Sashe 13
Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Y*ayi mata wani irin kallo cikin tarin mamaki da jin zafi a ranshi murya can k'asa yace.
"Ummul duk wannan kukan kina yinshi ne dan an had'a auren ki da Hamma Umar?
Ummul duk wannan zafi da tarin bak'in ciki dan an shigar da Hamma na cikin rayuwar ki ne kike haka?."
Sai kuma yayi shiru tare da dafe k'ahon zuciyarshi a hankali cikin jin jiri ya koma baya kad'an ya zauna ido ya rumtse da k'arfi sannan ya jingina da jikin gini,
numfashi ya rink'a furzarwa da sauri-sauri yana mai cushewar tunani.
Ita kuwa Ummul cikin kuka tace.
"Na tsaneshi na tsani Hamma Umar bana sonshi duniya da lahira ko fuskar sa bana k'aunar gani,
Hamma Umar ba abinda yake jazamin a rayuwa sai bak'in ciki ya zame min bak'in jakada a rayuwa ta."
K'ara ta saki da k'arfi tare da dafe fuskar ta jin wani irin zazzafan mari da ya Sadik ya zuba mata cikin huci da zafin rai ya nunata da yatsa murya a hargitse yace.
"Ki kula kisan furucin da zakiyi ki san waye Hamma Umar wallahi a kanshi zamu iya miki komai,
shi Mustapha ko tare kuka fito duniya bake ba shi."
Kife kai Ummul tayi a bakin gado ta saki wani irin kuka mai cike da zafi a zuciya kuka mai cushe zuciya gaba d'aya jikin ta sai b'ari yake lokaci d'aya ciwon mararta da ciki da k'ugunta suka taso a tare,
kuka take cikin tausayawa kanta da Mustapha.
Gaba d'aya sukuwa shiru su kayi cikin jin sautin kukan ta, ya Usman ne yake tunani a ranshi
tabbas Ummul akwai kuna a ranta akwai zafi da ciwon rabuwa da masoyi,
sannan ga cushen mak'iyi da akayi mata,
har cikin ranshi yake tausayawa mata,
a sashin zuciyar shi kuwa,
yana jin zafi da bak'in ciki da takaici yadda Ummul ta tsani d'an uwanshi mafi soyuwa a gareshi.
Nenne kuwa itama shiru tayi tana jin sautin kukan y'ar tata har cikin ranta take tausayawa mata,
amman a zahiri tafi jin dad'in auren Ummul da Umar akan ace da Mustapha dan ita Nenne tana son Umar da Usman tamkar yayanta na cikinta bata son abinda zai b'atawa Usman rai da yanayin ciwon sa bata k'aunar taga damuwa a fuskar Umar dan shi jigone mai burin samawa kowa farin ciki shi baya shiga sabgar daba tasaba,
shi ba a gane matsalar sa dan ba fad'a zaiyi ba duk halin da yake ciki dan shi mutun ne mai kunya da zurfin ciki da kara da kawaici shiyasa bata son abinda zai cutar da Hamma Umar d'in,
haka yasa take ji a ranta dole zata iya juya d'iyarta tayi mishi biyeyya.
Ya Adam kuwa wata iriyar kunyace ta rufeshi ganin yadda a gaban Usman Ummul ke kuka kamar ranta zai fita dan an hada ta Aure da Hamma Umar,
kunya yake ji ya Ummul zata nuna bata son d'an uwan shi alhalin shi a koda yaushe cikin nuna mata kulawa da gata yake.
Ya Sadik har cikin ranshi yake jin tsanar Mustapha tunda a kan Mustapha ne Ummul take furta kalaman k'iyeyyar Hamma Umar d'in nasu haka kuma yake jin zai iya yiwa Ummul ko wanne hukuncin matuk'ar zatayi wa Hamma Umar d'in rashin da'a.
Auta Aliyu kuwa abokin fad'in Ummul kuma kaninta mai tausayawa mata ganin yadda take kuka ba wanda yake lallashin ta gashi dama ya Usman ne mai kareta kuma yau shima fad'an ya shafeshi,
kawai shima Aliyu sai hawaye yake zubda wa a hankali ya matso kusa da Ummul d'in murya na rawa yace.
