AMARI*
Page 6⃣
*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*
ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
Ya tsugana gaban Abba cikin girmamawa irin ta tsurkai ya yace.
"Barka da dawo Abba."
"Barka dai Mustapha ya hanya?."
"Alhamudulallah Abba."
"Masha Allah ,
taso ka isa daga ciki ko."
Mik'ewa yayi cikin kunya tare da d'an murmushi a fuskar sa,
gaban Hama Umar ya matso cikin sakin fuska ya mik'a mishi hannu.
Shima Hamma Umar d'in d'an gajeren murmushi yayi tare da mik'o hannunshi suka gaisa.
Abbanne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa.
"Farouq isar dashi parlour ciki."
"Toh" yace sannan yayi gaba Mustapha na biye dashi a baya.
Shi kuwa Abba part d'in shi ya nufa.
Suna zuwa Umar ya kalli Mustapha a fakaice yace.
"Ka isa ni zanyi cikin gida."
"Toh nagode Hamma Umar Allah bar girma."
"Amin" yace a tak'aice sannan ya fita ,
cikin gida ya wuce parlour Hajjajo ya nufa,
yana zuwa yayi sallama jin shiru ba wanda ya amsa yasashi shigowa a hankali,
parlour ba kowa,
kan 2. str ya zauna tare da dan jingina jikin kujarar ido ya lumshe yana mai fidda numfashi a hankali,
Hajjajo ce ta fito parlour hannun ta rik'e da carbi ido ta d'an zare tare da cewa.
"Kai Umaru yashe ka shigo?."
"Yanzu."
ya bata amsa a gajarce,
gefen shi taje ta zauna ta d'an kalleshi tare da tab'e baki tace.
"Hmmm yau kuma halin ya motsone?."
bai kulata ba sai zamewa yayi ya konta kan kujeran,
ganin haka itama ta koma gefe ta zauna tana murmushi tana mamakin hali irin na Umar mutun ba'a gane inda ya dosa.
A parlour Nenne kuwa Usman ne zaune yana kallon yadda Ummul ke zuba shek'i tayi kolliya mai kyau tayi shigarsu na shuwa'arab ta tubke gashinta tayi ras da ita riga da siket ne a jikin ta sunyi d'as gwanin shawa sai laffaya da ta yane jikin ta dashi har zuwa sama tayi irin yanawar da y'an mata sukeyi,
ga wani irin k'amsi da take zubawa na turarukan humrarsu na shuwa,
fuska ya d'an tab'e ya kalleta a d'an gyatsine yace.
"Wai gasar kyau zaki je kike ta wannan kolliyar akan wannan Mustapha naki."
Murmushi tayi tare da d'an juya ido ta d'an tsuke bakinta lips d'inta tad'an had'e tayi taku d'aya zuwa biyu tace.
"Kai Ya Usman kaima da kanka kasan Mustapha da banne dole kuma komai nashi da banne."
Fuska ya kuma tsukewa ya kalli Anty Halima dake ta nad'a mata laffayar yace.
"Waike Halima me naki na zak'ewa kina shiryata kamar wata amarya."
Murmushi tayi sannan ta kalli Usman cikin fara'a tace.
"Ya Usman ai mace 'yar gyara ce."
Ya Adam ne ya kalli Ummul d'in da Halima cikin harara yace.
"Aiki ya same ku ai, ni wallahi sam Mustapha nan ba wani burgeni yake yiba kuma wallahi zan zuga su Abba a hanashi ma zuwa kawai ."
Lokaci d'aya fuskar Ummul ta canza gaba d'aya annurin ta ya gimtse.
Aliyu ne ya kalleta cikin tsokana yace.
"Ummul in an hanaki shi zaki mutu ko?
dan wallahi na lura jinshi kike kamar sarki."
Harara ta cillawa Aliyu fuska a tsuke tace.
"Mustapha yafi sarki a gareni shi shugaba zai zame min kuma shi tamkar jinina ne,
shine bugun zuciya ta duk randa na ratsashi na rasa farin cikina."
Ido Usman ya zuba mata yana mamakin yadda take son Mustapha,
Halima ko murmushi kawai tayi ,
Ya Sadik ne ya kalleta a tsokone yace.
"Kuma wallahi inaji a jikina bazaki auri Mustapha ba."
Juyawa tayi tana fita tare da cewa.
"Ashe ko duk wanda aka hanani Mustapha a dalilinshi toh tabbas yayi ban kwana da farin ciki a rayuwar sa zai fuskanci k'iyeyyar iya k'iyayya zai samu bak'in ciki mai isarsa."
