← Book details Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 77

Sashe 56

Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

*U*sman ya d'ago jajayen idanuwan shi yazuba matasu sannan ya mik'e yana layi yaje bakin gadon ya sa hannuwanshi biyu a d'auko Umar faruq ya rungume sosai a jikin shi yana zubda hawaye mai tsanani da zafi da k'una a zuciya yana shafa kan yaron dake cike da suma bak'ik'k'irin daya kwanta luf,
ita kuwa Ummul cikin kuka taci gaba da cewa,
"Hamma Umar ne rayuwa ta nafi sonshi a kan kowa a duniya, shikad'ai nakeso shine komai nawa na rasa a lokacin da nake tsananin buk'atarshi".
Tana magana ne cikin matsanan cin kuka, bakajin komai a gun sai shashshek'ar kuka da duk wanda kegun yakeyi,
shiko Usman yana k'ollah ne idanuwan shi na kan Umar faruq yana mai wani irin kallo kamar a lokacin yafara ganin halittar jariri,
Itakuwa Ummul cikin kuka taci gaba da cewa,
"Ammi wallahi ina sonshi,
bazan k'ara son wani mutum a duniyar nan bayan Hammana,
ina kaunar shi fiye da kaina Inamai matsanan cin so da duk duniya bamai iya fahimta".
sei ta kuma jan gwiwoyinta data zuba k'asa har gaban Ya Adam dake ta faman zubda k'ollah tace, "Yaya na kafi kowa yimin fad'a bakamin wasa amman na kasa ganewa,
kuma baka son damuwa ta, nasan kayi iya k'ok'arinka ka d'orani ka turbar gaskiya,
amman taurin kaina da rud'un shaid'an yasa nak'i gane abinda nasan gaskiya ne gashi hakan ya jazamin nadama ta har abadan na cutar da kaina da kaina naga illar rashin yiwa iyaye biyeyya, nagode dakaita k'ok'arin nunamin hanyar gaskiya".
Hannu yasa ya kama hanna yenta duka biyu ya d'an matsesu sannan yace,
"Ummul nasan kina son shi naga sonshi a idonki amma inaso ki nunamai soyayyar da kikemai inaso ya amfana da ita ta hanyar yimai addu a Ummu ki dena zubda mai hawaye".
kai ta rink'a gyad'awa cikin rauni da tsananin nadama,
saita kuma juya ta kalli Abba dake tsaye yana kallonsu ido cike da k'ollah,
sannan ta dawo da kallon ta ga Ya Adam dake murza yatsunta a hankali tace,
"Ya Adam Abbana yamin zab'i mafi al'khairi zab'i mai cike da al'kairai a rayuwata amma ina shaid'an ya hanani ganewa nayiwa iyayena taurin kai gashi zan dauwama cikin nadama da dana sanin rashin biyayya haka zan k'are rayuwata na kasa yiwa iyayenmu d'a'a kaitona Allah ya wadaran halina bani da wani abun koyi lallai duk yarda tayiwa iyayenta ba dai-daiba tana tare da nadama ya Adam na tsani kaina na cutar da Hamma na na b'ata ran mahaifanmu".
sai kuma ta kife kai wani irin matsanan cin kukane ya kwace mata wanda ya hanata k'arasa kalaman ta ta kife kanta a gwiwar Ya Adam jiki na rawa tana cewa,
"Wallahi ina son shi, inason Hamma Umar Yazanyi Hamma Umar yaga soyayya da kaunar da nakemai,
ya Adam kullum Hamma Umar yana cewa Ummul zaki soni, zakisoni lokacin da soyayyar bazata amfane muba ashe wannan lokacin ne Hamma na yake ganemin dana sani dana nuna mishi so da yake son in nuna mai lallai wannan shine kuskure mafi muni da yarinya tayi dan iyayenta sun mata auren dole".
kuka takeyi sosai tana cike da madama,
Aliyu ne yataho jiki ba kwari yasa hannu biyu ya d'agota ya durkusa gabanta a hankali yace,
"Aunty Ummul kiyi hak'uri, Hamma yace nine abokin shawararki abokin kukanki kuma me rarrashinki kiyi hak'uri kidena kukan nan kinga kinsa Ammi da Nanne kuka ga Abban mu shima yanayi kinga Hamma junior zaiji sautin kukan mu ki dena auntyna dan Allah".
Cikin galabaita da ajiyar zuciya ta kwantar da kanta a cinyar Aliyu tana sheshshe k'ar kuka tana nannad'e kafafun ta,
hannun Aliyu yasa yana shafa bayanta yana bubbugawa tare da share mata k'ollar cikin lallashi da haka bacci yayi gaba da ita,
su kuma Abba ya zauna yayi ta musu nasiha Usman kuma sai ajiyar zuciya yake sauk'ewa yana ruggume da farouq,
a haka rayuwa tayi ta juyawa rana d'ad'd'ayace
basa zama suyi kuka a hankali mutuwar ta fara shiga jikinsu,
lokaci yaja kwanaki sun tafi tuni Farouq ya cika kwana arba'in.