"Ayyah Anty Ummul kiyi hak'uri kibar yin kukan haka."
Cikin tausayawa kanta da kanta ta fad'a jikin Aliyu kanta ta kife kan cinyar shi ta saki kuka mai cushewar sauti,
shima Aliyu sai hawaye car-car yana jin tausayin ta a ranshi,
cikin kuka tace.
"Aliyu yau kowa baya sona duk an tsanani sabida Hamma Umar ! sannan an rabani da Mustapha sabida Hamma Umar ! Auta kalli yau ya Usman ma fushi yake yi dani sabida Hamma Umar! kalli ya Adam da ya Sadik ji suke kamar su kashe ni sabida Hamma Umar! Abban mu da Nenne duk basa sona a yau sabida Hamma Umar!
Aliyu ba wanda ya tausayawa min sai kai."
sai kuma ta saki wani sabon kuka.
Ya Adam ne yayi kanta cikin nunata da yatsa murya a fad'ace yace.
"Kifa dena cika mana kunne da kuka wallahi in ba hakaba zan tattakaki."
Ya Sadik kuwa tsaki yaja cikin zuciya yace.
"Kiyi duk yadda kika ga dama ya rege naki tunda bakya ganin alkhairi zab'in da iyayen mu suka yi miki,
Mustapha ne dai bazamu bashi auren kiba."
Daga nan suka fice ita kuwa Nenne tsaki taja ta fice ta shiga kitchen ta kama aikin ta,
Aliyu kuwa tafin hannushi yasa yana gogewa Ummul d'in k'olloh dake bin fuskar ta,
shi kuwa ya Usman zama yayi kusa da Ummul d'in daketa murk'ususu tana ta cike lips d'in ta zufa na keto mata tako ina sai kukan da takeyi cikin raunin da wahala.
A hankali ya kalleta cikin sanyi ya d'an yi murmushi yace.
"Ummul khairi banyi fushi da keba ,
ki sani ke tawace kamar yadda Hamma Umar yake nawa ni Usman Ku duk nawa ne ba Wanda zank'i a cikin Ku kiyi hak'uri k'anwata kiyiwa kanki da Hamma na addu'a Allah ya muku zab'in abinda yafi zamewa alkhairi a gare Ku."
Kai kawai ta juya tana mai azabtuwa da ciwon cikin da tarin damuwa.
Shi kuwa Usman haka yayi ta bata baki ,
Amman ina Ummul bata ma san yana yiba,
ganin haka yasa. Usman ya fita kai tsaye parlour Hajjajo yaje,
cikin sanyi yayi mata maganar abinda ke faruwa,
kai ta d'an jinjina cikin k'arfin guiwa ta kalli Usman tace.
"Ku kanta na d'an wani lokacin ne zatayi ta bari ta saduda ta zauna da Umaru cikin aminci,
aini naji kukan nata zuwa ne bazan yiba,
dan inta ga ana damuwa da kukan nata dayin lallashin ta toh bazata bariba ku fita sha'anin ta."
Ido ya tsurawa Hajjajo cikin sanyi yace.
"Hajjajo indai Hamma Umar na son wannan had'in toh ina farin ciki da auren nan domain farin ciki B'iyayen na shine nawa."
Haka suka d'an tattauna kan zancen.
Itako Ummul tunda suka waste suka barta take kuka kamar zata had'iyi zuciya ta mutu,
Aliyu yayi ta lallashin ta amman ina dan abin ya had'e mata ga ciwon ga bak'in ciki,
haka Aliyu sai ya fito yaje kitchen ya dawo gunta yana ta sintiri ya kasa zama.
Haka har dere yayi Nenne kam ko ta kanta bata kuma biba dan inta tsaya kusa da ita tana jin tausayin d'iyar tata,
ta dai sa abinci Aliyu ya kawo mata,
ita kuwa Ummul yau abincin bazai ciwuba.