Tana kaiwa nan ta fice,
Usman ne ya bita da sauri gaban ta ya tsaya cikin yin murmushi yace.
"Koda ko d'an uwanki ne?."
"Sosai ma ya Usman ko d'an uwa nane."
K'irjinshi ya dafe cikin lumshe ido yace.
"Koda ko nine ya Usman d'in ki?."
Dariya tayi cikin lumshe ido tace.
"Kai ai kai d'an uwa nane mai tayani son abin da nake so kai nasan bazaka zama silar bak'in cikina ba."
Tana fad'in haka ta wuce ta tafi,
shi ko Usman d'akin Hajjajo ya shiga yana murmushi gafen Hamma Umar d'in shi yaje ya zauna cikin sauk'e ajiyan zuciya yace.
"Hamma yau kuma k'irjina yana min nauyi."
Da sauri Hamma Umar ya mik'e tare da bud'e ido yana kallon Usman cikin tuhuma yace.
"Me kaci? kashe maganin ka ?."
Ido ya lumshe sannan yace .
"Allah ko Hamma na ba abin da naci,
maganin nedai ban shaba."
Hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa cikin mik'ewa tsaye ya fice .
Jim kad'an ya shigo hannushi rik'e da magungunan shi,
bashi yayi yasha sannan ya kalleshi a hankali yace.
"Jeka shirya kazo muje jama'a clinic na d'an dubaka sai mu biya,
baba aura chemist na d'auko ma magungunan ka d'an sun kusa k'arewa."
"Toh" yace sannan suka fito suka nufi part d'insu Usman ne ya fara wonka sannan yana fita Umar ya fitomai da kayan da zai saka,
shima ya shiga yayi wonkan yana fitowa ya shirya tsab,
shiga irin d'aya sukayi shigar shuwa'arab shigar da tafi kama da ta larabawa,
sun fito ras tamkar tagwaye komai nasu irin d'aya hatta tafiyar su farar fatarsu sajen fuskarsu kamace ta sak da sak suke sun fito ras tamkar taurari sai shek'i da k'amshi suke zubawa,
Suna fitowa Motar Umar suka shiga shi yake jan motar kai tsaye al'ameen restaurant suka nufa,
suna zuwa suka shiga can ciki,
lokaci d'aya aka had'a musu abinci dan sun saba zuwa wurin su maikatan har sunsan iya abincin da Usman ke iyaci so dama suna zuwa za'a kawo musu komai yadda ya kamata,
kamar yaro Umar ya tasa Usman a gaba saida yaci yayi tik sannan ya biya komai suka fito,
daga nan kuma clinic d'in suka wuce anan ya k'ara duba lafiyar d'an uwan nashi suna fitowa nan,
kai tasaye katafaren chemist d'inshi suka wuce,
ya had'a komai na maganin Usman d'in sannan,
suna fita Umar ya sake jansu sai dicency super market ,
suna zuwa Umar ya had'e musu duk wani abin buk'atan su sannan aka loda musu a mota suka fito suka nufi gida.
Ummul kuwa da Mustapha hirarsu sukayi sosai gaba d'aya sun susucewa juna hak'ik'a Mustapha yana son Ummul so na hak'ik'a haka itama take mishi so da iya gaskiyarta hirarsu suke basuma san maggariba tayiba saida suka ji kiran sallah,
Mustaphanne ya kalleta cikin tarin so ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya murya can k'asa yace.
"Ummul idanuna basa gajiya da ganin kekyawar fuskar ki! kunnuwana basa k'osawa da jin sautin ki mai zak'i ! hancina bayi da wani b'uri daya wuce shak'ar k'amshin ki,
Ummul ina sonki son da bana yiwa kaina."
Tafin hannun ta tasa ta rufe fuskar ta cikin jin dad'i da kunya tace.
"Habeebi dani da murya ta da fuskarta da k'amshi na duk naka ne."
Ido ya tsura mata tare da tasowa yazo gaban ta durk'usawa yayi a guiwowin shi a k'asa ido ya lumshe sannan ya bud'e su a hankali yace.
"Ina jin tsoro Ummul inajin tsoron karna rasaki Ummul har yanzu baki zama tawaba gashi ban san yaushe Allah zai mallaka min keba ina sonki inason mu kasance ma'aurata Ummul kimin al'k'awarin duk rinsi kina tare dani ki min tattalin kanki kada idon wani namiji ya dira a kanki."
Kallon shi tayi cikin murmushi tace.
