← Book details Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 77

Sashe 23

Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*K*allon ta yayi cikin mamaki ganin yadda take konce duk ta duk'unk'une wuri d'aya gaba d'aya ta takura kanta ga kayan jikin ta duk ta konta dasu hatta hijabin kanta bata cireba ta nad'e guiwowin ta har suna tab'a k'irjin ta sai hannun ta data sa ta kame kafad'un ta sannan ta cusa kanta cikin pillow da kaga ganta kasan bacci takeyi amman cikin tsoro duk ta takure hatta numfashi ta da kalan tsoro take fidda sautin shi,
gyara zaman shi yayi yana fuskan tarta a hankali yasa hannu tare da kamo hijabin ya fara k'ok'arin zare mata shi a jikin ta,
ita kuwa cikin baccin tsoron da tunda tazo gidan a haka take rayuwa cikin tsoro dan ita bata tab'a kwana ita kad'ai a d'aki ba a rayuwar ta gata da tsoro amman kuma k'iyeyyar Hamma Umar d'in ta hanata kusantan inda yake ta gommace ta rayu cikin tsoro,
a hankali ta d'an motsa tare da k'ara jawo hijabin nata duk cikin bacci,
shi kuwa ganin ta d'an motsa ne yasa ya d'an janye hannunshi yayi shiru yana kallon fuskar ta,
can zuwa wani lokacin kuma ya d'an k'ara matsota sannan yasa hannun ya fara zaro hijabin har ya cire shi a kanta,
dai-dai sanda ya cire ita kuwa ta bud'e idonta,
gaba d'aya jikinta rawa yakeyi tamkar mazari sai wani irin zaro idanu tayi cikin tsoro ta mik'e tare da fizgewa tana tuttureshi,
shi kuwa Hamma Umar kamota yayi da k'arfi ya maidata kan gadon pillow ya jawo sannan ya kontar da ita kan pillow sai kuma yasa hannu a hankali ya fara zuge zip d'in rigarta,
ganin haka yasa ita kuwa tayi wani irin yunk'uri tare da sa hannu bibbiyu ta tureshi da k'arfi har saida kanshi ya bugi jikin gado da sauri ya dafe kanshi da hannun d'aya d'ayan kuma ya kamota ya rik'e gam,
cikin sanyi yace.
"Ina zaki je?
ki nitsu mana zakiji wa kanki ciwo fa zoki konta ba abinda zai sameki gani a kusa da ke."
hannu tasa tana ta kiciniyar b'amb'are yatsun hannu shi cikin tsiwa tace.
"Bana so ka sake min hannun na ka fita harkata ba ruwan ka da ni ka barni inje duk inda naga dama kar woni zo ka mak'ale ni kace zaka min dad'in baki ni bana sonka bana son ganin ka."
jawota yayi jikin shi cikin tsura mata ido yace.
"Bakya sona fa kikace khairi nifa d'an uwan kine."
"Eh bana sonka bana son ganin ka na tsanekaaa."
lips d'in shi na k'asa ya kamo ya rink'a tsotsa a hankali yana jin zafin kala manta ,
sai kuma ya k'ara matsota tare da zare rigar sannan yasa hannun yana kunce d'aurin da tayiwa zanin ta,
ita kuwa gaba d'aya sai wujijjigashi takeyi tana ta kici niyar kwace kanta amman ta kasa kawai sai ta sunkuyar da kanta tare da kafa bakinta a damtsen hannun shi ta datsa mishi cizo mai zafi dan gaba d'aya ta tsinke da Hamma Umar d'in,
yana jin yadda ta dasa hak'oran ta a damtsen hannun shi zafin yana ratsashi madadin ya saketa sai ya k'ara matsota jikin shi ido ya rumtse da k'arfi cikin wani irin yanayi yace.
"Zaki kasheni kike so? Ummu kiji tsoron Allah fa meyasa kika zab'i ki azabtar dani bayan kin san ni mijin kine."

Ita kam ganin bata da k'arfin kwatar kanta yasa ta saki kuka mai cike da tsoro murya a birkice tace.
"Ka sani wallahi ni bana sonka bana son ganin ka,
ka fita hanya ta."
Ido ya lumshe dan hak'ik'a yana jin ciwon yadda take cemai bata sonshi cikin sanyi yace.
" Khairi bakya sona ko ?"
"Ehh bana sonka."
Kai ya jinjina sannan yace .
"Kin dai san ni mijin kine ke kuma matata ce so kin san akwai hak'k'ina a kanki ko? kin kuwa san zaman aure mukeyi ni kuwa ba waliyi bane."
tureshi ta k'ara yi cikin kuka tana Jan hijabinta tana k'ok'arin rufe jikin ta murya na rawa tace.
"Ni bana sonka kuma ba zaman auren da zanyi dakai dan bazan karya al'k'awarin da nayiwa Mustapha ba ni ka sake ni."
ajiyan zuciya ya rink'a sauk'e wa cikin yanayin cushewar tunani ga yanayin canji daya tsinci kanshi a ciki shi da kanshi bai san yana da wannan halittar ba dan a zaton shi da zai iya rayuwa ko ba mace amman gaba d'aya tunda akayi auren yake jin bak'in al'amura a jikin shi,
saketa yayi cikin sanyi ya mik'e ya tsaya a bak'in gadon yana mai jin zafin kanshi data gwora da jikin gado da kuma cizon da tayi mishi,
hannun yasa ya kamo hannun ta a hankali yace.
"Ki dena kwana da bra a jikin ki yana haddasa ciwon k'irjin yana kuma iya jawo cancer ko ya sa miki toshewar numfashin,
ki dena kwana da kayan masu nauyi a jikin ki,
ki rink'a yin al'wala kafin ki kwanta ki kuma yi addu'ar bacci."
Baki ta tab'e cikin jin haushin sa tace.
"Nida jikina ba ruwan wani dani inyi yadda nike so kuma dole in kula da kaina tunda ina rayuwa da kai gida d'aya."
Murmushi yayi gano wai danshi take kwana a hakan,
hannun ta yaja har zuwa cikin bathroom a hankali yace.
"kiyi al'wala."
baki ta tura sannan tayi al'walar nan ma dan tasan hakan koyarwa ce ta annabi,
bayan tayi al'walan suna fitowa ta zauna bak'in gadon cikin tsiwa tace.
"Zanyi bacci fa."
Kai ya gyad'a sannan yasa hannu ya kontar da ita blanket ya jawo ya d'an rufeta ,
hannun shi na cikin blanket d'in ya sunkuye kanta a hankali yace.
"D'an d'ago bari in cire miki bra d'in."
harara tayi mishi k'asa-k'asa cikin tura baki tace.
"Ni ai ba karuwa bace."
sai ta kuma ture hannun shi sannan ta juyo ta konta ta a kife,
shi kuwa Addu'a yayi tare da shafe jikinta kamar yadda ya saba yiwa Usman ,
sannan ya kalleta ahankali ya juya ya fita,
a parlour ya konta tare da son jin d'umin ta Amman yasan hakan bazai samu ba,
haka ya kwana cikin halin takura.