9:00 pm har yanzu Ummul tana kuka ne hannun ta dafe da mararta da k'ugunta akaro na biyu Aliyu ya shigo cikin tausayawa yace.
"Ummul naje na gayawa Nenne baki da lafiya Abba kuma yace kije gun Hamma Umar ya duba ki."
Kai ta kuma kifewa kan kago ta ci gaba da kukan da sautin shi baya fita dan muryar ta ta dashe,
Ya Adam ne dake zaune a parlour Nenne jin Abinda Aliyu ya fad'a yasa shi mik'e wa ya shigo bedroom d'in cikin tsuke fuska da bada umurni yace.
"Ke mike kije Hamma Umar d'in ya duba baki,
kin zauna kin wuni kuka shin kukan zai miki magani ne?
ki mik'e ko nace."
Cikin kuka dabin umurnin mahaifin nata da Yayan nata da tsoron ya Adam d'in ta mik'e cikin wahala hannun ta damk'e da mararta ta fice tana kuka,
kuma Ita da kanta ta san in Hamman ya mata Allurar tana jin sauk'i,
cikin kukan ta nufi part d'in su Hamma Umar d'in.
Shi kuwa Hamma Umar duk kukan da Ummul keyi yana ji dan lokacin da tafara kukan yana parlour Hajjajo jin kukan yayi yawane gashi yaji bala'in da su Adam ke mata yasa ya zame jikin shi ya dawo parlournsu cikin sanyi jiki ya konta kan kujera yasa tafin hannushi ya rufe fuskar sa,
zuciyar shi cike da tausayin Ummul ,
yana koncen yaji sautin kukanta a hankali yana ratsa parlour cikin rawan murya yaji tana sallama,
ido ya lumshe cikin jin zafin kukan da takeyi ga kunyar da ta rufeshi,
a hankali ya amsa mata sallamar,
Ita ko da zuwa yanzu ko tsawonta bata iya mik'ewa,
a sunkuye ta shigo parlour hawaye cike a fuskar ta da tayi jazir da kuka ida nunta duk sun kumbura,
a hankali ta durk'usa gaban kujerar da yake konce cikin kuka da rawan murya tace.
"Abba yace inzo kamin al..! alluran da kake min."
Shiru yayi zuciyar shi cike da tausayin ta gaba d'aya yake jin haushin kanshi tunda sana dinshi take irin wannan kukan.
Ita kuwa ganin bai kulatan ba ta saki kuka mai cike da raunin gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi,
jin yadda take kukan ne ya mik'e cikin sanyi bedroom ya shige yana zuwa ya had'a allurar, sannan ya dawo parlour yana zuwa gabanta ya k'afa guiwowin shi a k'asa kan carpet suna fuskan tar juna,
kanshi a sunkuye yasa hannushi ta bayan ta a hankali ya murza siket d'in atampa dake jikin ta,
ita kam Ummul ido ta rumtse da k'arfi zuciyar ta cike da tsanarsa a ranta,
fuskarta ya d'an kallah sannan ya zira bakin allurar a cikin jikin ta,
k'ara ta saki cikin kuka da zafi ta fad'a jikin shi.
Ido ya rumtse da k'arfi sannan yasa hannushi d'aya ya matso ta cikin sanyi da raunin murya yace.
"Kar kiyi inji miki ciwon ki nitsuba ba zafi."
kuka ta kuma fara cikin dashewar muryar,
shi kuwa idoya lumshe sannan ya k'ara saita allura a hankali ya rink'a cusa ruwan a jikin ta,
yanayi a hankali yana ce mata .
"Sorry."
Ita kuwa jin zafin yadda ruwan ke ratsata yasa ta ya matso shi ta rik'eshi gam,
yana gamawa ya zare allurar sannan a hankali ya tureta baya ya janye jikin shi,
ya mik'e kenan ya kalli Usman dake dafe da bak'in k'ofa ya zuba musu ido sai kallon suyake cikin wani irin yanayi.
Ita kuwa yana tureta ta mik'e cikin jin jiri ta ratsa gefen ya Usman d'in ta wuce.