"Ako da yaushe ina shaida maka kai Habeebi da'iman ne a gareni zuciya ta ba inda wani zai samu ma tsuguni."
Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan ya mik'e yana kallon ta,
itama mik'ewa tayi ta d'an matsa gefen shi,
cikin sanyi tace.
"Sai yaushe zaka kuma zuwa?."
"Ko gobe in kina so zanzo, ina damaturu ina potiskum garin masoyi baya nida."
"Gobe kam ai baka huta bama tukun."
"Hutu kuma Ummul aini bani da wani hutu har sai na ganki cikin gida na."
Murmushi tayi sannan tace,
" toh muje kayi sallan maggariba sai ka tafi kar dare ya maka."
"Kin gaji da ganina ne?."
"Inko zangaji da kallon fuskar ka toh zan gaji da kallon tawa fuskar kenan."
Murmushi yayi ya mik'a mata hannu wai suyi musabaha,
kai ta sunkuyar a hankali tace.
"Da saura."
wasa-wasa ko wanne wota Ummul sai ta galabai ta abin yaci tsura tasha magunguna da allurai har tagaji a banza.
Abba kuwa ya matsala Nenne da tabbayarshin dama haka ko wacce mace take fuskantar wannan matsalar ne yayin yin al'adarta.
Nenne takan ce mishi .
"Insha Allah in tayi aure zai bari."
A haka suka bar maganar.
Sai yau kuwa tunda gari ya waye Ummul ta tashi da. ciwon ciki da matar ga sarawar da k'ugunta keyi.
Kasan cewa Hamma Umar baya gida yana cikin Damaturu yasa Abba ya d'auketa shida Nenne suka kaita jama'a clinic kasan cewa doctor abokin Hamma Umar ne.
Gwajin forko da doctor yayi ya gane matsalar ta,
cikin girmamawa doctor yayiwa Abba baya nin ciwon nata ya kuma k'ara da cewa.
"Abba dama akan samu wasu matan da irin wannan larurar,
maganar gaskiya duk magungunan da za'a bata ko allurai duk aikin banza ne mafita d'ayace wacce zata rabata da ciwon nan da izinin Allah muddin akayi mata aure ta mu'amalantu da zaman takewar aure toh insha Allah zata rabu da ciwon nan."
Cikin kad'uwa Abba yace toh,
"Doctor menene mafita?."
Ajiyan zuciya ya sauk'e tare da cewa .
"Mafitar dai itace ayi mata aure kawai."
Da wannan shawarar Abba ya koma gida tare da Nenne Ita kuwa Ummul bata san abinda ke wakana ba.
Sai fama da takeyi da ciwon ta.
Bayan kwana biyu Abba ya kira Hussain shi suka zauna a d'akin Hajjajo suka tattauna kan maganar Ummul su yasu suka gama maganarsu
ba and a yasan abinda suka zantar.
Yau jumma'a tun safe Ummul keta gyare-gyare da girkr-girke dan yau Habeebin ta Mustapha yana kan hanyarshi ta zuwa,
4:15 pm Mustapha ya iso,
yana isowa Abba da Hamma Umar suka shigowa,
da sauri Mustapha yayi parking ya fito ya nufi su Abba yana zuwa kusa dasu,yayi sauri ya....
By
*GARKUWAR FULANI*
ðŸ“ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
*RUBUTACCEN AL,AMARI*
Page 6⃣
*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*
ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡ðŸ‡
Ya tsugana gaban Abba cikin girmamawa irin ta tsurkai ya yace.
"Barka da dawo Abba."
"Barka dai Mustapha ya hanya?."
"Alhamudulallah Abba."
"Masha Allah ,
taso ka isa daga ciki ko."
Mik'ewa yayi cikin kunya tare da d'an murmushi a fuskar sa,
gaban Hama Umar ya matso cikin sakin fuska ya mik'a mishi hannu.
Shima Hamma Umar d'in d'an gajeren murmushi yayi tare da mik'o hannunshi suka gaisa.
Abbanne ya kalli Hamma Umar d'in tare da cewa.
"Farouq isar dashi parlour ciki."
"Toh" yace sannan yayi gaba Mustapha na biye dashi a baya.
Shi kuwa Abba part d'in shi ya nufa.
Suna zuwa Umar ya kalli Mustapha a fakaice yace.
"Ka isa ni zanyi cikin gida."
"Toh nagode Hamma Umar Allah bar girma."
