← Book details Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 77

Sashe 22

Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan Hamma Umar d'in ya dawo masallaci ne ya zauna a parlour tare da kunna TV ya kama tashar manara idan ya samu sun saka sautin karatu k'ura'ani tare da muryar Ahmad Sulaiman volume ya k'ara ta yadda sautin ya rink'a ratsa cikin gidan baki d'aya kan kujera ya konta ya lumshe ido yana bin sautin karatu hannun shi kuma rik'e da carbi,
itako Ummul tunda tayi salla ta konta kan sallayar cikin jin zazzab'i ga ciwon kai kuma ta k'asa barin kukan,
a haka tana kukan har bacci ya saceta,
shi kuwa bai bar parlour ba sai 9:00 am ya mik'e ya shige kitchen nasu gas ya kunna tare da d'an tafa musu ruwan tea sannan ya sake d'uma kajin daya seyo ajiyan ya had'a musu komai yazo ya ajiye kan dinning d'in ,
d'akin shi ya shige wonka yayi sannan ya shirya cikin kananan kayan ya fito ras sai k'amshi yake zubawa,
kai tsaye k'ofar d'akin ta yazo ya tsaya cikin sanyi yace.
"Khairi ! Khairi ! tashi kizo kiyi breakfast."
tana jinshi tayi shiru kamar bata jinshi ,
sai mik'e wa tayi ta zauna ta jingina jikin gado tana jin yadda yake kiranta tayi cib kamar bata d'akin,
shi kuwa sai komawa yayi ta jikin window ta ya bud'e glass d'in sannan yasa hannun ya bud'e labulen ido ya zuba bata,
itama idon ta zuba mishi cikin nuna kiyayyarsa a fili,
kai ya jinjina cikin jin tausayin ta yace.
"Khairi taso kizo kinji ko."
"Bazan zoba bazan cin abince ba,
Na mutuwa mane me ruwan ka?."
Kai ya juya tare da cewa.
"Meyasa bazaki ciba."
a kufule tace .
"Sabida na tsane kaa! bana son ka! bana son ganin ka! bana son ko jin muryar ka!."
ido ya zuba mata cikin tsananin mamaki da al'ajabi bai tab'a zaton k'iyayyar da Ummul take Mashi yakai matsayin da zata kalleshi ido da ido tace mishi bata sonshi bata k'aunar shiba,
muryar tace ta kuma katsemai tunani tana cewa .
"Na tsane ka tunda ko yaushe a sana dinka nake azabtuwa."
Kallon ta ya kumayi sannan a hankali yace.
"Kina son kanki ai?."
"Sosai ma dama ina son kaina kam mana."
murmushi ya d'an yi sannan yace.
"Toh ki fito kici abinci dan ki kula da kanki ni kuma nagode da k'iyayyarki gareni."

"Bazan ciba ! ba kuma zan fito ba!."

Haka Hamma Umar yake ta fama da Ummul Amman sam tak'i fitowa ,
zuwa yanzu kuwa kukan har ya gaji da ita dan ba itace ta gaji da kukan ba kukanne ya gaji da ita sai dai tayi ta diri ba hawaye shi kuwa duk kula da tattali yana had'a mata Amman ko fitowa tak'i tayi bataci komai sai ruwan da take sha da fari bata jin yuwar Amman zuwa yau da tayi kwana biyu a hakan sai take jin yunwar kamar zata kasheta inta tsaya sai jiri ,
tayi wonka kuwa yafi sau 3 wai duk ko zataji k'arfi Amman abin yaci tura a deren kwana na 3 ne ta k'asa bacci dan yunwar dake kwak'ularta.

Shi kuwa Hamma Umar gaba d'aya kewar d'an uwanshi ya cika mar jiki da zuciya haka yasa kullum sai sunyi magana a woya a kalla sau 5 zuwa sau 6 duk lokacin shan maganin Usman in yayi sai Umar ya kirashi yace mishi kasha maganin a b'aggaren Ummul kuwa yana damuwa da halin da take ciki.

