Sashe 62
Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
K'arfe 9:30 na dare Ummul tana kwance ganin zata fara aikin ta na tunani da kuka da take duk darene yasa ta janyo wayar ta kunna sannan ta lalubo number ya Usman ta danna kira aiko bugu d'aya ya d'auka daman yanada niyyar kiranta sallama yayi ta amsamai sannan shiru ya biyo baya,
a hankali ta katse shirun da cewa,
"ya Usman nagode". wata irin ajiyar zuciya ya sauke,
tare da lumshe ido a hankali yace,
"Nima nagode da kika amshi keutata,
Ummu ina sonki ina son auren ki kiyi hak'uri ki yarda da k'addararki ta sirens dan inba mutuwa ba ba abinda zaisa ni Usman k'anin Umar nace zan aureki da haka shima wannan ki sanyashi a cikin littafin k'addarar rayuwarmu Ummu na ina sonki ki shigo rayuwata ki zame min gurbin Hamma na nima na zame miki gurbin sa,
Ummu wallahi da gaske ina murad'in yin aure na gaji da zaman kad'aici ina son samun me d'ebemin kewa da kawarmin da buk'atuna ko zan samu sukuni a rayuwa ta Ummu ina da buk'atar ki kusa dani". saurin cire wayar tayi daga kunnenta ta katse kiran,
tana jin zuciyarta na bugawa da k'arfi salon maganganun Ya Usman d'in nata suna bata tsoro dan a hankali ta fara fahimtar yana yin irin tasa halittar Kuma,
Kamar zata ajiye wayar sai kuma ta bud'e data,
aiko sak'onni sukayi ta shigowa saida ta bud'e na sauran groups d'in sannan ta dawo kan wanda taga sakon shi sunfi yawa mai suna 'COOL NOVELS ' na Hayatu Baba Zubairu, ta bude magan ganu tarink'a gani anayi a group din daga dukkan alamu a kan novel suke tattaunawa,
wata tace daga cikin members na group d'in tace,
"Gaskiya Meenal ta Hamma Haiydar ce". wasu suce,
"A barwa Dr jabeer".
wasu suce General Aliyu ai shine jarumin amman kuma Allah yasa kar Abdul yaci nasarar ketawa Meenal haddi". Saida tayi ta dubawa sannan taga suna maganane akan wani novel dataga antura page d'aya mai suna, *'BANDIRAWO'* na marubuciya nan *AYSHA ALIYU GARKUWA,* fita tayi tayiwa Aunty Halima magana data tura mata novel d'in saboda ta faro daga farko,
aiko nan da nan ta turo mata, saida takai k'arfe 1:50 tana karantawa har ta iso inda aka tsaya sannan ta tashi tayo alwala tayi nafiloli day'an addu o i sannan ta kwanta.
Tunda ta karanta littafin *Bandirawo* tafara tunani da kuma son taga itama labarin rayuwarta yazama littafin da jama a da dama zasu karanta kuma su ilmantu da sanin illolin rashi biyayya ga iyaye da rashin karb'ar k'addara sannan da sanin muhimmancin mutum mai hakuri da illar cutar da masoyi sannan jama a da dama zasuji labarin d'an kad'an daga cikin illar da boko haram sukayi ga zuciyoyin al'umar dake arewa maso gabashin Nigeria tana son yan mata su d'auki darasi a rayuwar ta tunda ita kam ta rigada tayi kuskure da nadamar yin tirjiya ga zab'in iyayenta amman tana son labarin ta ya zama izina ga yan mata da su guji yiwa iyayen su tirjiya dan nadama zata biyo baya tana son taga irin muhawarar da mutane zasuyi a kanta da abin da ta aikatawa Hamma Umar tana son taga an fad'i laifinta ko zata k'ara dauwama cikin dana sani da yiwa Hamman ta addu'a.
Aliyu tafara bawa shawara sannan sukaiwa Ya Sadiq da Adam shawarar hakan shima ya gamsu amma yace mata ta sanar da ya Usman kafin ta ai watar da komai dan shine babba kuma shi zai bada shawara mafi dacewa dan haka tai niyyar sanar dashi buk'atar ta.