"Amin" yace a tak'aice sannan ya fita ,
cikin gida ya wuce parlour Hajjajo ya nufa,
yana zuwa yayi sallama jin shiru ba wanda ya amsa yasashi shigowa a hankali,
parlour ba kowa,
kan 2. str ya zauna tare da dan jingina jikin kujarar ido ya lumshe yana mai fidda numfashi a hankali,
Hajjajo ce ta fito parlour hannun ta rik'e da carbi ido ta d'an zare tare da cewa.
"Kai Umaru yashe ka shigo?."
"Yanzu."
ya bata amsa a gajarce,
gefen shi taje ta zauna ta d'an kalleshi tare da tab'e baki tace.
"Hmmm yau kuma halin ya motsone?."
bai kulata ba sai zamewa yayi ya konta kan kujeran,
ganin haka itama ta koma gefe ta zauna tana murmushi tana mamakin hali irin na Umar mutun ba'a gane inda ya dosa.
A parlour Nenne kuwa Usman ne zaune yana kallon yadda Ummul ke zuba shek'i tayi kolliya mai kyau tayi shigarsu na shuwa'arab ta tubke gashinta tayi ras da ita riga da siket ne a jikin ta sunyi d'as gwanin shawa sai laffaya da ta yane jikin ta dashi har zuwa sama tayi irin yanawar da y'an mata sukeyi,
ga wani irin k'amsi da take zubawa na turarukan humrarsu na shuwa,
fuska ya d'an tab'e ya kalleta a d'an gyatsine yace.
"Wai gasar kyau zaki je kike ta wannan kolliyar akan wannan Mustapha naki."
Murmushi tayi tare da d'an juya ido ta d'an tsuke bakinta lips d'inta tad'an had'e tayi taku d'aya zuwa biyu tace.
"Kai Ya Usman kaima da kanka kasan Mustapha da banne dole kuma komai nashi da banne."
Fuska ya kuma tsukewa ya kalli Anty Halima dake ta nad'a mata laffayar yace.
"Waike Halima me naki na zak'ewa kina shiryata kamar wata amarya."
Murmushi tayi sannan ta kalli Usman cikin fara'a tace.
"Ya Usman ai mace 'yar gyara ce."
Ya Adam ne ya kalli Ummul d'in da Halima cikin harara yace.
"Aiki ya same ku ai, ni wallahi sam Mustapha nan ba wani burgeni yake yiba kuma wallahi zan zuga su Abba a hanashi ma zuwa kawai ."
Lokaci d'aya fuskar Ummul ta canza gaba d'aya annurin ta ya gimtse.
Aliyu ne ya kalleta cikin tsokana yace.
"Ummul in an hanaki shi zaki mutu ko?
dan wallahi na lura jinshi kike kamar sarki."
Harara ta cillawa Aliyu fuska a tsuke tace.
"Mustapha yafi sarki a gareni shi shugaba zai zame min kuma shi tamkar jinina ne,
shine bugun zuciya ta duk randa na ratsashi na rasa farin cikina."
Ido Usman ya zuba mata yana mamakin yadda take son Mustapha,
Halima ko murmushi kawai tayi ,
Ya Sadik ne ya kalleta a tsokone yace.
"Kuma wallahi inaji a jikina bazaki auri Mustapha ba."
Juyawa tayi tana fita tare da cewa.
"Ashe ko duk wanda aka hanani Mustapha a dalilinshi toh tabbas yayi ban kwana da farin ciki a rayuwar sa zai fuskanci k'iyeyyar iya k'iyayya zai samu bak'in ciki mai isarsa."
Tana kaiwa nan ta fice,
Usman ne ya bita da sauri gaban ta ya tsaya cikin yin murmushi yace.
"Koda ko d'an uwanki ne?."
"Sosai ma ya Usman ko d'an uwa nane."
K'irjinshi ya dafe cikin lumshe ido yace.
"Koda ko nine ya Usman d'in ki?."
Dariya tayi cikin lumshe ido tace.
"Kai ai kai d'an uwa nane mai tayani son abin da nake so kai nasan bazaka zama silar bak'in cikina ba."
Tana fad'in haka ta wuce ta tafi,
shi ko Usman d'akin Hajjajo ya shiga yana murmushi gafen Hamma Umar d'in shi yaje ya zauna cikin sauk'e ajiyan zuciya yace.
"Hamma yau kuma k'irjina yana min nauyi."
Da sauri Hamma Umar ya mik'e tare da bud'e ido yana kallon Usman cikin tuhuma yace.
"Me kaci? kashe maganin ka ?."
Ido ya lumshe sannan yace .
