Sashe 37
Rubutaccen Alamari Part 1 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Direct general Hospital dake cikin damaturu ya kaita. bayan yayi parking motar sa a parking lot ya kalleta yace " sai ki fito mu shiga ai", ba tareda ta musan tashiba ta gyara hijabin ta, mik'a mata farar hankerchief yayi wanda yake fitar da wani k'amshi mai dad'in gaske yace "Haka zaki fita salon a ganeh kinyi kuka koh? Maza karb'a ki goge fuskan ki" ba musu ta karb'a hankerchief d'in ta goge fuskan ta,bayan ta kimsa yace "Toh muje koh" ba musu ta sauk'o a motar suka jera suna tafiya abun sha'awa har office na abokin shi Doctor Nasir Fuskan tausayi tayi tana kallon shi tace
"Ayyah Hamma Umar fallasa ni kake sonyi? Salon abokin ka yasan abunda na aikata?". Hararar ta yayi ya bud'e office yashiga ita kuma tabisa a baya. Sosai Doctor Nasir ya amshe su yana mai zolayar abokin sa ango, bayan sun gama gaisawa Hamma Umar yace "Yawwa ina wancan Doctor'n take neh?" Cikin rashin fahimta Doctor Nasir yace,
"Wacce kenan?"
"Doctor Rukayya"
"Ohh tana nan bari na kirata tazo tayi assisting naku"
Ciro wayan sa yayi ya kirata tazo, dagan nan ya had'a su.
Bayan an had'a ta da Doctor'n tayi mata fad'a sosai tareda mata wa'azi tace "D'an adam kenan, wasu har kuka suke. Wallahi jiya wata mata da tazo shekarunta arba'in da biyar kuma tun tana shekaru goma sha tara tayi aure, bata tab'a family planning bata tab'a koh da b'ari ba. Jiya da tazo ta same ni sanda na zubda hawaye, kuka take sosai tana masifan son haihuwa kuma Allah bai bata ba, amma ke sai k'okari toshe ni'iman Allah kike bayan mijin ki naso, gaskia kin bani kunya kin ban haushi" Haka ta ta mata masifa har ta cire roban tareda bata wasu magani.
Bayan sun gama taje ta samu Hamma Umar a cikin motar sa yana zaune already daman sunyi waya ta same shi a cikin mota. Yana ganin ta da Doctor'n ya fita a motar sa ya mata godiya sosai tana mai k'ara basa hak'uri irin halin 'yan matan yanzu. daga nan ya shige motar sa daman tuni har Ummul ta shige ta kwanta a kan kujera tareda lumshe idanuwan ta,wani irin ciwon kai take ji dalilin kukan da tasha, tsantsan tausayin ta yaji ya shafa laulausar fuskan ta yace "Sannu kin gaji koh?" D'aga masa kai tayi ba tareda ta basa amsa ba, restaurant ya wuce ya musu odering abinci a take away yazo ya zuba su a seat na baya ya sake tsayawa ya siyo musu icecream dayawa daga nan ya kama hanyan gida.
Suna isa Ummul direct d'akin ta tashige shi kuma ya kwasa kayakin da ya siya ya shigar dasu, icecream d'in ya zuba su a fridge ya ajiye abincin dinning shima ya shige d'akin sa dan wanka.
Bayan ya fito ya saka jallabiyar sa ya fesa jikin sa da turaruka masu k'amshi gaske yaje d'akin Ummul, yana shiga ya ganta a kwance akan gado but da gani alama tayi wanka dan ta canza kaya, zama yayi a gefen ta yana mai shafan fuskan ta yace
"Ummul taso muje muci abinci tun safe fa ba abun da kika ci sai d'azu da kika sha coke a asibiti", ita kanta tasan tana jin yunwan haka ta taso a daddafe tace "Toh muje". Tasowa yayi shima ya kama kugunta suka fara tafiya har dinning, ya jawo mata kujera ta zauna, haka yayi serving mata abinci taci ta koshi,daga nan yace "Ummul bari naje masallaci kinji kinga yanzu za'a kira magrib bayan sallah'n isha zan shigo". d'aga masa kai tayi tace
"Toh sai ka dawo". Ganin yanayin da tayi magana da k'yar ya matso kusa da ita yace
"Lafiya kuwa Ummul? meke damunki?", wasu zazzafan hawaye neh suke sauk'a akan kuncin ta tace "Hamma Umar ciwon kai", kallon ta yake da tausayi fal kwance kan fuskan sa yace "Kinga illan yawan kuka koh? maza tashi ki shiga d'akin ki na kawo miki magani kisha"
Haka ta taso yana rik'e da ita har d'akin ta ya zaunar da ita kan bakin gado, ya shige d'akin sa ya d'auko magani ya had'o da faro ya mik'a mata, duk yadda yakai da batason magani ganin yadda ya tsareta da kallo ba yadda ta iya haka ta amsa maganin tasha,
daga nan ya wuce masallaci itama ta tashi tayi sallah a daddafe, ita bata tashi akan daddumar sallah'n ba har sanda aka kira sallar isha'i tayi, a yanzu dai ta d'an ji saukin ciwon kai d'in. Shiga toilet tayi tayi brush tabi lafiyan gado sabida tana wani irin jin bacci, cikin minti biyu bacci b'arawo ya d'auke ta.