Ranar asabar misalin k'arfe sha d'aya na rana Ummul tayi wanka tad'au doguwar rigarta ta saka tai rolling kanta da mayafin rigar ta feshe jikinta da turare mai kamshi sannan ta zauna bakin gado ta d'auki wayar ta a hankali tai dialing number Ya Usman sannan ta kara a kunnen ta,
Usman dake zaune gaban laptop yana d'an danne danne ya d'aga wayar yasa ki murmushi mai sauti dayasa Adam dake latsa wayar shi juyowa yana kallon shi, ciki jin dadi ya amsa kiran ya karata a kunne yayi k'asa da murya yace,
"Assalamu alaiki ya noorul hayati na". Ummul ta amsa da, "Wa alaikassalam, ya Usman ka fitane?". saida ya sake kashe murya yace,
"waneni infita banyi sallama da ruhina ba,
inzone?".
Dasauri tace,
"a a ina zuwa".
bata jira amsar shiba ta katse wayar ta tashi ta fito.
Juya kai Usman yayi ya harari Adam cikin wasa yace,
"meye ka zuban ido, kake wata dariya kamar mara gaskiya".
k'asa da kai Adam yayi yana danne dariyar dake shirin fitowa da k'arfi yace,
"ni menace?".
tsuke fuska yayi yace, "Daman me ka isa kace,
fita zaka yi daga d'akin Ummuna zatazo".
Adam baisan lokacin da dariyar ta kwace mashi ta fitoba,
shiko Usman yunk'ura wa yayi ya kawomai dukan wasa Adam ya kauce yace,
"kuda zakuyi maganar ku a palour ina ruwana ina nan".
Kai ya kad'a yace,
"Allah saika fita d'an sa ido kawai".
Wayarshi ya d'auka yasauko daga gadon yana dariya yace, "intai tsami naji".
"inba tagi tsaminba kuma kai sai kayi tsamin ko".
Adam yana fita yasami Ummul bakin k'ofa tana sallama ya amsa cikin kauda kai sannan suka gaisa ya wuce yanufi b'angaren Nanne.
a hankali ta katse shirun da cewa,
"ya Usman nagode". wata irin ajiyar zuciya ya sauke,
tare da lumshe ido a hankali yace,
"Nima nagode da kika amshi keutata,
Ummu ina sonki ina son auren ki kiyi hak'uri ki yarda da k'addararki ta sirens dan inba mutuwa ba ba abinda zaisa ni Usman k'anin Umar nace zan aureki da haka shima wannan ki sanyashi a cikin littafin k'addarar rayuwarmu Ummu na ina sonki ki shigo rayuwata ki zame min gurbin Hamma na nima na zame miki gurbin sa,
Ummu wallahi da gaske ina murad'in yin aure na gaji da zaman kad'aici ina son samun me d'ebemin kewa da kawarmin da buk'atuna ko zan samu sukuni a rayuwa ta Ummu ina da buk'atar ki kusa dani". saurin cire wayar tayi daga kunnenta ta katse kiran,
tana jin zuciyarta na bugawa da k'arfi salon maganganun Ya Usman d'in nata suna bata tsoro dan a hankali ta fara fahimtar yana yin irin tasa halittar Kuma,
Kamar zata ajiye wayar sai kuma ta bud'e data,
aiko sak'onni sukayi ta shigowa saida ta bud'e na sauran groups d'in sannan ta dawo kan wanda taga sakon shi sunfi yawa mai suna 'COOL NOVELS ' na Hayatu Baba Zubairu, ta bude magan ganu tarink'a gani anayi a group din daga dukkan alamu a kan novel suke tattaunawa,
wata tace daga cikin members na group d'in tace,
"Gaskiya Meenal ta Hamma Haiydar ce". wasu suce,
"A barwa Dr jabeer".
wasu suce General Aliyu ai shine jarumin amman kuma Allah yasa kar Abdul yaci nasarar ketawa Meenal haddi". Saida tayi ta dubawa sannan taga suna maganane akan wani novel dataga antura page d'aya mai suna, *'BANDIRAWO'* na marubuciya nan *AYSHA ALIYU GARKUWA,* fita tayi tayiwa Aunty Halima magana data tura mata novel d'in saboda ta faro daga farko,
aiko nan da nan ta turo mata, saida takai k'arfe 1:50 tana karantawa har ta iso inda aka tsaya sannan ta tashi tayo alwala tayi nafiloli day'an addu o i sannan ta kwanta.