"Allah ko Hamma na ba abin da naci,
maganin nedai ban shaba."
Hannu yasa ya d'an bugi k'eyarsa cikin mik'ewa tsaye ya fice .
Jim kad'an ya shigo hannushi rik'e da magungunan shi,
bashi yayi yasha sannan ya kalleshi a hankali yace.
"Jeka shirya kazo muje jama'a clinic na d'an dubaka sai mu biya,
baba aura chemist na d'auko ma magungunan ka d'an sun kusa k'arewa."
"Toh" yace sannan suka fito suka nufi part d'insu Usman ne ya fara wonka sannan yana fita Umar ya fitomai da kayan da zai saka,
shima ya shiga yayi wonkan yana fitowa ya shirya tsab,
shiga irin d'aya sukayi shigar shuwa'arab shigar da tafi kama da ta larabawa,
sun fito ras tamkar tagwaye komai nasu irin d'aya hatta tafiyar su farar fatarsu sajen fuskarsu kamace ta sak da sak suke sun fito ras tamkar taurari sai shek'i da k'amshi suke zubawa,
Suna fitowa Motar Umar suka shiga shi yake jan motar kai tsaye al'ameen restaurant suka nufa,
suna zuwa suka shiga can ciki,
lokaci d'aya aka had'a musu abinci dan sun saba zuwa wurin su maikatan har sunsan iya abincin da Usman ke iyaci so dama suna zuwa za'a kawo musu komai yadda ya kamata,
kamar yaro Umar ya tasa Usman a gaba saida yaci yayi tik sannan ya biya komai suka fito,
daga nan kuma clinic d'in suka wuce anan ya k'ara duba lafiyar d'an uwan nashi suna fitowa nan,
kai tasaye katafaren chemist d'inshi suka wuce,
ya had'a komai na maganin Usman d'in sannan,
suna fita Umar ya sake jansu sai dicency super market ,
suna zuwa Umar ya had'e musu duk wani abin buk'atan su sannan aka loda musu a mota suka fito suka nufi gida.
Ummul kuwa da Mustapha hirarsu sukayi sosai gaba d'aya sun susucewa juna hak'ik'a Mustapha yana son Ummul so na hak'ik'a haka itama take mishi so da iya gaskiyarta hirarsu suke basuma san maggariba tayiba saida suka ji kiran sallah,
Mustaphanne ya kalleta cikin tarin so ido ya lumshe tare da sauk'e ajiyan zuciya murya can k'asa yace.
"Ummul idanuna basa gajiya da ganin kekyawar fuskar ki! kunnuwana basa k'osawa da jin sautin ki mai zak'i ! hancina bayi da wani b'uri daya wuce shak'ar k'amshin ki,
Ummul ina sonki son da bana yiwa kaina."
Tafin hannun ta tasa ta rufe fuskar ta cikin jin dad'i da kunya tace.
"Habeebi dani da murya ta da fuskarta da k'amshi na duk naka ne."
Ido ya tsura mata tare da tasowa yazo gaban ta durk'usawa yayi a guiwowin shi a k'asa ido ya lumshe sannan ya bud'e su a hankali yace.
"Ina jin tsoro Ummul inajin tsoron karna rasaki Ummul har yanzu baki zama tawaba gashi ban san yaushe Allah zai mallaka min keba ina sonki inason mu kasance ma'aurata Ummul kimin al'k'awarin duk rinsi kina tare dani ki min tattalin kanki kada idon wani namiji ya dira a kanki."
Kallon shi tayi cikin murmushi tace.
"Ako da yaushe ina shaida maka kai Habeebi da'iman ne a gareni zuciya ta ba inda wani zai samu ma tsuguni."
Ajiyan zuciya ya sauk'e sannan ya mik'e yana kallon ta,
itama mik'ewa tayi ta d'an matsa gefen shi,
cikin sanyi tace.
"Sai yaushe zaka kuma zuwa?."
"Ko gobe in kina so zanzo, ina damaturu ina potiskum garin masoyi baya nida."
"Gobe kam ai baka huta bama tukun."
"Hutu kuma Ummul aini bani da wani hutu har sai na ganki cikin gida na."
Murmushi tayi sannan tace,
" toh muje kayi sallan maggariba sai ka tafi kar dare ya maka."
"Kin gaji da ganina ne?."
"Inko zangaji da kallon fuskar ka toh zan gaji da kallon tawa fuskar kenan."
Murmushi yayi ya mik'a mata hannu wai suyi musabaha,
kai ta sunkuyar a hankali tace.
"Da saura."