A al'adun shuwa'arab d'in kuwa suna yin wata al'adarsu duk lokacin da akayi Aure aka kai Amariya gidan ta washe gari y'an uwanta zasuje karb'ar tukuici a gun aggo kuma Wannan tukuici ba'a badashi sai aggo ya kusanci matarshi so haka yasa wasu basa zuwa washe garin randa aka kai Amariya sukan bari sai randa tayi kwana 3 ko 7 kuma Wannan tukuici ba'a ba dashi ga amariyar da bata kai budurcin ta gidan mijin taba,
so Hamma Umar kuwa yasan da wannan al'dartasu,
so yau ya tashi da wuri ya kimtsa ko ina na gidan dan yana tsammanin y'an uwan Ummul zasu zo yau d'in tunda yau kwanan ta uku da zuwa gidan,
bayan ya gama komai yayi wonkan shi fes ya fito ya shirya cikin
wagamri mai kalar sararin samaniya ya fito ras sai k'amshi yakeyi.

kamar kullum yazo bak'in k'ofar d'akin nata cikin sanyi yace.
"Khairi ki zo ki bud'e k'ofar nan zakiyi bak'i su Anty Shuwa na zuwa."
A hankali cikin wahala da jiri ta mik'e tazo bak'in k'ofar ta bud'e sai kuma ta juya ta koma ta zauna gefen gado tana ta haki hannun ta rik'e da cikin ta,
shi kuwa Hamma Umar yana ganin haka ya koma parlour dinning area ya nufa yana zuwa,
ya d'auki cup tea ya had'a mata mai kauri sannan ya juyo ya dawo cikin d'akin yana shiga kiran Usman na shiga woyar shi gefen ta yaje ya zauna sannan ya mik'a mata cup d'in cikin kula yace.
"Karb'i kisha tea zakiji k'arfi."
kai ta juya tare da matse ido ta samu ta zubda k'ollah,
shi kuwa woyarshi ya zaro ya amsa kiran yana kallon fuskar ta,
gaisawa sukayi da Usman sannan yace .
"Kashe maganin ko?."
"Eh nasha tun d'azun ma."
sai kuma yayi shiru... can kuma yace .
"Hamma Umar Ummul fa?."
"Gata nan tana ta kuka tak'i cin komai kuma bata da lafiya ,
gata bari in bata woyar."
"Toh" yace sannan yayi shiru yana jin Hamma Umar d'in yana cewa.
"Ga Usman yana magana."
Karb'ar woyar tayi cikin rawan jiki murya na rawa tace.
"Hello ya Usman."
A hankali cikin sanyi yace.
"Na'ammmm Ummul."
Tana jin muryar shi sai kuma ta fashe da kuka cikin kukan tace.
"Ya Usman cikina ciwo , kaina ciwo jiri nake ji duhu nake gani ya Usman ni dai zan dawo gida."
sai kuwa ta fashe da kuka.
shi kuwa Hamma Umar shiru yayi ya zuba mata ido yana sauraron magarda takeyi,
shi kuwa Usman a hankali yace.
"Ummul kinfi son zuciyata ta fashe ko? Ummul bazaki bar kukan nan ba ko? Ummul kina son inyi fushi da ke ko?."
Kai ta rink'a juyawa kamar tana gaban shi sai kuma tasa tafin hannu ta share hawayen ta murya a sanyaye tace.
"Ah ah ya Usman bana so kayi hak'uri nayi shiru."
Ajiyar zuciya ya sauk'e sannan yace.
"Ban yarda ba nasan yanzu haka idanun ki na zubda hawaye kuma ba zakici abinci ba."
da sauri tace.
"Wallahi nayi shiru kuma na share hawayen kuma wallahi zanci abincin."

"Kin tabbata ?."