Tunda ta karanta littafin *Bandirawo* tafara tunani da kuma son taga itama labarin rayuwarta yazama littafin da jama a da dama zasu karanta kuma su ilmantu da sanin illolin rashi biyayya ga iyaye da rashin karb'ar k'addara sannan da sanin muhimmancin mutum mai hakuri da illar cutar da masoyi sannan jama a da dama zasuji labarin d'an kad'an daga cikin illar da boko haram sukayi ga zuciyoyin al'umar dake arewa maso gabashin Nigeria tana son yan mata su d'auki darasi a rayuwar ta tunda ita kam ta rigada tayi kuskure da nadamar yin tirjiya ga zab'in iyayenta amman tana son labarin ta ya zama izina ga yan mata da su guji yiwa iyayen su tirjiya dan nadama zata biyo baya tana son taga irin muhawarar da mutane zasuyi a kanta da abin da ta aikatawa Hamma Umar tana son taga an fad'i laifinta ko zata k'ara dauwama cikin dana sani da yiwa Hamman ta addu'a.
Aliyu tafara bawa shawara sannan sukaiwa Ya Sadiq da Adam shawarar hakan shima ya gamsu amma yace mata ta sanar da ya Usman kafin ta ai watar da komai dan shine babba kuma shi zai bada shawara mafi dacewa dan haka tai niyyar sanar dashi buk'atar ta.
Ranar asabar misalin k'arfe sha d'aya na rana Ummul tayi wanka tad'au doguwar rigarta ta saka tai rolling kanta da mayafin rigar ta feshe jikinta da turare mai kamshi sannan ta zauna bakin gado ta d'auki wayar ta a hankali tai dialing number Ya Usman sannan ta kara a kunnen ta,
Usman dake zaune gaban laptop yana d'an danne danne ya d'aga wayar yasa ki murmushi mai sauti dayasa Adam dake latsa wayar shi juyowa yana kallon shi, ciki jin dadi ya amsa kiran ya karata a kunne yayi k'asa da murya yace,
"Assalamu alaiki ya noorul hayati na". Ummul ta amsa da, "Wa alaikassalam, ya Usman ka fitane?". saida ya sake kashe murya yace,
"waneni infita banyi sallama da ruhina ba,
inzone?".
Dasauri tace,
"a a ina zuwa".
bata jira amsar shiba ta katse wayar ta tashi ta fito.
Juya kai Usman yayi ya harari Adam cikin wasa yace,
"meye ka zuban ido, kake wata dariya kamar mara gaskiya".
k'asa da kai Adam yayi yana danne dariyar dake shirin fitowa da k'arfi yace,
"ni menace?".
tsuke fuska yayi yace, "Daman me ka isa kace,
fita zaka yi daga d'akin Ummuna zatazo".
Adam baisan lokacin da dariyar ta kwace mashi ta fitoba,
shiko Usman yunk'ura wa yayi ya kawomai dukan wasa Adam ya kauce yace,
"kuda zakuyi maganar ku a palour ina ruwana ina nan".
Kai ya kad'a yace,
"Allah saika fita d'an sa ido kawai".
Wayarshi ya d'auka yasauko daga gadon yana dariya yace, "intai tsami naji".
"inba tagi tsaminba kuma kai sai kayi tsamin ko".
Adam yana fita yasami Ummul bakin k'ofa tana sallama ya amsa cikin kauda kai sannan suka gaisa ya wuce yanufi b'angaren Nanne.