← Book details Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 77

Sashe 55

Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Bayan awanni shida Ummul na kwance kan gadon hutu na asibitin, shiko Usman yana kwance kan d'ayan gadon dake kallon nata yasanya jinjirin gaba yanata kallo dan yariga ta farfad'owa,
yayinda Abba ke zaune a kan kujera a gaban gadon Usman kusa dashi kuwa Dr Bashir ne suna kallon yanda Ummul kedan motsa k'afarta a hankali,
Ammi ko tana zaune bakin gadon da ummul ke kwance tana rik'e da hannun ta idon ta ya na kanta,
yun kurin bude idonta tafarayi a hankali tanajin yamata nauyi,
da hannu Ammi taiwa Dr Bashir nuni aiko tare suka taso sukayo bakin gadon,
Tana bud'e idonta da kyar ta d'aga hannun ta da kyar ta shafi cikinta dan jin yayi mata wayam aiko saita d'an kara zaro idonta tabud'e baki da kyar murya nara voice a disashe a hankali tace,
"In in inaaaa cikin?". Hamdala suka rink'a jerawa cikin tsananin happy dan tunda Hamma Umar ya rasu sai yau Ummul ta iya magana,
ya Usman kuwa juya kanshi yayi a hankali wasu irin hawaye masu zafi suna bin fuskarsa,
Ammi ce ta mik'e da sauri ta d'auko babyn da yaketa bacci a gaba Usman shiko Usman sai kallon yaron yake cikin tsananin k'auna yana jin son yaro fiye da kowa a duniyar nan,
a hankali Ammi tace, "gashi nan Ummul, ga d'anki wanda Allah ya azurtaki dashi keda Faruoq na amman ke Allah ya nunawa shi shi kam Umar ya rasu da begen wannan rana ya rasu da kumfar rashin ganin d'anshi Ummul ga d'anki maraya zai tashi maraya kamar yadda iyayenshi suka tashi marayu".
Daga kwance tasa hannu ta d'ora akan yaron ta kuramai idanu tanajin k'aunar shi na ratsa zuciyar ta da dukkan jikinta sai kuma tayi kurui tana kallon Usman dake konce yana hawaye cikin sanyi yace,
"Ammi yaron nan bazaiyi maraiciba Insha Allah bazai yi kukan rashin mahaifiba Ammi da izinin Allah indai ina raye yaronan bazai zubda k'ollah".
sai kuma ya rink'a kuka yana rik'e da hannun Abba,
shima Abban kuka yake Ammi kuwa zuwa yanzu hawayenta sun fara k'agewa,
Adam ma gaba d'aya ya zama mai raguwar zuciya abu kad'an sai Kuka amman shi tausayi Usman ke addabar rayuwarshi,
haka Dr Bashir kuwa da sauran doctors din sukayi ta kula da Usman da Ummul da jaririnta k'ato fari tas kekyawa, sukaita kula dasu cikin ikon Allah kuwa Ummul da Usman duk Alhamdulillah jiki yayi kyau Ummul kuwa tun randa tayi magana bata kuma yiba.

Doctors sun bada tabbacin zuciyar Usman zata iya aikin da ake but'ata amman a guji b'acin ransa sosai sukayi kashedin gudun b'acin ran shi,
a gefen Ummul Kuwa sunce kar a damu da rashin maganarta sunce a koda yaushe maganarta zata iya dawowa amman kuma a duk randa suka tsinci Ummul na kuka toh karsuyi yunk'urin hanata a barta domin a cewarsu yin kukan zai iya maida tunaninta dai-dai har ta fara magana kuma sanyin da zuciyarta tayi harda rashin kukan.

Bayan kwanaki shida dayin aikin aka sallamesu da sharadin kulawa da bawa Ummul da Usman magunguna don cigaba da samarwa zuciyoyin su lafiya, da haka suka tattaro suka dungumo sai gida Nigeria.

Randa suka dawo gaba d'aya zuriyar Shuwa sun cika da farin ciki domin samun lafiyar Usman da Ummul ga jariri da ya zamo magajin Hamma Umar kowa zaizo da Happy amman abin fargaba har yanzu Ummul bata mgn,
Nenne takan buya tayi ta kuka,
Ummul kuwa in banda bawa yaro nono da da tasashi a gaba tayi ta kallo ba abinda takeyi da kanta sai an tasa a gaba wani lokacin sai ta wuni ta kwana bataci komaiba inko yaronta na kuka sai tai ta rawan jiki ta gigice,
in tak'i cin abinci da wonka Usman yakan zauna a gabanta yayi ta magiya har ya fara zubda k'ollah to da zaran taga yana kuka sai ta zauna ta fara cin abincin.

A haka rayuwa tayi ta juyawa har sukayi kwana 9 da dawowa,
yau asabar da safe bayan sun gama aiyu kansu,
Abba da kanshi ya shiga d'akin da Ammin ke zaune da Ummul a nan ya samu Usman da Nenne da Adam Ummul ruggume da yaron,
bayan sun gaisa cikin kula Abba ya kalli Usman yace,
"ni kam Usman me sunan yaron ne har yau baka gaya min
ba? ".
cikin mamaki Usman yace,
"Abba baka yiwa yoron huduba bane dama ni yamin ka gaya mai sunanshi ai".
a hankali Abba yace,
"A a Usman ya za'ayi haka yaro yau kwana 14 kuma ashe ba'a mai huduba ba".
Ammi ce ta kallesu a hankali tace,
"mahaifiyarshi ta mishi huduba tun randa yayi kwana uku amman har yau bata gaya min sunan shiba".
usman d'in ya zuba mata ido cikin sanyi yace,
"Ummul kiyi hak'uri mana ki ruggumi k'addararki ki rink'ayi mana magana yanzu tsakanin ki da Hamma kiyi mishi gatan Addu'a ki bawa d'anshi tarbiya to amman a hakan zakiyi wad'an nan abubuwan"?.
shiru tayi tana jinshi karo na forko da ida nunta suka ciwo da hawaye tab,
Abba ne ya kalleta a raunane yace,
"Me sunan yaron?".
murya can k'asa cikin rauni da tsananin k'una a zuciya tace,
"Washe garin za'a kashe Hamma na yace min in namiji na haifa ya bani dama nasa sunan wanda nafiso a duniya wanda duk duniya bani da kamarshi".
sai kuma ta saki wani irin kuka ta ruggumo yaron tana kallon shi,
Usman ma kukan ya fara a hankali yace,
"Ummul me sunan yaron?".
cikin tsananin kuka tazo ta durk'usa gaban Abba murya a disashe tace,
"Abba ina sonshi Abba ina sonshi ina sonshi Abba duk duniya bani da kamarshi Abba ina son Hamma Umar Abba ina zan ganshi Abba sun kashe min Hamma na a gabana Abba ina son Hamma Umar".
sai kuma ta kife kanta a cinyar mahaifin nata cikin rauni da tausayawa rayuwarta,
shiko Abba a hankali yace,
"Me sunan yaron kika saka? ".
cikin tsananin kuka tace,
"Sunan shi *Umar Faruoq*".
tana fad'in haka Usman ya........

*Sadaukarwa ga Umar Ibrahim Umar Hamma Umar*

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*RUBUTACCEN AL,AMARI*

Page 3⃣2⃣

*Na*
*AYSHA ALI GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*MOH ALLAH WUJI FURD'ATA*

*Kin kid'i kankad'a damoni na damoni giddo mo fina laramo gaid'omo fina sukoyo ladde Allah yamad'u benduki yamete ki b'ib'b'e sammete joruki tenete ki d'oidi yalete*
Chapter 55 · 0% Book details