"Ehh wallahi."

"Na tabbayi Hamma Umar?."

"Ehh gashi ka tabbaye shi."

Sai kuma ta mik'awa Hamma Umar d'in woyar tana cewa.
"Bani zansha shayin."
Mik'a mata cup d'in yayi sannan ya karb'i woyar tashi,
yana kallon fuskar ta,
shi kuwa Usman dariya ya d'an yi cikin sanyi yace.
"Hamma na tayi shiru ko? ta karb'i tea d'in ? ta fara sha ne?"

Murmushi yayi tare da cewa.
"Ehh ."
Dariya Usman ya kumayi sannan yace.
"Hamma na kai baka saba lallashin wani d'an adam bayan ni a duniya ba shiyasa ka k'asa sata tayi shiru Hamma dole ka koyi lallashi fa tunda Allah ya had'a ka da Ummul."

murmushi kawai yayi sannan yace.
"Toh."

Bayan ya katse kiran ne ya juyo ya kalli Ummul da tuni ta shanye tea d'in sai zufa keta tsatstsafo mata tako ina sai damk'e cikin tayi tana murk'ususuwa,
mik'ewa yayi ya tsaida ta sannan ya rink'a jijjigata har saida yaji tayi gyatsa sannan ya meda ita kan gadon ya kontar da ita,
d'akin shi yaje jim kad'an ya dawo hannun shi rik'e da magani ,
shida kanshi ya bata tasha sannan ta koma ta konta,
shi kuwa rafan kud'i ya ajiye mata a gefen ta wanda zasu kai dubu 100 sai kuma wata y'ar counter near yar k'arama sarkace da y'an kunne sai zobe,
zoben ya zaro sannan ya kamo hannun ta ya zura zoben a yatsarta dake kusa da y'ar karamar yatsar ta sannan yace.
"Gashi insu Anty Shuwa sunzo ki basu wannan kud'in da sark'ar."
Harara tayi mishi k'asa-k'asa sannan ta zare zoben ta jefar gefe,
shi kuwa parlour ya koma ya zauna,
ya zauna kenan su Anty Shuwa suka iso bayan sun gaisa ne sai ya fita shida ya SADIK daya kawo su.

Su Anty Shuwa kam tunda suka samu Ummul a konce ba lafiya sai sukayi zaton ta zama cikekkiyar matar aure,
yayin da Usman ma tunda Hamma Umar yace mai Ummul bata da lafiya kuma tana ta kuka sai ya d'auka Hamman nashi ya zama oggone a daren jiyan,
so haka suma su Anty Shuwa amman Anty Halima ita ta gane sarai ba abinda Hamma Umar yayiwa Ummul kawai ya bada tukuicin ne.
haka suka wuni suka yi tayiwa Ummul nasiha ta kuma ci abinci so ta samu tayi k'arfi,
sai yamma lis suka tafi.

bayan sun tafi kuma ta wore ras ta fito parlour dan a cewarta yanzu lokaci yayi da zata fara gasa Hamma Umar d'in.

Da dere yayi Hamma Umar yana d'akin shi bayan ya yayi wonka ya fito yayi shirin bacci har ya konta sai kuma ya mik'e ya nufi d'akin ta yana zuwa ya zauna gefen ta a hankali ya....

*Dedde na Allah ya baki lafiya*

By
*GARKUWAR FUlANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*RUBUTACCEN AL,AMARI*

Page 1⃣5⃣

*NA*
*AYSHA ALI GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*Alhamhadullih jikin Dedde na da sauk'i sosai ta samu lafiya nagode wa Allah daya bata lafiya kuma nagode muku masu kirana da masu turo min messages da yi mata addu'a a groups da masu bina pc, UWA uba wad'an da sukayi tattaki suka zo dubiya duk nagode da addu'oinku gareta ngd matuka Allah bar zumunci 🤝😘😍🤝*
Chapter 22 · 0% Book details