"Ummul duk wannan kukan kina yinshi ne dan an had'a auren ki da Hamma Umar?
Ummul duk wannan zafi da tarin bak'in ciki dan an shigar da Hamma na cikin rayuwar ki ne kike haka?."
Sai kuma yayi shiru tare da dafe k'ahon zuciyarshi a hankali cikin jin jiri ya koma baya kad'an ya zauna ido ya rumtse da k'arfi sannan ya jingina da jikin gini,
numfashi ya rink'a furzarwa da sauri-sauri yana mai cushewar tunani.
Ita kuwa Ummul cikin kuka tace.
"Na tsaneshi na tsani Hamma Umar bana sonshi duniya da lahira ko fuskar sa bana k'aunar gani,
Hamma Umar ba abinda yake jazamin a rayuwa sai bak'in ciki ya zame min bak'in jakada a rayuwa ta."
K'ara ta saki da k'arfi tare da dafe fuskar ta jin wani irin zazzafan mari da ya Sadik ya zuba mata cikin huci da zafin rai ya nunata da yatsa murya a hargitse yace.
"Ki kula kisan furucin da zakiyi ki san waye Hamma Umar wallahi a kanshi zamu iya miki komai,
shi Mustapha ko tare kuka fito duniya bake ba shi."
Kife kai Ummul tayi a bakin gado ta saki wani irin kuka mai cike da zafi a zuciya kuka mai cushe zuciya gaba d'aya jikin ta sai b'ari yake lokaci d'aya ciwon mararta da ciki da k'ugunta suka taso a tare,
kuka take cikin tausayawa kanta da Mustapha.
Gaba d'aya sukuwa shiru su kayi cikin jin sautin kukan ta, ya Usman ne yake tunani a ranshi
tabbas Ummul akwai kuna a ranta akwai zafi da ciwon rabuwa da masoyi,
sannan ga cushen mak'iyi da akayi mata,
har cikin ranshi yake tausayawa mata,
a sashin zuciyar shi kuwa,
yana jin zafi da bak'in ciki da takaici yadda Ummul ta tsani d'an uwanshi mafi soyuwa a gareshi.
Nenne kuwa itama shiru tayi tana jin sautin kukan y'ar tata har cikin ranta take tausayawa mata,
amman a zahiri tafi jin dad'in auren Ummul da Umar akan ace da Mustapha dan ita Nenne tana son Umar da Usman tamkar yayanta na cikinta bata son abinda zai b'atawa Usman rai da yanayin ciwon sa bata k'aunar taga damuwa a fuskar Umar dan shi jigone mai burin samawa kowa farin ciki shi baya shiga sabgar daba tasaba,
shi ba a gane matsalar sa dan ba fad'a zaiyi ba duk halin da yake ciki dan shi mutun ne mai kunya da zurfin ciki da kara da kawaici shiyasa bata son abinda zai cutar da Hamma Umar d'in,
haka yasa take ji a ranta dole zata iya juya d'iyarta tayi mishi biyeyya.
Ya Adam kuwa wata iriyar kunyace ta rufeshi ganin yadda a gaban Usman Ummul ke kuka kamar ranta zai fita dan an hada ta Aure da Hamma Umar,
kunya yake ji ya Ummul zata nuna bata son d'an uwan shi alhalin shi a koda yaushe cikin nuna mata kulawa da gata yake.
Ya Sadik har cikin ranshi yake jin tsanar Mustapha tunda a kan Mustapha ne Ummul take furta kalaman k'iyeyyar Hamma Umar d'in nasu haka kuma yake jin zai iya yiwa Ummul ko wanne hukuncin matuk'ar zatayi wa Hamma Umar d'in rashin da'a.
Auta Aliyu kuwa abokin fad'in Ummul kuma kaninta mai tausayawa mata ganin yadda take kuka ba wanda yake lallashin ta gashi dama ya Usman ne mai kareta kuma yau shima fad'an ya shafeshi,
kawai shima Aliyu sai hawaye yake zubda wa a hankali ya matso kusa da Ummul d'in murya na rawa yace.
