← Book details Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 77

Sashe 50

Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

A gida kuwa Usman ne ya kalli Adam dake gefen shi cikin sanyi yace,
"Adam zan tafi damaturu zanje naga Hamma na tun shekaran jiya bamuga junaba yanzu zan tafi".
cikin sanyi Adam yace,
"Ni dai bazani ba sai Hamma ya huce ".
haka yayi shirin tsab ya fito ya sallami su Nenne da Hajjajo sannan ya fito ya bud'e motarshi ya shiga.

Ita Kuwa Ummul Hamma Umar na fita wani irin zazzab'i mai zafi ya rufeta a take taji wani irin yunk'u ri... ..

*By*
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*RUBUTACCEN AL,AMARI*

Page 2⃣9⃣

*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*JAMU NA HOLARE BALD'E*

*Y*unk'uri tayi cikin gala baita dan aman da takeyi tun bayan fitan Hamma Umar d'in nata amai d'in take tayi har jikin ta na rawa gaba d'aya ta gala baita intayi yunk'uri sai taji zuciyarya taja ta tsinke ras gaban ta na fad'uwa,
a wahalce ta tashi cikin layi da rawan sanyin zazzab'in dake bibiyarta tattare wurin da tayi amai d'in tayi ta goge filin sannan ta kashe A/C dan sanyin da taji ya rufe ta sannan ta sassake labulayen windows nata har ta konta ta kuma mik'ewa da kyar taje ta rufe k'ofar bedroom nata d'in sannan ta dawo ta konta ta gudundune cikin blanket tana jin yadda d'an cikin ta ya tattare ya dawo k'asan k'ahon zucuyarta,
yayi cus ya dena motsi,
itako lokaci d'aya wani irin fargaba da razani da tsoro mai tsanani ya rufeta haka kawai taji jikinta kamar an rufamata d'anyen fata duk zuciyarta ta raunata a hakan cikin kad'uwa da ciwon wani irin bacci ya saceta.

Shiko Hamma Umar da yake Federal Medical center duk da dama ba kullum yake zuwaba sai akwai imergency dan shi aikin shi duba govnr ne,
so yauma imergency ne ya kawoshi,
aiki sukayi cikin sauk'i shida abakin shi Dr Bashir Ibrahim,
k'arfe takwas da mintu hamsin da biyu suka fito kai tsaye office nasu suka nufa dan office en a jere suke,
suna tafiya Dr Ibrahim na bin bayan Dr Umar Ibrahim Umar d'in da ido ganin gaba d'aya yau komai yake jikin shi a mace duk motsin da zaiyi sai yace,
"Sauri nake zan Koma gidana Ummul bata da Lafiya,
kuma inaso muje gida nayi kewar Usman".
murmushi Dr Bashir yayi cikin sanyi yace,
"Dr Umar anya ko kana son kanka kamar yadda kake son Usman da Ammin ku da Ummul? ".
kai ya gyad'a mai a hankali yace,
"ina jin tausayin su ne".
a dai-dai tsakiyar farfajiyar asibitin suka tsaya sukayi shiru suna kallon juna cikin kasa kunnuwa yayin da gaba d'aya illajirin mutanen dake wurin sukayi cirko-cirko suna baza ido da kasa kunne.

Ta kasance yau Monday 27 February 2014 ranar da mutanen garin damaturu bazasu tab'a mantashi a kund'in tarihin rayuwar su da garin ba musamman zuriyar Alhaji Umar Shina
k'arfe tara dai-dai na safiyar wannan rana *BOKO HARAM* sukayiwa garin Damaturun diran mikiya inda sukayiwa garin zobe wanda forkon shigarsu ta layin uguwarsu Hamma Umar suka shigo wato gidan Ummul kenan dake nyanya line dake gujba road damaturu,
yayin da suna shiga suka rink'a sake bomb da harbe-harbe duk wanda suka kama suyi mishi kisan gillah,
lokaci d'aya garin damaturu ya hargitse ya birkice sai gudu akeyi ana neman tsiratar da rai,
😭😭😭suko tsinannun Allah ta ala sai bi suke gida diga suna kashe Al'Ummar Annabi sannan sun datse hanyoyin shiga garin duk motor da tazo su tsare su kashe a bakin mashigar garin,
a haka har suka kusan to gidan Hamma Umar.
Chapter 50 · 0% Book details