"Ayyah Hamma Umar fallasa ni kake sonyi? Salon abokin ka yasan abunda na aikata?". Hararar ta yayi ya bud'e office yashiga ita kuma tabisa a baya. Sosai Doctor Nasir ya amshe su yana mai zolayar abokin sa ango, bayan sun gama gaisawa Hamma Umar yace "Yawwa ina wancan Doctor'n take neh?" Cikin rashin fahimta Doctor Nasir yace,
"Wacce kenan?"
"Doctor Rukayya"
"Ohh tana nan bari na kirata tazo tayi assisting naku"
Ciro wayan sa yayi ya kirata tazo, dagan nan ya had'a su.
Bayan an had'a ta da Doctor'n tayi mata fad'a sosai tareda mata wa'azi tace "D'an adam kenan, wasu har kuka suke. Wallahi jiya wata mata da tazo shekarunta arba'in da biyar kuma tun tana shekaru goma sha tara tayi aure, bata tab'a family planning bata tab'a koh da b'ari ba. Jiya da tazo ta same ni sanda na zubda hawaye, kuka take sosai tana masifan son haihuwa kuma Allah bai bata ba, amma ke sai k'okari toshe ni'iman Allah kike bayan mijin ki naso, gaskia kin bani kunya kin ban haushi" Haka ta ta mata masifa har ta cire roban tareda bata wasu magani.
Bayan sun gama taje ta samu Hamma Umar a cikin motar sa yana zaune already daman sunyi waya ta same shi a cikin mota. Yana ganin ta da Doctor'n ya fita a motar sa ya mata godiya sosai tana mai k'ara basa hak'uri irin halin 'yan matan yanzu. daga nan ya shige motar sa daman tuni har Ummul ta shige ta kwanta a kan kujera tareda lumshe idanuwan ta,wani irin ciwon kai take ji dalilin kukan da tasha, tsantsan tausayin ta yaji ya shafa laulausar fuskan ta yace "Sannu kin gaji koh?" D'aga masa kai tayi ba tareda ta basa amsa ba, restaurant ya wuce ya musu odering abinci a take away yazo ya zuba su a seat na baya ya sake tsayawa ya siyo musu icecream dayawa daga nan ya kama hanyan gida.
Suna isa Ummul direct d'akin ta tashige shi kuma ya kwasa kayakin da ya siya ya shigar dasu, icecream d'in ya zuba su a fridge ya ajiye abincin dinning shima ya shige d'akin sa dan wanka.
Bayan ya fito ya saka jallabiyar sa ya fesa jikin sa da turaruka masu k'amshi gaske yaje d'akin Ummul, yana shiga ya ganta a kwance akan gado but da gani alama tayi wanka dan ta canza kaya, zama yayi a gefen ta yana mai shafan fuskan ta yace
"Ummul taso muje muci abinci tun safe fa ba abun da kika ci sai d'azu da kika sha coke a asibiti", ita kanta tasan tana jin yunwan haka ta taso a daddafe tace "Toh muje". Tasowa yayi shima ya kama kugunta suka fara tafiya har dinning, ya jawo mata kujera ta zauna, haka yayi serving mata abinci taci ta koshi,daga nan yace "Ummul bari naje masallaci kinji kinga yanzu za'a kira magrib bayan sallah'n isha zan shigo". d'aga masa kai tayi tace
"Toh sai ka dawo". Ganin yanayin da tayi magana da k'yar ya matso kusa da ita yace
"Lafiya kuwa Ummul? meke damunki?", wasu zazzafan hawaye neh suke sauk'a akan kuncin ta tace "Hamma Umar ciwon kai", kallon ta yake da tausayi fal kwance kan fuskan sa yace "Kinga illan yawan kuka koh? maza tashi ki shiga d'akin ki na kawo miki magani kisha"
Haka ta taso yana rik'e da ita har d'akin ta ya zaunar da ita kan bakin gado, ya shige d'akin sa ya d'auko magani ya had'o da faro ya mik'a mata, duk yadda yakai da batason magani ganin yadda ya tsareta da kallo ba yadda ta iya haka ta amsa maganin tasha,
daga nan ya wuce masallaci itama ta tashi tayi sallah a daddafe, ita bata tashi akan daddumar sallah'n ba har sanda aka kira sallar isha'i tayi, a yanzu dai ta d'an ji saukin ciwon kai d'in. Shiga toilet tayi tayi brush tabi lafiyan gado sabida tana wani irin jin bacci, cikin minti biyu bacci b'arawo ya d'auke ta.