"Ayyah Anty Ummul kiyi hak'uri kibar yin kukan haka."
Cikin tausayawa kanta da kanta ta fad'a jikin Aliyu kanta ta kife kan cinyar shi ta saki kuka mai cushewar sauti,
shima Aliyu sai hawaye car-car yana jin tausayin ta a ranshi,
cikin kuka tace.
"Aliyu yau kowa baya sona duk an tsanani sabida Hamma Umar ! sannan an rabani da Mustapha sabida Hamma Umar ! Auta kalli yau ya Usman ma fushi yake yi dani sabida Hamma Umar! kalli ya Adam da ya Sadik ji suke kamar su kashe ni sabida Hamma Umar! Abban mu da Nenne duk basa sona a yau sabida Hamma Umar!
Aliyu ba wanda ya tausayawa min sai kai."
sai kuma ta saki wani sabon kuka.
Ya Adam ne yayi kanta cikin nunata da yatsa murya a fad'ace yace.
"Kifa dena cika mana kunne da kuka wallahi in ba hakaba zan tattakaki."
Ya Sadik kuwa tsaki yaja cikin zuciya yace.
"Kiyi duk yadda kika ga dama ya rege naki tunda bakya ganin alkhairi zab'in da iyayen mu suka yi miki,
Mustapha ne dai bazamu bashi auren kiba."
Daga nan suka fice ita kuwa Nenne tsaki taja ta fice ta shiga kitchen ta kama aikin ta,
Aliyu kuwa tafin hannushi yasa yana gogewa Ummul d'in k'olloh dake bin fuskar ta,
shi kuwa ya Usman zama yayi kusa da Ummul d'in daketa murk'ususu tana ta cike lips d'in ta zufa na keto mata tako ina sai kukan da takeyi cikin raunin da wahala.
A hankali ya kalleta cikin sanyi ya d'an yi murmushi yace.
"Ummul khairi banyi fushi da keba ,
ki sani ke tawace kamar yadda Hamma Umar yake nawa ni Usman Ku duk nawa ne ba Wanda zank'i a cikin Ku kiyi hak'uri k'anwata kiyiwa kanki da Hamma na addu'a Allah ya muku zab'in abinda yafi zamewa alkhairi a gare Ku."
Kai kawai ta juya tana mai azabtuwa da ciwon cikin da tarin damuwa.
Shi kuwa Usman haka yayi ta bata baki ,
Amman ina Ummul bata ma san yana yiba,
ganin haka yasa. Usman ya fita kai tsaye parlour Hajjajo yaje,
cikin sanyi yayi mata maganar abinda ke faruwa,
kai ta d'an jinjina cikin k'arfin guiwa ta kalli Usman tace.
"Ku kanta na d'an wani lokacin ne zatayi ta bari ta saduda ta zauna da Umaru cikin aminci,
aini naji kukan nata zuwa ne bazan yiba,
dan inta ga ana damuwa da kukan nata dayin lallashin ta toh bazata bariba ku fita sha'anin ta."
Ido ya tsurawa Hajjajo cikin sanyi yace.
"Hajjajo indai Hamma Umar na son wannan had'in toh ina farin ciki da auren nan domain farin ciki B'iyayen na shine nawa."
Haka suka d'an tattauna kan zancen.
Itako Ummul tunda suka waste suka barta take kuka kamar zata had'iyi zuciya ta mutu,
Aliyu yayi ta lallashin ta amman ina dan abin ya had'e mata ga ciwon ga bak'in ciki,
haka Aliyu sai ya fito yaje kitchen ya dawo gunta yana ta sintiri ya kasa zama.
Haka har dere yayi Nenne kam ko ta kanta bata kuma biba dan inta tsaya kusa da ita tana jin tausayin d'iyar tata,
ta dai sa abinci Aliyu ya kawo mata,
ita kuwa Ummul yau abincin bazai ciwuba.