A bangaren Mustapha kuwa a kullum koda yaushe tunanin shi nakan Ummul da yaronta dan haka ranar Asabar suka shirya da umman shi suka nufo potiskum dan duba lfy Ummul da jaririnta, dai dai lokacin da motar Mustapha na shirin shiga harabar gidanne motar Dr Bashir ta sako kai dan fitowa wanda shima zuwa ganin Ummul da yaronta ya zame masa jiki a duk lokacin da baida aiki,
daga cikin mota suka gaisa da Mustapha sannan ya wuce cikin gidan shiko Dr bashir ya fita,
Kayane na gani na fad'a da suka had'a da sabulai man shafawa powder, pampers, wipers da sauran kayan jinjiri Mustapha ya lodo kamar me bud'e shagon mother care, duk na Umar faruq wanda Aliyu ke kira da junior,
Bayan ya gaisa da su Ammi da Nanne Aliyu yamai jagoranci zuwa palourn bak'i sannan ya kawomai abin sha sannan ya fita,
a cikin d'akin Kuwa Ammi ce ta maida hankalin ta kan Ummul dake zaune bakin gado cikin sigar lallashi da bada umarni da kulawa
tace,
"Ummu na ki kaiwa Mustapha yaron nashi ko".
Dakai ta amsa tad'au katon hijab ta saka sannan Umman Mustapha dake rik'e da Farouq ta mik'a matashi ta karb'a ta fice,
sukuma sukaci gaba da jajantawa juna irin jarrabawar da suka fuskanta.

Mustapha dake zaune yana latsa wayar shi sallamar Ummul tasa ya aje wayar a gefe yamik'e tare da amsa sallamar yamik'a hannu ya karb'i Farouq dake ta bacci sannan ya koma ya zauna yad'an dago kai yana kallon Ummul dake tafiya kamar mara lakka a jiki har ta sami kujerar dake fuskan tar wadda yake zaune ta zauna tai k'asa dakai tana wasa da yatsun hannun ta sannan yamai da kallon shi ga Umar faruq,
Shiru ya ratsa na y'an muntina sannan Ummul tai k'arfin hali tace,
"ina kwana".
Saida taji shirun yayi yawa sannan ta d'ago kanta a hankali tasauk'e idanun ta kan fuskar Mustapha dake rungume da Umar faruq kallon yaron cikin tsananin k'auna da tausayawa maraicin shi, lokaci d'aya tausayi shi ya rufeshi tuno Hamma Umar kawai sai idanun shi ya fara zubda k'ollah,
da sauri ta maida kanta k'asa ganin
hawayen Mustapha sai wani irin raunataccen kuka mai zafi ya kubce mata,
Mustapha da kyar ya dai-dai ta nutsu warshi sannan yace,
"Khairi dan Allah kiyi hak'uri banyi haka dan na saki kukaba please ki dena zubdawa Hamma Umar hawaye Insha Allah muna zata mai rahama gatan da zakiyi mishi addu'a ce".
ai kamar ya dad'a tunzura ta tacigaba da kukan da sauri ta mik'e ta fita daga palour cikin kuka a zahiri ko fuskar Mustapha bata son gani ji take sanadin shine tayi duk wani kuskure da taurin kai shiyasa da zaran ance mata yazo sai ta resa meke mata dad'i,
gashi shima in yazo kullum sai Farouq ya sashi Kuka tana fitan,
Mustapha yasake rungume Umar Faruq ya lumshe idanuwa yanajin kaunar yaron na ratsa duk wata gab'a ta jikin shi,
Dasu Ya Adam sukaita hira har lokaci yaja sannan yaje sukai sallama dasu Ammi suka kama hanyar damaturu.

Yau asabar wanda yayi dai-dai cika watanni 4 da Farouq yayi,
misalin k'arfe takwas Usman yafito daga b'angarensu sanye da farar jallabiya yanufi b'angaren Nanne kai tsaye d'akin Ummul ya shiga yasame su zaune da alama nono Ummul keba Umar Farouq ta yadda yaga tai maza ta sauke rigarta,
k'asa yayi da kai ya tsugunna ya kuma gaida Ammi sannan ya dago kai ya kalli Ummul yace,
"kawo shi".
mik'a shi tai batare da ta dago kantaba yasa hannu ya karb'e shi sannan yace,
"kinci abinci ne?".
Kai ta girgiza alamar a a d'an juyawa yayi ya kalli Ammi kafin yayi magana Ammin tace, "kaga abincin nan zataci kenan yaron yafarka daga bacci,
to nabashi ruwa yasha nace taci sannan ta ba shi nonon,
amma saina ga hankalin ta bai kwanta da hakan ba, shiyasa nabata shi yasha tukuna".
Murmushin karfin hali yayi ya kalli Ummul ya jijjiga kai ya juya rungume da yaron shi, a parlour su ya zauna ya kwantar da Faruq kan cikin shi ya zubamai ido saikuma ya fashe da kuka mai cin zuciya da k'unar rai yana kad'a kai wanda hakan yazama al'adarsa yana dawowa daga aiki zai d'auki Faruq yaje yasashi a gaba yaita aikin zubda k'ollah yana tuno d'an uwanshi Hamman shi abin begenshi.

Ammi ce zaune tana kallon farcen hannun ta taga yanda suka fito sukai tsayi nan da nan ta tuna gudan jininta wanda tunda yayi wayo shike yanke mata farce dan haka ta manta da lokacin da ta yanke farce ta a rayuwar ta, hannu tasa ta d'auko abin yankan farce sannan ta koma ta zauna kan carpet ta fara gwada yankewan sai abin ya murd'e mata lokaci d'aya begen Farouq d'inta ya rufeta mutuwar ta dawo mata sabuwa kawai sai ta kifa kai jikin gado tasaki matsanan cin kuka mai cike da tausayi.
Chapter 56 · 0% Book details