Haka rayuwa taci gaba da juya musu duk wata kulawa da gata Hamma Umar yanayiwa khairn shi yayin da ita kuwa take ta azabtar dashi ,
ta yadda baya samun ko magana mai dad'i ma bare ya samu hakkin shi dake kanta duk da yana yawan zuwa inda take amman haka ba abinda yake sama mishi sai azaba da bak'in ciki ko tafin hannun ta bai isa ya murzaba sai yasha bak'ar magana.

Yau Monday kuma Yau kwanan su takwas da tarewa kenan,
yau tunda sassafe Hamma Umar ya shirya komai tsab kamar yadda yasaba sannan ya shiga wonka sauri sauri ya shirya dan yau zai fita zaije gidan governor dan duba lafiyar shi duk da dai bai gama hutun auren nashi ba amman zaije dan duba lafiyar shi ,
bayan ya gama shirin shi tsab sannan ya fesa turaren shi mai tarin k'amshi laptop nashi da phone dinshi ya d'auko sannan ya fito parlour kan dinning table ya ajiye su ,
sannan ya jawo cups guda biyu tea ya had'a ,
sannan ya d'an juya rik'e da cups d'in ya nufi cikin parlour gaban Ummul d'in ya d'an tsaya cikin sanyi yace.
"Khairi taso kisha tea sauri nake zan fita yanzu zan dawo."
kallon shi tayi sannan ta kalli yadda tea d'in yake ta tiriri da alamun ruwan yana da zafi sosai ido ta lumshe cikin jin dad'in shawarar da shaid'an ya kawo mata fuskar shi ta kuma kalla cikin mugunta ta mik'e ta tsaya a gaban shi,
hannu tasa ta karb'i cup d'in tare da tsura mishi ido,
shi kuwa kanshi ya sunkuyar tare da d'an juya tea spoon d'in dake cikin cup d'in,
itako murmushi mugunta tayi,
cup d'in ta d'ago tare da watsa mishi ruwan zafin a fuskarsa ,
ba zato ba tsammani yaji ta watsa mishi tea d'in a fuskar da jikin wani irin zafi da rad'a d'i yaji yana ratsashi,
jin zafin ruwan daya sauk'a a jikin shi yayi wani irin yunk'uri ya hankad'ata da k'arfi saida ta fad'i k'asa,
sai kuma cup d'in hannun shima ya sub'uce yayi k'asa,
hannun shi ya rink'a yarfawa yana d'an jujjuya kai yana jin zafin na ratsa fatarshi har cikin zuciyar shi yake jin zogin,
a take fuskar shi tayi jazir sai zufa keta keto mishi tako ina,
ita kuwa Ummul yana tureta tana fad'uwa ta kife kai tare da sakin kuka,
kuka ta saki da k'arfi shi kuwa jin kukan yayi sauri yayi kanta yana zuwa ya d'ago ta ya sa hannu biyu ya rik'e kafad'un ta ido ya zuba mata cikin wani irin yanayi ya lumshe ido murya a sanyaye yace.
"Kiyi hak'uri Ummulkhari bawai na tureki dan zafin ruwan da kika watsa min bane,
a a wallahi na tureki ne dan kar ruwan ya fantsalu ya dawo jikinki ya k'onaki ,
kiyi hak'uri."
Ido Ummul ta zuba mishi tare da k'ara sautin kukan nata tanayi tana mita,
a cikin zuciyar ta kuwa tabbas ta cika da mamaki har cikin ranta taji mamakin yanayin da Hamma Umar keyi mata magana a yanzu bayan k'onashi tayi sannan kuma shike bata hak'uri har kuma yana cewa ya tureta ne dan kar itama ta k'one,
kuma a zahiri da kaga fuskar shi kasan yana jin zafin k'unan amman bai bi ta kanshi ba ya tsaya bata hak'uri,
shi kuwa Hamma Umar har cikin ranshi bawai ya tureta dan ta watsa mishi ruwan zafin bane kuma yaji zafin yadda ya ture harta fad'i har takai da tana kuka,
a hankali ya kuma matsota yana kallon bakinta da take ta kuka da iya k'arfin ta ya lura so take ta tara mishi mak'otan su,
kuka take tana.
"Allah zai saka min ka rabani da kowa nawa kazo kana azabtar dani na tsane k...!"
Chapter 23 · 0% Book details