9:00 pm har yanzu Ummul tana kuka ne hannun ta dafe da mararta da k'ugunta akaro na biyu Aliyu ya shigo cikin tausayawa yace.
"Ummul naje na gayawa Nenne baki da lafiya Abba kuma yace kije gun Hamma Umar ya duba ki."
Kai ta kuma kifewa kan kago ta ci gaba da kukan da sautin shi baya fita dan muryar ta ta dashe,
Ya Adam ne dake zaune a parlour Nenne jin Abinda Aliyu ya fad'a yasa shi mik'e wa ya shigo bedroom d'in cikin tsuke fuska da bada umurni yace.
"Ke mike kije Hamma Umar d'in ya duba baki,
kin zauna kin wuni kuka shin kukan zai miki magani ne?
ki mik'e ko nace."
Cikin kuka dabin umurnin mahaifin nata da Yayan nata da tsoron ya Adam d'in ta mik'e cikin wahala hannun ta damk'e da mararta ta fice tana kuka,
kuma Ita da kanta ta san in Hamman ya mata Allurar tana jin sauk'i,
cikin kukan ta nufi part d'in su Hamma Umar d'in.
Shi kuwa Hamma Umar duk kukan da Ummul keyi yana ji dan lokacin da tafara kukan yana parlour Hajjajo jin kukan yayi yawane gashi yaji bala'in da su Adam ke mata yasa ya zame jikin shi ya dawo parlournsu cikin sanyi jiki ya konta kan kujera yasa tafin hannushi ya rufe fuskar sa,
zuciyar shi cike da tausayin Ummul ,
yana koncen yaji sautin kukanta a hankali yana ratsa parlour cikin rawan murya yaji tana sallama,
ido ya lumshe cikin jin zafin kukan da takeyi ga kunyar da ta rufeshi,
a hankali ya amsa mata sallamar,
Ita ko da zuwa yanzu ko tsawonta bata iya mik'ewa,
a sunkuye ta shigo parlour hawaye cike a fuskar ta da tayi jazir da kuka ida nunta duk sun kumbura,
a hankali ta durk'usa gaban kujerar da yake konce cikin kuka da rawan murya tace.
"Abba yace inzo kamin al..! alluran da kake min."
Shiru yayi zuciyar shi cike da tausayin ta gaba d'aya yake jin haushin kanshi tunda sana dinshi take irin wannan kukan.
Ita kuwa ganin bai kulatan ba ta saki kuka mai cike da raunin gaba d'aya jikin ta rawa yakeyi,
jin yadda take kukan ne ya mik'e cikin sanyi bedroom ya shige yana zuwa ya had'a allurar, sannan ya dawo parlour yana zuwa gabanta ya k'afa guiwowin shi a k'asa kan carpet suna fuskan tar juna,
kanshi a sunkuye yasa hannushi ta bayan ta a hankali ya murza siket d'in atampa dake jikin ta,
ita kam Ummul ido ta rumtse da k'arfi zuciyar ta cike da tsanarsa a ranta,
fuskarta ya d'an kallah sannan ya zira bakin allurar a cikin jikin ta,
k'ara ta saki cikin kuka da zafi ta fad'a jikin shi.
Ido ya rumtse da k'arfi sannan yasa hannushi d'aya ya matso ta cikin sanyi da raunin murya yace.
"Kar kiyi inji miki ciwon ki nitsuba ba zafi."
kuka ta kuma fara cikin dashewar muryar,
shi kuwa idoya lumshe sannan ya k'ara saita allura a hankali ya rink'a cusa ruwan a jikin ta,
yanayi a hankali yana ce mata .
"Sorry."
Ita kuwa jin zafin yadda ruwan ke ratsata yasa ta ya matso shi ta rik'eshi gam,
yana gamawa ya zare allurar sannan a hankali ya tureta baya ya janye jikin shi,
ya mik'e kenan ya kalli Usman dake dafe da bak'in k'ofa ya zuba musu ido sai kallon suyake cikin wani irin yanayi.
Ita kuwa yana tureta ta mik'e cikin jin jiri ta ratsa gefen ya Usman d'in ta wuce.